← Book details Daren Aurena Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 46 OF 54

Sashe 46

Daren Aurena Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read

Aliyu kuwa bacci yayi tayi dan sai wajen 11:45am ya tashi ya shiga wanka ya shirya cikin wani yadi mai tsada green colour, ya fito ya nufi falo domin ya gaishe da Hajiya Mama kuma ya ga sahibarsa, Yana shiga ya tarar da Hajiya Mama zaune a kan kujera tana kallon labarai ita kad'ai ce "Assalamu alaikum" Hajiya Mama ta d'ago tana murmushi tare da amsa masa sallamar ta sa "Wa'alaikassalam" Zama yayi a k'asa wajen k'afafuwanta "Ina kwana Hajiyata","Lafiya k'alau d'an albarka ka tashi lafiya" Aliyu ya ce "Lafiya alhamdulillah Ina su Amatullahi ko sun tafi makaranta ne?" Hajiya Mama ta ce "A'a yau ai lahadi ba su je ba suna cikin d'akinsu" Aliyu ya ce "Ohh haka ne fa" Daga nan suka zaune suna yin hirarsu irin ta jika da Kaka.

Khadijatullah wacce tunda Aliyu yayi sallama take son ta fito Amman ganin idanuwan Amatullahi a kanta yasa ta share rumgume take da Affan a hannunta gaba d'aya hankalinta Yana wajen Aliyu, mik'ewa tayi ta nufi hanyar da zata sadata da falon taji muryar Amatullahi tana cewa "Ina za ki je kuma bayan muna hira","Zan je gurin Hajiya Mama" Ba ta jira abin da za ta ce ba ta fita da sauri.

Shahida tayi murmushi ta ce "Sister kin ga Allah ya amshi addu'armu sister ta fara son Yaya Aliyu Haidar" Amatullahi ta ce "Hakane kam dan d'azu ma jiransa ta fita yi a waje shine na je na fatattakota" Dariya Shahida tayi sosai sannan ta ce "Kaii Sister ki barta su soye abin su mana ke kuwa" ita ma dariyar tayi ta ce "To na barsu Sister Shahida" Daga nan suka cigaba da yin hirarsu ta duniya.

Khadijatullah tana fita su ka yi ido biyu da Aliyu murmushi ya sakar mata, nan ta ji wani irin dad'i ya tsarga mata cikin jijiyoyin jikinta, zuciyarta kuwa ta cika da farin ciki, Zama tayi a kan kujera tare da sunkuyar da kanta "Sannu da hutawa Hajiya" Ta fad'a kanta a sunkuye "Yawwa Khadijatullah ya babana har yanzu bacci ya ke yi?","A'a ya tashi idonsa biyu" Hajiya Mama ta tashi tare da zuwa gurin da Khadijatullah take zaune ta karb'i Affan d'in sannan ta shige bedroom d'inta, Shuru falon ya d'auka na tsawon mintina 10 babu Wanda yayi magana a cikin su Aliyu ya kafeta da kyawawan idanuwansa Yana k'ara jin k'aunarta na shiga zuciyarsa, Khadijatullah ta ce "Ina kwana" Murmushi yayi sannan ya amsa "Lafiya alhamdulillah Gimbiyar Mata yau Kuma rowar kyakkyawar fuskar nan ake min ba'a d'ago a kalleni ba","A'a ba rowa nake maka ba" Tayi maganar cike da jin kunyarsa, Amatullahi da Shahida ne suka fito tare da zama kusa da Khadijatullah "Muma ba za'ayi ba mu ba, mun zo a koya mana soyayya" Amatullahi tayi maganar tana kallon Khadijatullah.

Aliyu ya ce "Kun zo dai kawai ku takura mana, muna cikin soyayyarmu, idan soyayya ku ke son koya kowaccenku tayi zuciya ta samo saurayi mana gauraye kawai bamashinshini" Yayi maganar Yana dariya, Shahida ta ce "Laaa Yaya Aliyu Haidar mu ne gaurayen? Gaskiya ka taro match" Amatullahi ta ce "Fad'a masa dai dan kuwa ya taro babban match" Aliyu ya ce "Ahh abin na d'an sauk'i ni da nake da messi, please ku tashi ki bamu waje kun ji darling sisters" Tashi su ka yi Amatullahi ta ce"To zamu ba ku guri ku zanta Amman fa ba mu hak'ura ba" Aliyu ya ce "To na ji" Fita su ka yi tsakar gida suka zauna a kan taburma, Khadijatullah suna fita ta d'ago kai ta kalli Aliyu sannan ta ce "Kaii Yaya Aliyu Amatullahi rigimarta tayi yawa na san ita ta giggib'o Sister suka fito" Dariya yayi sosai sannan ya ce "Bar ni da su ai na fuskanci takura mana suke son su fara yi" Murmushi tayi ba tare da ta ce masa komai ba, nan Aliyu ya shiga kashe Khadijatullah da kalaman soyayya masu ratsa zuciya da jinin jiki.

_Ni kuma na ce Bari na bar ku haka Masoya na rankaya gidan Nihal da Salis iyayen soyayya🤣💃_

*'BANGAREN SALIS DA NIHAL💕💖*

Kwance take a jikinsa tana ta zuba masa shagwab'a iri-iri, shi kuma sai lallab'ata ya ke yi kamar wata kwai "Babyna ni gaskiya ba zan yarda ba, sai mun je tare Allah ba za ka bar ni a gida ba idan kuwa ka fita wallahi kuka zan tayi Kuma har ka dawo ba zan daina ba" Salis ya ce "Haba babyna so kike zuciyata ta buga, tunda haka ne to ni na hak'ura da fitar ma tunda daman yamma tayi" Murmushi Nihal tayi tare da cewa "Da gaske ka ke babyna" Salis ya ce "Eh mana Baby Nafisa kuma Baby Nihal Kuma Babyn baby" Dariya tayi sosai ta ce "Sweetheart duk ni kad'ai wannan sunan, to nagode sosai Babyn baby, can't love you less" D'aukarta yayi kamar wata jaririya suka shige bedroom suka rufe kofa.

_ni kuma er sa ido na ce sai na bi su na ga me za su yi Amman kuma sun kulle kofar da key🤣sai na yanke shawarar kawai nayi gidan Teemarh da Jabir😂_

*'BANGAREN TEEMARH DA JABIR😂💖*

Teemarh tana kwance tana jiran dawowar Jabir ganin har k'arfe 12pm na dare bai dawo ba, ta kifa kanta da guiyoyinta tana kuka kamar ranta zai fita, dan ta san Jabir yana chan yana shek'e ayarsa da yammata dan kuma hausawa sun ce Mai hali baya fasa halinsa, ji tayi an dafata da sauri ta d'ago rinannun idanuwanta ta zubawa Wanda ya dafatan Jabir ne da sauri ta ture hannunsa tare da juyar da fuskarta jefe ta cigaba da yin kukanta, Jabir kuwa duk da cewar baya son Teemarh Amman sai da ya ji hankalinsa ya tashi Dan ya San dalilin kukan na ta ba zai huce na rashin dawowarsa da wuri ba.

Zama yayi kusa da ita tare da kok'arin jiyo da fuskarta, Amman tak'i yarda sai tureshi ta ke yi da ya gaji ya mik'e tsaye tare da d'aukarta cak sannan ya koma ya zauna a kan kujerar Yana rumgume da ita a jikinsa, Teemarh tai-tayi ta kwace Amman ta kasa tana kuka ta fara magana "Tunda ka nuna min ba ka k'aunata kuma ka tsaneni kawai ka rabu da ni ka sakeni na koma gidanmu" Tayi maganar tana cigaba da tureshi, Jabir ya k'ara k'ank'ameta sosai a jikinsa yana cewa "Haba Darling wane dak'ik'in ne ya fad'a miki na tsaneki kuma ba na sonki da har ki ke cewa na sakeki ai darling ni da ke mutukaraba babu mai rabamu dan ko mutuwa ma tare da za mutu da ke please ki tsaya ki saurareni kin ji","Me zan saurara daga bakinka na san club ka je gurin yammatanka ka fad'a min me na rageka dashi ko kuma me suka fini dashi, kyau ko kuma surar jikin ko Kuma......" Bakinta ya toshe mata "Ba su fiki da komai ba darling kuma wallahi ba Wai na je club Dan"........"Dakata Jabir ba na son jin komai daga bakinka".

Da k'arfi ta fisge jikinta daga na shi ta fad'a kan gado tare da rushewa da wani irin kuka Mai cin rai, Jabir ya tashi ya koma kan gado Yana cewa "Darling ki daina kukan nan haka Dan Allah kinji babyn Jabir"

Cikin zafin nama Teemarh ta mik'e daga kwancen da take tana cewa.
"Karka k'ara cemin wani babyn Jabir dan ni ba babynka ba ce, babu ni babu kai ka ji na fad'a maka ka fita idona" Tayi maganar cikin kunar zuci, murmushi Jabir yayi ya ce "Ok am so sorry dear na dena, amman dan Allah ki daure ki saurareni ko da sau d'aya ne kinji baby boo" Teemarh tayi masa wani irin kallo "Ba ni da lokacin da zan saurareka, ka matsa daga kusa da ni dan manzon Allah","Hmmm!" Abin da Jabir ya iya cewa kenan sannan ya koma kan kujera ya zabga tagumi yana kallonta ta cigaba da kukan, wani irin haushin kansa ya fara ji saboda ya san Teemarh tana son shi sosai bai kamata yana yi mata abin da zuciyarta zata k'untata ba, kwantawa yayi a kan kujera a hankali bacci mai nauyi yayi awon gaba da shi, ita kuwa Teemarh sai da tayi kukanta mai isarta bacci 'barawo ya sace ta.

~*BAYAN WATA BIYU✨*~

A yau aka d'aura auren Alhaji Mukhtar da Hajiya Asiya bayan rigingimun da suka faru a tsakaninsu, dan da aka sallameta daga asibitin gidanta ya kai ta inda matarsa ta nuna ba za ta iya zama da ita ba tunda ba matarsa ba ce ta ya ya zai d'auko macen da ba muharramarsa ya kawo ta gidansa, nan suka huce suka bar ta tana ta 'ba'batu ya kai ta d'akinsa, kullum ya zamana ya na gurin Hajiya Asiya a cikin d'akin domin so ya ke ya shawo kanta ya gama da ita amman sam ta k'i yarda ta ce masa ita ba za ta yarda tayi zina ba sai dai ya aureta haka ya amince ba dan yaso ba, wannan shine dalilin da yasa a ka daura auren Hajiya Asiya.

*Ya ku ke ganin wannan drama fans Alhaji Mukhtar ya auri Asiya domin ya cika burinsa a kan ta akwai cakwakiyoyi sosai🤣✨*
Chapter 46 · 0% Book details