Sashe 9
Daren Aurena Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Hajiya Asiya ta gama rikicewa saboda rashin ganin d'an nata Aliyu har zazzab'i tayi ta kira Abbansu domin taji ko suna tare ya ce "basa tare" haka dai ta b'oye Masa Bata fad'a masa komai ba, saboda ta san in har ta fad'a masa to ta shiga uku a gurin Alhaji Mansur, gashi Shima Jabir tun ranar da ba'a ga Aliyu ba ya fita yau kwana uku Bata saka shi a idanuwanta ba, Amman shi Bata damu ba domin ta san ba zai huce yana club da yammatan shi ba, haka dai zata zauna tayi ta sam batunta duk da irin tsananin son da take yiwa Jabir Amman ranta yana matuk'ar k'aunar Aliyu, zaune suke ita da Shahida domin Nihal tun jiya da saurayinta yazo ya d'auketa suka fita bata dawo gidan ba, Hajiya Asiya ta zabga tagumi tana kuka Shahida ce ta matso kusa da ita tana ta rarrashinta, Jabir ne ya shigo falon daman bai shi bai san wata sallama ba, dan haka ya shigo falon ko sallama bai yi ba yana fi to, wani irin kallon yabi mahaifiyar tasa da 'yar uwarta dashi na rashin mutunci sannan yayi shigewarsa d'aki babu sannu da gida ba gaisuwa, (ni kuwa 'yar mutanan zazzau nace yau Jabir har Hajiya Asiyan baka kyale ba, lallai abin naka ya huce tunanina😂), Abin mamaki maimakon Hajiya Asiya ta damu da irin yadda d'annata yayi Mata, Amman ko kad'an Bata damu ba sai ma tashi da tayi ta bi sa 'bangarensa ta tarar dashi a falo ya bage a kan kujera ya d'ora 'kafarsa d'aya a kan center table d'in da ke falon yana jijjigata, k'arasawa kujerar da yake tayi tana yi Masa sannu da zuwa "My son sannu da zuwa" Kallon kan ki ake ji ya bita dashi sannan ya tab'e Baki tare da cewa "Ai nayi tunanin ba zaki zo kiyi min sannu da zuwa ba, sai wani kuka kike tun ranar da ba'a ga Aliyu ba, Amman ni kwanana uku bana gidan nan Amman ko ki kirani ki ji lafiya" Mami ta zauna a kusa dashi tare da cewa "My Son ai kai nasan kana club ne, shiyasa ban kira ka ba, saboda nasan baka son takura, Amman shi Aliyu bai dawo ba har yanzu kuma na kira Abbanku ya ce basa tare" ta k'arasa maganar tana kuka, duk da irin yadda Jabir yake jin haushin Mamin a kan rashin kiransa da ba tayi ba sai da yaji tausayinta kuma ya ji hankalinsa ya tashi,"Mami kina nufin har yanzu Aliyu bai dawo ba" kai ta gyad'a masa alamar "eh", Jabir ya bud'e kenan zai yi magana sai ga Aliyu ya shigo falon bakinsa d'auke da sallama "Assalamu alaikum" yayi sallamar cikin sanyayayyiyar muryarsa mai d'aukar hankalin mutane, babu wanda ya amsa sallamar gaba d'aya sukai gurin da yake tsaye a bakin kofar falon, rumgumeshi Mami tayi tana fad'ar "Yarona ina ka tafi ka bar ni, nasan ban kyauta maka ba amman bai kamata kayi tafiyarka ba,kasan ina sonka sosai" zame jikinsa yayi daga rumgumar da Mami tayi masa ya k'arasa gurin Jabir suna kallon kallo sunyi kusan minti biyar suna kallon juna Jabir da ya gaji ya ce "Menene kake wani kallona kamar wanda yayi maka wani mugun abu", Wani irin murmushi mai ciwo Aliyu yayi tare da cewa "ina kallonka ne saboda kayi abin da ya kamata a kalleka kuma a kiraka da mara tausayi mara imani, Jabir wallahi kaii ba mutum bane dabba ne" Mami tayi saurin zuwa gaban Aliyu tana cewa "Aliyu baka da hankali d'an uwan naka kake cewa dabba" kallon takaici ya bi Mami dashi daba dan ita d'in mahaifiyarsa ce ba da yau yayi mata abin da ba za ta tab'a mantawa dashi ba, amman kash! ta ci dajarar ita mahaifiyarsa ce, cikin muryar da take nuna alamu yana cikin tsantsar bakin ciki da jin haushinsu ya fara magana "Mami banyi tunanin haka daga gurinki ba, ta yaya zaki bada goyon baya aka zalinci baiwar Allah marainiya to ku sani duk abin da kuke b'oyewa yanzu nasan komai kuma zan fad'awa Abba, shiyasa kace wai Auren wucin gadi kuka yi da yarinya to kasani duk abin da kayi sai an yiwa k'anwarka ko kuma 'ya'yanka kuma idan an tashi yi musu sai anyi musu ninkin abin da kayi banza,dabba,dak'ik'i" yana gama fad'ar haka ya fita ya koma b'angarensa zuciyarsa cike da bak'in ciki, Jabir kuwa ransa ya gama b'aci sai huci yake kamar wank tsohon mayun wacin zaki, Mami ta kamashi suka je suka koma ta shiga rarrashinsa cikin hassala ya ce "dalla ni ki kyaleni kina kallon wannan yaron har ni zai zo gaba na ya ce min ni dabba, dak'ik'i, banza" ya mik'e ya fara zagaye d'akin Mami ta tashi zata matsa kusa dashi ya d'aga mata hannu cikin tsawa ya ce "Mami karki matso kusani ki fice min a d'aki kafin na sauke fushi na a kan ki" fita Mami tayi ba tare da ta ce masa komai ba, 'bangaren Aliyu taje tayi ta bubbuga kofar d'akin nasa amman yayi banza da ita sai da ta gaji dan kanta, ta koma b'angarenta bedroom d'inta ta nufa taje ta kwanta tana sake-sake a cikin ranta maganar Aliyu ce ta fad'o mata da yake cewa sai ya fad'awa Abbansu sauke nannauyan ajiyar zuciya tayi tare da cewa "duk yadda zanyi, zanyi Aliyu ba zan tab'a barin ka ka fad'awa Abbanku komai gamai da Auren wucin gadin da Jabir yayi ba" ta saka wannan ta saka wannan har bacci ya d'auketa.
*B'ANGAREN AMATULLAHI DA KHADIJATULLAHI*
Yau Lado ya shirya tsaf zai d'aukarwa mahaifiyarsa fansar abin da Amatullahi tayi mata, wajen k'arfe 9:00pm na dare Lado ya d'auki ruwan zafin da ya tafasa shi ya nufi d'akin Amatullahi dashi, yayi sa'a kuwa kofar d'akin a bud'e take dan haka ya kutsa kansa a kwance ya tarar da ita tayi lanfa dan ta ji shigowar Ladon Amman tayi kamar bacci take yi, "Lado kenan idan kasan wata ai baka san wata ba daman nasan duk daran dad'ewa zaka zo d'aukarwa mahaifiyarka fansar abin da nayi mata shiyasa kullum cike nake da shirin zuwanka" Zabagegiyar wuk'ar da take gafenta kasancewar Amatullahi ta kashe wutar d'akin shiyasa Lado bai ga wuk'ar ba idonsa ya riga da ya rufe kawai burinsa ya watsawa Amatullahi ruwan zafin a fuska, ya d'aga d'an k'aramin bokitin da ya d'ebo ruwan zafin zai shek'a mata ai kuwa sai jin saukar wuk'ar yayi a hannunsa ya saki bokitin a kasa ruwan zafin ya zuba a k'afafuwansa ya kwala wani irin jijitatcen ihuuuuuuuu.......
Anan zan tsaya sai ku dakace ni a gobe idan Allah ya kaimu domin jin yaya zata kasance tsakanin Lado da Amatullahi shin Aliyu zai fad'awa Abba tak'adirancin da yake yi ko kuma Mami zata hanashi yaya rayuwar Jabir zata kasance anan gaba dashi da mahaifiyarsa da kuma k'anwarsa Nihal ku cigaba da biyo ni 'yar mutanan zazzau domin jin yadda zata kasance.
Da gudu Lado ya fita daga d'akin Amatullahi yana zabga ihu kamar zai zauce, Amatullahi wacce take tsaye a kan gadonta ta shek'e da wata irinyar dariya tare da cewa "An gaya maka ni d'in ta wasa ce, da ka tsaya hannunnaka zan cire gaba d'aya d'an iskan banza". A tsakar gida Lado ya tarar da Inna larai tana jiran fitowarsa zuciyarta cike da farin cikin d'annata zai d'aukar mata fansa, jin ihun Lado da tayi ne yasa hankalinta ya tashi gashi kuma tana tsoron shiga d'akin Amatullahi saboda tana tsoron abin da zai biyo baya gashi daman bata gama jinyar fuskarta ba, da gudu Lado ya k'araso gabanta har yana ban gaje ta yana fad'ar "inna 'yar ta'adda ce Amatullahi 'yar daba ce" ya fad'a a rud'e hannunsa yana fitar da jini kamar da bakin k'warya, Inna a gigice ta ce "me tayi maka Lado?" Lado ya ce "Inna ta sare ni a hannuna, kalli ki gani" da kyar Inna ta iya bud'e idonta domin tun ranar da Amatullahi ta dannata a cikin kaskon mai ta dena gani sosai, kuka Inna larai ta saka tana magana cikin sarkewar murya "gaskiya yarinyar nan ta cika tantiriya,bari ubanta yazo wallahi bazan iya zama da ita ba, ko ni ko ita wallahi" ta k'arasa maganar tare da shigewa d'akinta tana kuka shi kuma Lado ya fita zuwa *BUBA SPEACIAL HOSPITAL* domin a duba shi.
*Wace ce Amatullahi?*
*B'ANGAREN AMATULLAHI DA KHADIJATULLAHI*
Yau Lado ya shirya tsaf zai d'aukarwa mahaifiyarsa fansar abin da Amatullahi tayi mata, wajen k'arfe 9:00pm na dare Lado ya d'auki ruwan zafin da ya tafasa shi ya nufi d'akin Amatullahi dashi, yayi sa'a kuwa kofar d'akin a bud'e take dan haka ya kutsa kansa a kwance ya tarar da ita tayi lanfa dan ta ji shigowar Ladon Amman tayi kamar bacci take yi, "Lado kenan idan kasan wata ai baka san wata ba daman nasan duk daran dad'ewa zaka zo d'aukarwa mahaifiyarka fansar abin da nayi mata shiyasa kullum cike nake da shirin zuwanka" Zabagegiyar wuk'ar da take gafenta kasancewar Amatullahi ta kashe wutar d'akin shiyasa Lado bai ga wuk'ar ba idonsa ya riga da ya rufe kawai burinsa ya watsawa Amatullahi ruwan zafin a fuska, ya d'aga d'an k'aramin bokitin da ya d'ebo ruwan zafin zai shek'a mata ai kuwa sai jin saukar wuk'ar yayi a hannunsa ya saki bokitin a kasa ruwan zafin ya zuba a k'afafuwansa ya kwala wani irin jijitatcen ihuuuuuuuu.......
Anan zan tsaya sai ku dakace ni a gobe idan Allah ya kaimu domin jin yaya zata kasance tsakanin Lado da Amatullahi shin Aliyu zai fad'awa Abba tak'adirancin da yake yi ko kuma Mami zata hanashi yaya rayuwar Jabir zata kasance anan gaba dashi da mahaifiyarsa da kuma k'anwarsa Nihal ku cigaba da biyo ni 'yar mutanan zazzau domin jin yadda zata kasance.
Da gudu Lado ya fita daga d'akin Amatullahi yana zabga ihu kamar zai zauce, Amatullahi wacce take tsaye a kan gadonta ta shek'e da wata irinyar dariya tare da cewa "An gaya maka ni d'in ta wasa ce, da ka tsaya hannunnaka zan cire gaba d'aya d'an iskan banza". A tsakar gida Lado ya tarar da Inna larai tana jiran fitowarsa zuciyarta cike da farin cikin d'annata zai d'aukar mata fansa, jin ihun Lado da tayi ne yasa hankalinta ya tashi gashi kuma tana tsoron shiga d'akin Amatullahi saboda tana tsoron abin da zai biyo baya gashi daman bata gama jinyar fuskarta ba, da gudu Lado ya k'araso gabanta har yana ban gaje ta yana fad'ar "inna 'yar ta'adda ce Amatullahi 'yar daba ce" ya fad'a a rud'e hannunsa yana fitar da jini kamar da bakin k'warya, Inna a gigice ta ce "me tayi maka Lado?" Lado ya ce "Inna ta sare ni a hannuna, kalli ki gani" da kyar Inna ta iya bud'e idonta domin tun ranar da Amatullahi ta dannata a cikin kaskon mai ta dena gani sosai, kuka Inna larai ta saka tana magana cikin sarkewar murya "gaskiya yarinyar nan ta cika tantiriya,bari ubanta yazo wallahi bazan iya zama da ita ba, ko ni ko ita wallahi" ta k'arasa maganar tare da shigewa d'akinta tana kuka shi kuma Lado ya fita zuwa *BUBA SPEACIAL HOSPITAL* domin a duba shi.
*Wace ce Amatullahi?*