Sashe 45
Daren Aurena Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Lado kuwa duk irin abin da ake yi wa mahaifiyarsa ko a jikinsa dan wani abun ma shi yake tsara yadda za'ayi mata kuma shine ya hana a dinga bata abinci sai dai ragowar da aka ci aka rage, saboda a cewarsa wai ta haka za'a horata idan wani ya nemeta da niyyar yayi zina da ita ba za ta yarda ba, Yau kamar kullum Zaituna 'yar k'anwar Inna Larai Hafsatu ta d'auki kwanon abincin da aka tarkatawa Inna Larai abincin a aka ci aka rage ta nufi d'akin kajin "Ke! Ke Zaituna tsaya" Lado wanda ya fito daga d'akinsa ya dakatar da Zaituna daga shiga d'akin, juyowa tayi tare da cewa "Na'am Yaya" Karb'ar kwanon abincin yayi daga hannun Zaituna ya k'arasa d'akin kajin ta window ya jefawa Inna Larai abincin ai kuwa kaji suka yo kanta suna caccakarta suna cin abinci Lado ya saki dariya tare da cewa "Kaii wannan abin yana saka ni nishad'i sosai" Sai ya juya ya shige d'akinsa dan daman abin da ya fito dashi kenan.
Zaituna kuwa hawaye ne suka shiga gangaro mata tana matuk'ar jin tausayin Inna Larai sosai kuma tana son ta taimaka mata amman bata da halin da za ta yi hakan dan kuwa ko ta ce zata taimaka mata Lado ba zai tab'a barin tayi ba, nan wata dabara ta fad'o mata tayi murmushi "Inna insha Allahu zan yi kok'arin na taimaka miki ta wannan hanyar, ba zan bari ki wulak'anta ba ai k'addara tana kan kowa" Tayi maganar a zuciyarta daga nan ta juya ta koma d'akinta.
Inna Larai kuwa kuka take kamar ranta zai fita takaici da bak'in ciki had'e da nadama sun gama kasheta yanzu da bata biyewa D'an Ladi ba da tuni tana chan gidanta babu wanda ya isa yayi mata wannan wulak'anci, anan ta fara tunanin yadda za ta yi domin ta tsaratar da kanta daga wannan uk'ubar da ake yi mata amman ta rasa mafita tayi kuka har ta godewa Allah.
Wajen k'arfe 9:00pm na dare bayan kowa ya kwanta Zaituna ta fito rik'e da kwanon abinci tana sand'a a haka har ta isa d'akin kajin ta shiga chan ta hango Inna Larai ta takure a jikin bango, k'arasawa tayi kusa da ita tare da kiran sunanta "Inna" Da sauri Inna Larai ta d'ago tare da cewa "Na'am Zaituna ke ce?","Eh Inna ni ce" Tayi maganar tare da zama kusa da ita ta bud'e mata kwanon da ta zo dashi Shinkafa da miya ce wacce ta ji kifi "Ga shi Inna ki ci, kuma Insha Allahu kullum da daddare bayan kowa yayi bacci zan dinga kawo miki abinci kina ci" Murmushi Inna Larai tayi hawaye suna bin kuncinta ta ce "Nagode sosai yarinyata, kowa ya guje ni amman kuma ke baki gujeni ba, nagode da kulawarki","bakomai Inna ki yi sauri ki cinye abincin kar wani ya fito" Haka Inna Larai ta karb'i kwanon ta dinga zabga loma daman wata iriyar bak'ar yunwa ta ke ji, gaba d'aya ta cinye abincin, sannan ta mik'awa Zaituna kwanon tare da cewa "nagode" Zaituna ta fita daga d'akin ta nufi na ta d'akin tana sand'a har ta shige ta ja kofar ta kulle, ta ajiye kwanon sannan ta koma kan gado ta kwanta tana jin wani irin dad'i a zuciyarta da ta samu ta taimakawa Inna Larai.
*'BANGAREN ABBA DA AUNTY MURJA🥰💃🏽*
Yau Aunty Murja ta tashi da rashin lafiya komai ta ci sai ta amayo shi, hankalin Abba ya tashi haka ya shiryata suka je asibiti likita yayi mata gwaje-gwaje anan ya gano cewar tana d'auke da d'an k'aramin ciki ne sati hud'u, farin ciki gurin Abba ba'a magana, haka ya rik'e Aunty Murja suka fito daga asibitin suka nufi gida, Aunty Murja gaba d'aya kunyar Abba ta ke ji kamar ta nitse a k'asa, Abba shima ya fuskanci haka, kuma ya ji ya k'ara jin son Aunty Murja a cikin zuciyarsa, suna isa gida ta fito ya zagaya ya bud'ewa Aunty Murja murfin motar ta fito kanta a k'asa tana shirin wucewa ta barshi ya rik'e hannunta "Menene haka kuma Murjanatu? Ba na so ki daina kinji" Kai ta gyad'a masa alamar eh "Yauwa ko kefa kin ga babu inda kika tab'a ganin ance wai mata tana jin kunyar mijinta, ko saboda kina da ciki yanzu shine zaki sauya min ki daina kula dani kamar yadda ki ke yi?","A'a ba zan sauya maka ba" Tayi maganar kanta a k'asa "To d'ago ki kalleni","ba zan iya ba, dan Allah kar ka ce dole sai na kalleka kuma karka yi fushi dani" Abba ya b'ata fuska sannan ya ce "Wato ban isa na ce ki yi abu ba ki yi ko?" Hawaye suka shiga zubo mata dan kuwa ba za ta iya kallonsa ba, gaba d'aya wata iriyar muguwar kunyarsa ta ke ji tun da likita ya sanar masu cewar tana da ciki "Kayi hak'uri dan Allah ba haka ba ne" Tayi maganar cikin muryar kuka.
Abba zuciyarsa tayi matuk'ar shiga bak'in ciki saboda ganin zubar hawayen Aunty Murja amman kuma duk da haka dole ya san yadda zai yi ya cire mata wannan sabuwar kunyar da ta tsiro da ita yau, hannunta ya saki sannan ya nufi hanyar da zata sadashi da babban falon, Aunty Murja ta bi bayanshi tana kuka babu kowa a falon ko da yake babu kowa daman a gidan Teemarh ce sai Jabir shi kuma Jabir ba ya zama a gidan Teemarh kuma ba ko yaushe take fitowa babban falon ba kullum tana d'akinta, Suna shiga d'akin Aunty Murja ta sha gabansa tana kuka kuma har lokacin kanta na k'asa kok'arin tureta Abba yake amman ta rumgumeshi tare da k'ank'ameshi sosai tana kuka "Kayi hak'uri dan Allah zan kalleka wallahi da gaske na ke yi zan kalleka" D'agota Abba yayi yana murmushi "To kalleni" Yayi maganar tare da kafeta da ido, d'agowa tayi ta zuba idanuwanta a cikin na sa tana hawaye "Yauwa ko kefa Matata" Yayi maganar yana goge mata hawaye murmushi Aunty Murja tayi tare da cewa "ka hak'ura kenan Yaya?" Kai ya gyad'a mata alamar eh ta rumgumeshi ya kamata suka zauna a kan kujera yana fad'a mata kalamai masu dad'i.
*Ni kuwa nace to Abba asha soyayya lafiya, amman ku yi a hankali karku kone nayi gidansu Safwan ni kam😂*
*'BANGAREN SAFWAN DA SAFNA🤗❤️🌹*
Kamar yadda yayi mata alk'awarin cewar zai kawo mata Khalid, haka kuwa a ka yi washe gari bayan ya dawo daga office ya biya gidansu Hafsa ya d'auki Khalid bayan ya cewa Hafsan gobe zai dawo dashi suka nufo gida tare dashi, Safna tana zauna tana kallo ta saka t.v a gaba kai sai kayi tunanim cewar kallon film d'in da ake yi ta ke yi saboda yadda ta kaf t.v da ido amman kwata-kwata hankalinta ma baya kan t.v yana kan yaronta da kuma mijinta dan ganin yau Safwan d'in ya dad'e ta san gurin Hafsa ya tafi kuma ga shi bata da damar tambaya sai ya ce tayi masa laifi.
Ta share guntun hawayen da ya zubo mata, ji tayi an dafata tayi saurin d'agowa anan idanuwanta su ka yi tozali da yaronta Khalid cikin tsananin murna ta jawo shi jikinta tana cewa "Yarona kai ne","Eh Mommy ni ne nayi kewarki sosai" Safna ta ce "nima haka darling nayi kewarka sosai i miss you more" Safwan wanda ya hard'e hannuwansa a k'irji yana kallonsu ya had'a hannuwansa guri d'aya tare da yin tafi, da sauri Safna ta kalli gurin da yake sam tama manta dashi kallon Khalid tayi sannan ta ce "je ka d'akinka ka huta ko? Na san ka kwaso gajiya","Eh mommy bacci ma zanyi"Khalid ya ce tare da nufar d'akinsa bai jira jin abin da Safna za ta ce ba.
Kallonta ta maida gurin Safwan wanda ya d'aure fuska kamar wanda aka aikowa da sakon mutuwa, tashi tayi ta matsa kusa dashi tana murmushi "Ruhina ka yi hak'uri kasan nayi missing d'in Khalid sosai, kuma"..........
D'aga mata hannu yayi tare da cewa "yi shuru wannan shine dalilin da yasa nace zan bar yaron chan gurin Hafsa saboda ke kwata-kwata ida yana kusa da ke bakya damuwa da ni ko kuma menene damuwata bakya yin hira da ni gaba d'aya lokacinki yana k'arewa ne a gurin dan haka yanzun nan zan mayar dashi dan ba zai zo ya hana ni jin dad'ina ba"
Safna ta kalleshi ta ce.
*Eid Mubarak 💞✨ Fans Ina yi muku barka da sallah da fatan an ci nama lafiya, aci nama dai a hankali kar azo a dinga ce min Dijartyy a kawo filajin😂*
"Ruhina wallahi ba haka ba ne kai ma kasan ka na da matuk'ar muhimmanci gurina ina sonka ina tsananin k'aunarka Amman tunda ka ce haka insha Allahu zan dinga ajiye duk abin da nake ina kula da kai" Safwan ya ce "To shikenan tunda kin ce haka Ruhina Ina sonki nima fiye da yadda ki ke sona" Murmushi Safna tayi sannan ta ce "To yanzu ka huce ko Ruhina" Kai ya gyad'a alamar eh, tayi kissing d'insa a kunci tare da cewa "Shiyasa nake sonka mijina, to yanzu tashi muje ka yi wanka" Harararta yayi ya ce "Kiyi min wanka dai" Safna ta ce "to shikenan tashi muje nayi maka wanka" Tashi yayi suka shiga d'akin Safwan d'in, toilet suka shiga tare su ka yi wanka sannan suka fito kayan bacci suka saka sannan suka kwanta bacci.
_Yau fa kuyi hak'uri ba zan yi typing mai tsayi ba saboda zan je na ci naman sallah🤣_
*'BANGAREN KHADIJATULLAH DA ALIYU💔💃*
Yau an tashi da ruwan saman tun asuba ake yi sai wajen k'arfe 11:00am na safe aka tsaya Khadijatullah ta fito tsakar gida ta tsaya bata da wani buri irin ta ga Aliyu ya fito ta kalleshi ta ji dad'i a zuciyarta, Amatullahi ce ta fito daga d'aki tana kallon Khadijatullah fuskarta kunshe da murmushi dafa Khadijatullah tayi ta ce "Dijan Yaya Aliyu meya faru?","Bakomai Bestyna me ki ka gani kike tambayata?" Amatullahi ta ce "Kawai dai na ga Mata ta fito tana jiran mijinta ya fito" Harararta Khadijatullah tayi sannan ta shige falon Dan ta San indai ta tsaya to Amatullahi sai ta k'ureta, Amatullahi ta bi bayanta tana yin dariya ciki².
Zaituna kuwa hawaye ne suka shiga gangaro mata tana matuk'ar jin tausayin Inna Larai sosai kuma tana son ta taimaka mata amman bata da halin da za ta yi hakan dan kuwa ko ta ce zata taimaka mata Lado ba zai tab'a barin tayi ba, nan wata dabara ta fad'o mata tayi murmushi "Inna insha Allahu zan yi kok'arin na taimaka miki ta wannan hanyar, ba zan bari ki wulak'anta ba ai k'addara tana kan kowa" Tayi maganar a zuciyarta daga nan ta juya ta koma d'akinta.
Inna Larai kuwa kuka take kamar ranta zai fita takaici da bak'in ciki had'e da nadama sun gama kasheta yanzu da bata biyewa D'an Ladi ba da tuni tana chan gidanta babu wanda ya isa yayi mata wannan wulak'anci, anan ta fara tunanin yadda za ta yi domin ta tsaratar da kanta daga wannan uk'ubar da ake yi mata amman ta rasa mafita tayi kuka har ta godewa Allah.
Wajen k'arfe 9:00pm na dare bayan kowa ya kwanta Zaituna ta fito rik'e da kwanon abinci tana sand'a a haka har ta isa d'akin kajin ta shiga chan ta hango Inna Larai ta takure a jikin bango, k'arasawa tayi kusa da ita tare da kiran sunanta "Inna" Da sauri Inna Larai ta d'ago tare da cewa "Na'am Zaituna ke ce?","Eh Inna ni ce" Tayi maganar tare da zama kusa da ita ta bud'e mata kwanon da ta zo dashi Shinkafa da miya ce wacce ta ji kifi "Ga shi Inna ki ci, kuma Insha Allahu kullum da daddare bayan kowa yayi bacci zan dinga kawo miki abinci kina ci" Murmushi Inna Larai tayi hawaye suna bin kuncinta ta ce "Nagode sosai yarinyata, kowa ya guje ni amman kuma ke baki gujeni ba, nagode da kulawarki","bakomai Inna ki yi sauri ki cinye abincin kar wani ya fito" Haka Inna Larai ta karb'i kwanon ta dinga zabga loma daman wata iriyar bak'ar yunwa ta ke ji, gaba d'aya ta cinye abincin, sannan ta mik'awa Zaituna kwanon tare da cewa "nagode" Zaituna ta fita daga d'akin ta nufi na ta d'akin tana sand'a har ta shige ta ja kofar ta kulle, ta ajiye kwanon sannan ta koma kan gado ta kwanta tana jin wani irin dad'i a zuciyarta da ta samu ta taimakawa Inna Larai.
*'BANGAREN ABBA DA AUNTY MURJA🥰💃🏽*
Yau Aunty Murja ta tashi da rashin lafiya komai ta ci sai ta amayo shi, hankalin Abba ya tashi haka ya shiryata suka je asibiti likita yayi mata gwaje-gwaje anan ya gano cewar tana d'auke da d'an k'aramin ciki ne sati hud'u, farin ciki gurin Abba ba'a magana, haka ya rik'e Aunty Murja suka fito daga asibitin suka nufi gida, Aunty Murja gaba d'aya kunyar Abba ta ke ji kamar ta nitse a k'asa, Abba shima ya fuskanci haka, kuma ya ji ya k'ara jin son Aunty Murja a cikin zuciyarsa, suna isa gida ta fito ya zagaya ya bud'ewa Aunty Murja murfin motar ta fito kanta a k'asa tana shirin wucewa ta barshi ya rik'e hannunta "Menene haka kuma Murjanatu? Ba na so ki daina kinji" Kai ta gyad'a masa alamar eh "Yauwa ko kefa kin ga babu inda kika tab'a ganin ance wai mata tana jin kunyar mijinta, ko saboda kina da ciki yanzu shine zaki sauya min ki daina kula dani kamar yadda ki ke yi?","A'a ba zan sauya maka ba" Tayi maganar kanta a k'asa "To d'ago ki kalleni","ba zan iya ba, dan Allah kar ka ce dole sai na kalleka kuma karka yi fushi dani" Abba ya b'ata fuska sannan ya ce "Wato ban isa na ce ki yi abu ba ki yi ko?" Hawaye suka shiga zubo mata dan kuwa ba za ta iya kallonsa ba, gaba d'aya wata iriyar muguwar kunyarsa ta ke ji tun da likita ya sanar masu cewar tana da ciki "Kayi hak'uri dan Allah ba haka ba ne" Tayi maganar cikin muryar kuka.
Abba zuciyarsa tayi matuk'ar shiga bak'in ciki saboda ganin zubar hawayen Aunty Murja amman kuma duk da haka dole ya san yadda zai yi ya cire mata wannan sabuwar kunyar da ta tsiro da ita yau, hannunta ya saki sannan ya nufi hanyar da zata sadashi da babban falon, Aunty Murja ta bi bayanshi tana kuka babu kowa a falon ko da yake babu kowa daman a gidan Teemarh ce sai Jabir shi kuma Jabir ba ya zama a gidan Teemarh kuma ba ko yaushe take fitowa babban falon ba kullum tana d'akinta, Suna shiga d'akin Aunty Murja ta sha gabansa tana kuka kuma har lokacin kanta na k'asa kok'arin tureta Abba yake amman ta rumgumeshi tare da k'ank'ameshi sosai tana kuka "Kayi hak'uri dan Allah zan kalleka wallahi da gaske na ke yi zan kalleka" D'agota Abba yayi yana murmushi "To kalleni" Yayi maganar tare da kafeta da ido, d'agowa tayi ta zuba idanuwanta a cikin na sa tana hawaye "Yauwa ko kefa Matata" Yayi maganar yana goge mata hawaye murmushi Aunty Murja tayi tare da cewa "ka hak'ura kenan Yaya?" Kai ya gyad'a mata alamar eh ta rumgumeshi ya kamata suka zauna a kan kujera yana fad'a mata kalamai masu dad'i.
*Ni kuwa nace to Abba asha soyayya lafiya, amman ku yi a hankali karku kone nayi gidansu Safwan ni kam😂*
*'BANGAREN SAFWAN DA SAFNA🤗❤️🌹*
Kamar yadda yayi mata alk'awarin cewar zai kawo mata Khalid, haka kuwa a ka yi washe gari bayan ya dawo daga office ya biya gidansu Hafsa ya d'auki Khalid bayan ya cewa Hafsan gobe zai dawo dashi suka nufo gida tare dashi, Safna tana zauna tana kallo ta saka t.v a gaba kai sai kayi tunanim cewar kallon film d'in da ake yi ta ke yi saboda yadda ta kaf t.v da ido amman kwata-kwata hankalinta ma baya kan t.v yana kan yaronta da kuma mijinta dan ganin yau Safwan d'in ya dad'e ta san gurin Hafsa ya tafi kuma ga shi bata da damar tambaya sai ya ce tayi masa laifi.
Ta share guntun hawayen da ya zubo mata, ji tayi an dafata tayi saurin d'agowa anan idanuwanta su ka yi tozali da yaronta Khalid cikin tsananin murna ta jawo shi jikinta tana cewa "Yarona kai ne","Eh Mommy ni ne nayi kewarki sosai" Safna ta ce "nima haka darling nayi kewarka sosai i miss you more" Safwan wanda ya hard'e hannuwansa a k'irji yana kallonsu ya had'a hannuwansa guri d'aya tare da yin tafi, da sauri Safna ta kalli gurin da yake sam tama manta dashi kallon Khalid tayi sannan ta ce "je ka d'akinka ka huta ko? Na san ka kwaso gajiya","Eh mommy bacci ma zanyi"Khalid ya ce tare da nufar d'akinsa bai jira jin abin da Safna za ta ce ba.
Kallonta ta maida gurin Safwan wanda ya d'aure fuska kamar wanda aka aikowa da sakon mutuwa, tashi tayi ta matsa kusa dashi tana murmushi "Ruhina ka yi hak'uri kasan nayi missing d'in Khalid sosai, kuma"..........
D'aga mata hannu yayi tare da cewa "yi shuru wannan shine dalilin da yasa nace zan bar yaron chan gurin Hafsa saboda ke kwata-kwata ida yana kusa da ke bakya damuwa da ni ko kuma menene damuwata bakya yin hira da ni gaba d'aya lokacinki yana k'arewa ne a gurin dan haka yanzun nan zan mayar dashi dan ba zai zo ya hana ni jin dad'ina ba"
Safna ta kalleshi ta ce.
*Eid Mubarak 💞✨ Fans Ina yi muku barka da sallah da fatan an ci nama lafiya, aci nama dai a hankali kar azo a dinga ce min Dijartyy a kawo filajin😂*
"Ruhina wallahi ba haka ba ne kai ma kasan ka na da matuk'ar muhimmanci gurina ina sonka ina tsananin k'aunarka Amman tunda ka ce haka insha Allahu zan dinga ajiye duk abin da nake ina kula da kai" Safwan ya ce "To shikenan tunda kin ce haka Ruhina Ina sonki nima fiye da yadda ki ke sona" Murmushi Safna tayi sannan ta ce "To yanzu ka huce ko Ruhina" Kai ya gyad'a alamar eh, tayi kissing d'insa a kunci tare da cewa "Shiyasa nake sonka mijina, to yanzu tashi muje ka yi wanka" Harararta yayi ya ce "Kiyi min wanka dai" Safna ta ce "to shikenan tashi muje nayi maka wanka" Tashi yayi suka shiga d'akin Safwan d'in, toilet suka shiga tare su ka yi wanka sannan suka fito kayan bacci suka saka sannan suka kwanta bacci.
_Yau fa kuyi hak'uri ba zan yi typing mai tsayi ba saboda zan je na ci naman sallah🤣_
*'BANGAREN KHADIJATULLAH DA ALIYU💔💃*
Yau an tashi da ruwan saman tun asuba ake yi sai wajen k'arfe 11:00am na safe aka tsaya Khadijatullah ta fito tsakar gida ta tsaya bata da wani buri irin ta ga Aliyu ya fito ta kalleshi ta ji dad'i a zuciyarta, Amatullahi ce ta fito daga d'aki tana kallon Khadijatullah fuskarta kunshe da murmushi dafa Khadijatullah tayi ta ce "Dijan Yaya Aliyu meya faru?","Bakomai Bestyna me ki ka gani kike tambayata?" Amatullahi ta ce "Kawai dai na ga Mata ta fito tana jiran mijinta ya fito" Harararta Khadijatullah tayi sannan ta shige falon Dan ta San indai ta tsaya to Amatullahi sai ta k'ureta, Amatullahi ta bi bayanta tana yin dariya ciki².