← Book details Hatsabibin Boka Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
CHAPTER 22 OF 41

PART 2⃣

Hatsabibin Boka Part 2 Complete Hausa Novel · about 5 min read

29
By gentle
lady 💃🏽


Bayan sungama cin abinci kaleed yamike yayimasu saida safe usman yace baxaka tayamu firaba""

Idanunsa yashafa yace barci nakeji dad nagaji dayawa,"" yace shikenan kaje kakwanta saida safe kaleed yace okay dad night yawuce abunshi haryana hadawa dadan gudu khadija tabishi dakallo tana murmushi

Usman yana kallonta shima murmushi yayi labila ce tamike itama tayimasu saida safe tadauki sapna tawuce su anwar sunawajen zahara u itama sapna batajin dadi shiyasa takawota wajen khadija

Yanxun khadija harmantawa takeyi tanada yaya dantunsafe idan tabasu abincinsu batasake ganinsu saikuma idan sunji yunwa"

Bayan labila tawuce Usman yadan jingina jikin kujerah yana kallon khadija yace mekika fuskanta akan kaleed naga kinbishi da murmushi akwai magana dauke abakinki

Dariya tadanyi mai sauti tace bakomaifa kawaidai yabani dariyane nasan babarci yakejiba""

Osman yasaki murmushi yace nima nasan haka yasake matsowa kusada itah yace kinsan Zainab dinsa???

Tace mezaihana tunda kanwatace yace anyihaka kaleed yafadamun ai khadija tace aisaikaji soyayyar tasuma sufa ada kafin natafi cen sunason junansu sosai
.
Saidai su tunaninsu babu aure tsakaninsu tunda iyayensu daya shi idan yaganta dasaurayi yahau zuciya itakuma idan taganshi da budurwa ranar babu Wanda zaiga fara arta saitayi kwana biyu bataci komaiba ...

Saiyaakoma rarrashi'"" usman yace toyanxu tasani? Khadija tayi shiru daga bisanie tace bana tunanin yasanarda itah

Usman yayi shiru daga bisanie yace zanso ace labila tasamu miji dasai ayi bikinsu lokaci daya Amman nalura batako kula samari bansan zatakeson zamaba

Khadija tace kamar yanda matarka tazama kamanta alkwarin mu da itah ainice zanzaba mata miji shiyasa batakula samari

Usman yarike baki yace hakane namanta toke waye zakibata??? Tace yayana Amman haryanzu bansanarda itaba inajiransa yadawone""

Usman harcikin ransa yaji dadi sosai''' yace Alhamdulillah Allah yatabbatar mana da alkhairi"' khadija tace Ameen

Usman yamike yace tashimuje kinji anbarmu anan gashinima nasomajin barci tana dariya tace katabbata barcin zamuyi ko??

Yace Sosai Amman saimun gama .....😉yakanne mata ido daya"" tana dariya suka wuce sama

Kaleed kuwa yakwana yanajan tsaki dankoda yakoma yakirah wayar Zainab kin dagawa tayi karshema takashe wayar

Shima jefarda tashi yayi yakwanta"" yadade kafin yasamu barci yadaukeshi
*************

Bayan kwana biyu jama ar unguwar da lubcy take suka soma takurah duk dare basa samun isashen barci saboda ihunda sukeji kuma yanxun sungano tacikin gidan ihun yake fitowa Amman kuma babu alamun akwai wata halitta mairayuwa acikin gidan

Wannan dalilinne yasaka suka dunguma zuwa gidan Usman dansu sanardashi abunda kefaruwa"""

Suna kaiwa gidan shikuma yafito tareda kaleeed zasuje office ganin mutanen yasa yatsaya yana kallon su sukayiwa maigadi magana

Osman yace barsu sukaraso khadija takoma Cikin gida suka karaso hannu yabasu suka gaisa yanayi masu kallon sanie

Amman yamanta inda yasansu danyadade rabonda yaje unguwar yadaina sauke baki agidan saidai hotel bayan sungaisa wani daga cikinsu yace sunana alhaji kabeer munzone akan maganar tsohon gidanka

Osman yace ayya nikam naga fuskar sanie kuwuceto mana yayi maganar yanayimasu iso falon baki yakaisu yasa aka kawomasu lemu daruwan sha"" bayan sunsha ruwa aka sake gaisawa Wanda yace sunansa kaberr yayi gyaran murya

Alhaji Usman wani bakon al a marine yakefaruwa agidanka kwana biyu abun yana damunmu mudamuke kusa dagidan takai yanxu kobarci bamayi damu da yaranmu"" Usman yagyara zama yace me yake faruwa danshi Sam yama manta lubabatu tanagidan

Alhaji kabeer yanisa yace kullum dadare wani irin kuka mukeji agidan da ihu da kururuwa bamasamun barci saikusan asuba dafari bamudauka daga gidanka abun yake zuwaba saidaga baya mukagane"" daga gidan kukan yake fitowa

Munfi saran aljanune kokuma fatalwa dankuwa duk sanda mukaji kukan ana Neman dauki kuma komenene macene danmuryar mace mukeji koda munzo kofar gidan kulle muke samunsa da tsohon kwado sannan ga yana duk ta baibayeshi banda tsatsarda yayi

Kagakuwa babu alamun da za ace mutum ne aciki munfidai zargin fatalwace

Usman yayi shiru aransa yanacewa tokodai lubabatu bataje gidanba??? To Amman inazataje badaita koma garinsuba"" alhaji kabeer yakatsemasa tunaninsa yace mafita daya mexaihana muje kagani kokabari saida dare muje Dan dazaran anyi magrib duhu yasamu abun kefaruwa

Usman yace ah ah basai dare yayiba ninasan mutumne agidan Amman baxan tabbatarba danbansaniba kotaje kowani gurin takoma

Sukahau kallon kallo yace alhaji badai mutum ba gaskiya gidan baiyi kamada akwai mutaneba

Usman yace banki tatakuba kutashi muje ingani inhar bansameta agidan ba sainasa ayiwa gidan karatu sainabadashi

Sukace hakanma yayi gabadayansu suka mike kaleed dama yana wajen mota yanajira Usman yace yashiga suwuce


Mota daya suka shiga sukuma sukashiga tasu suka dunguma zuwa unguwar.......


Kamar yanda suka fada aikuwa haka Usman yatarar gabadaya yanace akofar gidan babu alamar akwai mutum aciki

Sukace kagani ko dama munfadamaka "" Usman yace abun nan da mamaki aikoda Dadewarda akai ba ashiga gidan ba baidace yayi yana hakaba kubamu Aron wani karfe abuge kwadon

Wanine yatura yaronsa gida dagudu akaje akasamu abun bugu aka balle kadon suka shiga cikin gida kaleed ne yatsaida yara dangaba daya unguwar tacika harda mata anaso aga menene acikin gidan wasu harcewa suke kilantama tsafi yakeyi

Usman motar lubabatu yasoma cin karoda itah itakanta gabadaya yana tazagayeta yana tafiya yana waigen motar harsuka bude gidan

Kaisaikace kangon gida danyanace ako ina bakasaran akwai wani Abu agidan makotan sukace lallai bakomai agidan nan saidai infa fatalwace

Usman dakunan gidan yasoma bi daibayan daya """ harsuka gama zagayensu basu lura da lubabatu ba wacce take yashe kofar shiga daga gefe

Bayan sunfito Usman yana waigawa gefen yana dube dube yaganta dasauri yakarasa wajen hannu yasaka yatabata tareda Kiran sunanta

Tazaburah tatashi zaune tafasa ihu "" ihuntane yajawo daukacin mutanenda suke niyar fita gidan gabadaya sukajuya dagudu danjin ihun suka koma inda suka hangi Usman ciki kuwa harda kaleed dasauran yara

Tanayin ido hudu da Usman tatashi dagudu tayi hanyar fita gabadaya batada kaya ajikinta zindir take

Kurajenta suna nan saidai basucigaba da girmaba gashin kanta duk ya cukuikuye jikinta duk raunine tana fita mutane suka dafa mata baya

Usman kansa yakauce hawaye masu zafi suna saukomasa shihar kunya zaiji idan akace wannan matar wai matarsace.........


Aisha✍🏼
☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠
Chapter 22 · 0% Book details