Sashe 78
Gimbiya Balaraba Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Shamsiyya ce cikin kuryan d'akinsa tunda ta tashi da safe take jin ciwon ciki tayi shiru bata fada ba,sai da taga wani abu me kama da jini yana zubawa daga gabanta shine fa ta kira mahaifiyar ta ta fada mata, Uwa ta kira Lantana hankali a tashe! Tasan haihuwa CE,nan suka fara bata taimako ganin yadda take yunk'urin da alama haihuwar a kusa take.
********
Tashin hankalin da iyalin Waziri suka shiga ba a fad'ar sa, ganin yadda hallitun ubansu ya sauya ya munana ya jirkita sai kace ba mutum ba, tuni wasu suka fara kuka mussaman mata, da k'yar aka samu Kattime ta dawo hayyacin ta, ta kallin mijinata da ya koma kamar tsumma! Lokaci guda ubangiji ya tagayarashi tace." Alhamdullahi Allah na gode maka da ya mayar da kai haka hak'ika mutuwar ita tafi amfani da RAYUWAR ka, ka cucu ni ka cuci 'yayanka saboda son zuciya irin taka, ka kashe rai Wanda bamu San adadi ba, hak'ika nayi nadamar auranka bana fatan ko a lahira ubangiji ya had'a fuskoinmu"
Tana gama maganar ta fashe da kuka me cin rai!
Nan fa fadawan da suka kawo shi suka dinga silalewa suna futa cike da kunya.
********
Cikin hukuncin ubangiji Shamsiyya ta haihu lafiya inda ta haifi d'anta namiji yaro lafiyyaye dashi me kama da ubansa sak!!! Kuka sosai take uwa na tayata wai yau itace zata Goya Dan shege rayuwa kenan, haka Lantana ta dafa ruwan zafi tayiwa jinjiri Wanka tas ta shirya shi cikin kaya,ta goyashi tana daure zuciyarta itama amma kukan zuciya kam kullum sai tayi shi.
******
To ranar bayan sun dawo daga massalaci Shatima ya kira wayar mama ya Sanar mata halin da ake ciki, murna sosai Mama tayi ta dinga godewa Allah da ya kawo wa yaron ta sauk'i cikin lokaci kankani lallai duk Wanda ya dogara ga Allah yayi dace duniya da lahira
Me girma governor kuwa yana ganin kamar yafi kowa farin ciki, don haka nan take yasa mutanan sa afara shirye-shiryen nad'i domin a cewarsa me Martaba Sarki!Almansur na biyu na dawowa za'a fara shagalin nadin sarauta, aikuwa gari ya d'auka da murna,dama labarin halin da Waziri yake ciki ya karad'e ko ina cike da waje harda wajan gari ma kowa yaji wasu na turr dashi wasu kuma na tausaya masa halin da yake ciki.
Yau Litinin Wanda yayi dai-dai da sati uku kenan da tafiyar su saudi'a a yau din ne kuma suke d'aura niyyar dawowa gida cikin farin ciki da samun nasara, Balaraba tayi wani fresh da ita kyallin ciki duk ya bayyana a tattare da ita, ta kara cika da kwarjini sosai duk Wanda yasan mace me ciki ya kalleta a lokacin sai ya gane, shiko uban tafiyar tamkar ba Wanda yaje jinya ba ya had'a wata kiba fatarshi tayi sumul-sumul sai shek'i take,shida Balaraba har nasara Wanda yafi wani kyau da gogewa
******
Can gida kuwa ya hautsine da shagali gami da kid'e-kid'e da busa ko INA ka kalla jama'a ne suke kai kawo kowa yana cike da farin cikin dawowar me Martaba cikin aminci da koshin lafiya.
Halisa da Azima sai kintse-kintse sukeyi kowacce tana k'okarin tayi abunda zata fi 'yar uwarta dashi, Azima kokari kawai take tana ji ajikinta kamar asirinta zai tuno tunda dai gashi Waziri yana cikin wani hali shine dama ya yaudare ta, gashi yanzu tana mutukar son auranta addu'a kawai take Allah ya rufa mata asiri.
Fili jirgi a cike da a yarin gidan sarauta tare da ayarin me girma governor suna jiran saukar jirgin su, Sha biyu dai-dai jirgi ya sauka Shahid da Shatima ne a gaba, sai Sarki! Da BALARABA a bayansu ya rungomo ta jikinsa, tuni gadawan gurin suka fara zubewa suna kwasar gaisuwa, cike da kunya take k'okarin kwace jikinta ya ki s'akinta,cikin walwala suke gaisa da jama'arshi su Governor da Galadima da sauransu mota ta mussaman aka bude masa ya shiga ya zauna Balaraba ta shiga direba ya shiga domin su Kansu su Shahid wata motar daban suka shiga, direba yaja su suka nufi gida
*****
Tsabar hayaniya jama'a tasa kansa ya fara ciwo nan take yace. da Babu direba su huce can shashen Maman shi, amma duk da haka jama'a bin motar suke suna banbadan ci tare da roko da kid'a kowa na fadin albarka cin bakinsa, Sarki ya futo cikin walwala ya dinga daga musu hannu ya rike hannun matar shi tamm!!fadawa suka dunga sanya duka da bulala da k'yar dai ya samu ya tattatka suka shige gurin Maman shi, wacce take tsaye gurin wani k'aton window tana ganin abunda yake faruwa, ganin yaron ta yayi kiba da lafiya gashi kamar ba Wanda ya tafi jinya ba,yasa ta godewa Allah sosai yana shigowa ya rungume ta, Balaraba ta koma gefe tana murmushi, Mama ta rik'o hannunta tana fadin"Zonan yarinyar ta hak'ika ke alkairi ce a tare damu kin zama Wani jigo na rayuwar mu, Balaraba ina jinki a cikin jinana tamkar nice na haifeki ubangiji Allah ya sauke ki lafiya." Balaraba tayi saurin sunkuyar da kanta cike da kunya, lallaima ashe sai da ya fadawa Mama halin da take ciki" Mama ta cigaba da cewa." Duk irin dawainiyar da kikayi da mijinki ina da labari, babu abunda zan iya saka miki dashi sai dai addu'a ladan ki na gurin Allah domin kinyi ibada kin bautatawa mijinki ubangiji Allah ya jikan iyayaenki yayi miki albarka a rayuwar ki." Balaraba ta sunkuyar da kai kasa tana amsawa da amin kwalla duk ta cika mata ido.
Sadiya da Usuman ne tsaye can gefe suna kallonsu Mama ta kirasu tace." Kuzo ga aunty ta dawo,. " BALARABA ta daga Kai tana kallon yaran sunyi kyau sosai sun murje sun kara girma Sosai Mama take kula dasu, makaranta suke zuwa me tsada su saka suttura masu tsada babu. Shakka babu abunda zatace da Mama Fulani bisa alkairin ta a garesu.
Nan b'angaran Mama suka biyo shi Halisa da Azima kowacce tana wace wannan gurin ado gwal sai walwali yake a jikinsu, Balaraba ta basu gurin ganin yadda sukeyi I junansu tamkar su bangaji juna,duk wannan k'awancan babu shi, kowacce ta kwaci kanta, Halisa duk ta kanainaye shi, a cewar ta ai girkin ta ne yau don haka duk su matsa gefe, shidai kawai kallonsu yake, yana tunanin halin da zai shiga zai kwana ba tare da gimbiyar sa ba, ya Riga ya saba da dumin jikinta da shagwaba shi da take sosai da soayyarsu duk dare, to itama b'angaran ta hakan take duk tayi sanyi tana tunanin ta yaya zatayi bacci bataji kanta a kirjinsa ba yana mata wassanin kamar yanda suka saba a saud'ia.
*Daga wannan pege din sai na k'arshe Ku zauna cikin shiri*❤❤❤❤
👸🏻👸🏻👸🏻👸🏻👸🏻
_*GIMBIYA BALARABA*_
👸🏻👸🏻👸🏻👸🏻👸🏻
~*NA*~
_BINTA UMAR ABBALE_
*BINTUBATULA👄*
*MARUBUCIYAR*
```NANA KHADIJA```
```YARO DA KUDI```
```GIMBIYA BALARABA```
```TSANTSAR BUTULCI```
```LADIDI K'WADAGA```
_*ZAMANI WRITES ASSOCIATON🤝🏻*_
_____________________
```We are here to educate motivate and entertain aur reades```
_______________________
*JAN KUNNE⚠*
_*Ban yarda a siyar min da d'aya daga cikin books d'in ba, duk mai buk'atarsu sai ya nemi numbar ta, ban yarda ka/ki siyar min da littafi to wallahi tallahi ban yafe ba kuma zamu tsaya gaban Ubangiji kan hakan, hattara!! Masu satar fasaha, ka nemi halak d'in ka yafi kaci da gumin wani, halak d'in ka shine mafi alkairi a gare ka.*_
*DEDICATED*
~*TO*~
*RAHAMA ALIYU*
~*ABUJA*~
_*BISIMILLAHIR-RAHAMANIR-RAHIM*_
🔚🔚🔚🔚🔚🔚🔚🔚
*🅿115*
Da k'yar ya samu ya kufce daga hannun Halisa ya gudu part d'insa inda su Shahid suke zaman jiransa,nan kama kafin ya tafi sai ya gargade su kar wacce ta bishi, saboda hutawa zaiyi Balaraba cikin zuciyarta tace." Dama ni ko ka neme ni ba zuwa zanyi ba, zama zanyi inyi jinyar zuciyata da zatayi kwana hudu ba tare da Kai ba.
Nan gurin Mama suka zauna dukaninsu, kallon Balaraba sukeyi a fakaice ganin yanda tayi Wani mugun kyau, tayar ta kamar ka tab'a jini ya futo ta kara cika da kwarjini, wani kyashi da bakin ciki ya damu zuciyarsu babu abunda ya kara daga musu hankali sai yanda Mama take kula da ita, tana kaf-kaf da ita da tayi motsi zatace "Ya akayi in dai akwai abunda kike sha'awar ci kiyi magana akawo miki." Girgikai kai kurum take cike da kunyar Maman, Halisa ta kalli Mama da jiki a sanyaye tace." Bata da lafiya ne."? Murmushi tayi tace." Cutar ta arziki ce ai insha Allahu kun kusa samun baby." Ita da Azima ban San wanda yafi wani shiga rud'u da tashin hankali ba, neman miyau tayi ta rasa abakin ta, idonta ya ciko da ruwan hawaye, Balaraba na da ciki,cikin kuma na masoyinta Wanda taci burin ita zata fara Haifa masa 'yaya, to wai abun tambaya anan, shine mutumin da ya tafi Neman lafiya ta yaya har ya iya kwanciyar aure babban abun tambaya yaya akai shi da bashi da kafa ya sarrafa kansa.
*Dariya nayi nace lallai Halisa kin cika hamaguwa😄*
To tunani da take shi Azima take duk sun shiga tashin hankali Lallai BALARABA tayi musu fintinkau tayi musu zarra,yanzu meye abunyi? Halisa take tambayar zuciyar ta, wani b'angare na zuciyar tata Yace mata,kawai yau kema ki matsa masa yayi miki ciki ki haihu, aikuwa ta yarda da wannan shawarar ta zuciyar tata.
*******
Walidi ne ya siyowa Shamsiyya atamfa guda biyu dinkakkau ya siyo rago ranar suna yaro yaci sunan mahaifin su,wato Sallau, Salihu kenan, a ranar ne kuma labarin Mabaruka ya same su, ta hanyar k'afafun yada labarai, an nuno ta kwance gadon asibiti babu k'afafu, ana cigiyar danginta harda Lamar waya aka kawo wa Walidi aikuwa atake ya kira wayar yayi musu kwantan inda suke, ba tare da bata lokaci ba aka sako Mabaruka a mota tare da keken guragunta tana kuka tana da tasani abunda tayi, Ranar kwana sukai kuka Iya da Sadiya matar Maman suna ta tausar zuciyar su.
******
********
Tashin hankalin da iyalin Waziri suka shiga ba a fad'ar sa, ganin yadda hallitun ubansu ya sauya ya munana ya jirkita sai kace ba mutum ba, tuni wasu suka fara kuka mussaman mata, da k'yar aka samu Kattime ta dawo hayyacin ta, ta kallin mijinata da ya koma kamar tsumma! Lokaci guda ubangiji ya tagayarashi tace." Alhamdullahi Allah na gode maka da ya mayar da kai haka hak'ika mutuwar ita tafi amfani da RAYUWAR ka, ka cucu ni ka cuci 'yayanka saboda son zuciya irin taka, ka kashe rai Wanda bamu San adadi ba, hak'ika nayi nadamar auranka bana fatan ko a lahira ubangiji ya had'a fuskoinmu"
Tana gama maganar ta fashe da kuka me cin rai!
Nan fa fadawan da suka kawo shi suka dinga silalewa suna futa cike da kunya.
********
Cikin hukuncin ubangiji Shamsiyya ta haihu lafiya inda ta haifi d'anta namiji yaro lafiyyaye dashi me kama da ubansa sak!!! Kuka sosai take uwa na tayata wai yau itace zata Goya Dan shege rayuwa kenan, haka Lantana ta dafa ruwan zafi tayiwa jinjiri Wanka tas ta shirya shi cikin kaya,ta goyashi tana daure zuciyarta itama amma kukan zuciya kam kullum sai tayi shi.
******
To ranar bayan sun dawo daga massalaci Shatima ya kira wayar mama ya Sanar mata halin da ake ciki, murna sosai Mama tayi ta dinga godewa Allah da ya kawo wa yaron ta sauk'i cikin lokaci kankani lallai duk Wanda ya dogara ga Allah yayi dace duniya da lahira
Me girma governor kuwa yana ganin kamar yafi kowa farin ciki, don haka nan take yasa mutanan sa afara shirye-shiryen nad'i domin a cewarsa me Martaba Sarki!Almansur na biyu na dawowa za'a fara shagalin nadin sarauta, aikuwa gari ya d'auka da murna,dama labarin halin da Waziri yake ciki ya karad'e ko ina cike da waje harda wajan gari ma kowa yaji wasu na turr dashi wasu kuma na tausaya masa halin da yake ciki.
Yau Litinin Wanda yayi dai-dai da sati uku kenan da tafiyar su saudi'a a yau din ne kuma suke d'aura niyyar dawowa gida cikin farin ciki da samun nasara, Balaraba tayi wani fresh da ita kyallin ciki duk ya bayyana a tattare da ita, ta kara cika da kwarjini sosai duk Wanda yasan mace me ciki ya kalleta a lokacin sai ya gane, shiko uban tafiyar tamkar ba Wanda yaje jinya ba ya had'a wata kiba fatarshi tayi sumul-sumul sai shek'i take,shida Balaraba har nasara Wanda yafi wani kyau da gogewa
******
Can gida kuwa ya hautsine da shagali gami da kid'e-kid'e da busa ko INA ka kalla jama'a ne suke kai kawo kowa yana cike da farin cikin dawowar me Martaba cikin aminci da koshin lafiya.
Halisa da Azima sai kintse-kintse sukeyi kowacce tana k'okarin tayi abunda zata fi 'yar uwarta dashi, Azima kokari kawai take tana ji ajikinta kamar asirinta zai tuno tunda dai gashi Waziri yana cikin wani hali shine dama ya yaudare ta, gashi yanzu tana mutukar son auranta addu'a kawai take Allah ya rufa mata asiri.
Fili jirgi a cike da a yarin gidan sarauta tare da ayarin me girma governor suna jiran saukar jirgin su, Sha biyu dai-dai jirgi ya sauka Shahid da Shatima ne a gaba, sai Sarki! Da BALARABA a bayansu ya rungomo ta jikinsa, tuni gadawan gurin suka fara zubewa suna kwasar gaisuwa, cike da kunya take k'okarin kwace jikinta ya ki s'akinta,cikin walwala suke gaisa da jama'arshi su Governor da Galadima da sauransu mota ta mussaman aka bude masa ya shiga ya zauna Balaraba ta shiga direba ya shiga domin su Kansu su Shahid wata motar daban suka shiga, direba yaja su suka nufi gida
*****
Tsabar hayaniya jama'a tasa kansa ya fara ciwo nan take yace. da Babu direba su huce can shashen Maman shi, amma duk da haka jama'a bin motar suke suna banbadan ci tare da roko da kid'a kowa na fadin albarka cin bakinsa, Sarki ya futo cikin walwala ya dinga daga musu hannu ya rike hannun matar shi tamm!!fadawa suka dunga sanya duka da bulala da k'yar dai ya samu ya tattatka suka shige gurin Maman shi, wacce take tsaye gurin wani k'aton window tana ganin abunda yake faruwa, ganin yaron ta yayi kiba da lafiya gashi kamar ba Wanda ya tafi jinya ba,yasa ta godewa Allah sosai yana shigowa ya rungume ta, Balaraba ta koma gefe tana murmushi, Mama ta rik'o hannunta tana fadin"Zonan yarinyar ta hak'ika ke alkairi ce a tare damu kin zama Wani jigo na rayuwar mu, Balaraba ina jinki a cikin jinana tamkar nice na haifeki ubangiji Allah ya sauke ki lafiya." Balaraba tayi saurin sunkuyar da kanta cike da kunya, lallaima ashe sai da ya fadawa Mama halin da take ciki" Mama ta cigaba da cewa." Duk irin dawainiyar da kikayi da mijinki ina da labari, babu abunda zan iya saka miki dashi sai dai addu'a ladan ki na gurin Allah domin kinyi ibada kin bautatawa mijinki ubangiji Allah ya jikan iyayaenki yayi miki albarka a rayuwar ki." Balaraba ta sunkuyar da kai kasa tana amsawa da amin kwalla duk ta cika mata ido.
Sadiya da Usuman ne tsaye can gefe suna kallonsu Mama ta kirasu tace." Kuzo ga aunty ta dawo,. " BALARABA ta daga Kai tana kallon yaran sunyi kyau sosai sun murje sun kara girma Sosai Mama take kula dasu, makaranta suke zuwa me tsada su saka suttura masu tsada babu. Shakka babu abunda zatace da Mama Fulani bisa alkairin ta a garesu.
Nan b'angaran Mama suka biyo shi Halisa da Azima kowacce tana wace wannan gurin ado gwal sai walwali yake a jikinsu, Balaraba ta basu gurin ganin yadda sukeyi I junansu tamkar su bangaji juna,duk wannan k'awancan babu shi, kowacce ta kwaci kanta, Halisa duk ta kanainaye shi, a cewar ta ai girkin ta ne yau don haka duk su matsa gefe, shidai kawai kallonsu yake, yana tunanin halin da zai shiga zai kwana ba tare da gimbiyar sa ba, ya Riga ya saba da dumin jikinta da shagwaba shi da take sosai da soayyarsu duk dare, to itama b'angaran ta hakan take duk tayi sanyi tana tunanin ta yaya zatayi bacci bataji kanta a kirjinsa ba yana mata wassanin kamar yanda suka saba a saud'ia.
*Daga wannan pege din sai na k'arshe Ku zauna cikin shiri*❤❤❤❤
👸🏻👸🏻👸🏻👸🏻👸🏻
_*GIMBIYA BALARABA*_
👸🏻👸🏻👸🏻👸🏻👸🏻
~*NA*~
_BINTA UMAR ABBALE_
*BINTUBATULA👄*
*MARUBUCIYAR*
```NANA KHADIJA```
```YARO DA KUDI```
```GIMBIYA BALARABA```
```TSANTSAR BUTULCI```
```LADIDI K'WADAGA```
_*ZAMANI WRITES ASSOCIATON🤝🏻*_
_____________________
```We are here to educate motivate and entertain aur reades```
_______________________
*JAN KUNNE⚠*
_*Ban yarda a siyar min da d'aya daga cikin books d'in ba, duk mai buk'atarsu sai ya nemi numbar ta, ban yarda ka/ki siyar min da littafi to wallahi tallahi ban yafe ba kuma zamu tsaya gaban Ubangiji kan hakan, hattara!! Masu satar fasaha, ka nemi halak d'in ka yafi kaci da gumin wani, halak d'in ka shine mafi alkairi a gare ka.*_
*DEDICATED*
~*TO*~
*RAHAMA ALIYU*
~*ABUJA*~
_*BISIMILLAHIR-RAHAMANIR-RAHIM*_
🔚🔚🔚🔚🔚🔚🔚🔚
*🅿115*
Da k'yar ya samu ya kufce daga hannun Halisa ya gudu part d'insa inda su Shahid suke zaman jiransa,nan kama kafin ya tafi sai ya gargade su kar wacce ta bishi, saboda hutawa zaiyi Balaraba cikin zuciyarta tace." Dama ni ko ka neme ni ba zuwa zanyi ba, zama zanyi inyi jinyar zuciyata da zatayi kwana hudu ba tare da Kai ba.
Nan gurin Mama suka zauna dukaninsu, kallon Balaraba sukeyi a fakaice ganin yanda tayi Wani mugun kyau, tayar ta kamar ka tab'a jini ya futo ta kara cika da kwarjini, wani kyashi da bakin ciki ya damu zuciyarsu babu abunda ya kara daga musu hankali sai yanda Mama take kula da ita, tana kaf-kaf da ita da tayi motsi zatace "Ya akayi in dai akwai abunda kike sha'awar ci kiyi magana akawo miki." Girgikai kai kurum take cike da kunyar Maman, Halisa ta kalli Mama da jiki a sanyaye tace." Bata da lafiya ne."? Murmushi tayi tace." Cutar ta arziki ce ai insha Allahu kun kusa samun baby." Ita da Azima ban San wanda yafi wani shiga rud'u da tashin hankali ba, neman miyau tayi ta rasa abakin ta, idonta ya ciko da ruwan hawaye, Balaraba na da ciki,cikin kuma na masoyinta Wanda taci burin ita zata fara Haifa masa 'yaya, to wai abun tambaya anan, shine mutumin da ya tafi Neman lafiya ta yaya har ya iya kwanciyar aure babban abun tambaya yaya akai shi da bashi da kafa ya sarrafa kansa.
*Dariya nayi nace lallai Halisa kin cika hamaguwa😄*
To tunani da take shi Azima take duk sun shiga tashin hankali Lallai BALARABA tayi musu fintinkau tayi musu zarra,yanzu meye abunyi? Halisa take tambayar zuciyar ta, wani b'angare na zuciyar tata Yace mata,kawai yau kema ki matsa masa yayi miki ciki ki haihu, aikuwa ta yarda da wannan shawarar ta zuciyar tata.
*******
Walidi ne ya siyowa Shamsiyya atamfa guda biyu dinkakkau ya siyo rago ranar suna yaro yaci sunan mahaifin su,wato Sallau, Salihu kenan, a ranar ne kuma labarin Mabaruka ya same su, ta hanyar k'afafun yada labarai, an nuno ta kwance gadon asibiti babu k'afafu, ana cigiyar danginta harda Lamar waya aka kawo wa Walidi aikuwa atake ya kira wayar yayi musu kwantan inda suke, ba tare da bata lokaci ba aka sako Mabaruka a mota tare da keken guragunta tana kuka tana da tasani abunda tayi, Ranar kwana sukai kuka Iya da Sadiya matar Maman suna ta tausar zuciyar su.
******