Sashe 51
Daren Aurena Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Mik'ewa ya yi da sauri ya d'auki wayarsa tare da mukullin motarsa, ya fita daga office d'in bayan ya kulleshi motarsa ya shiga yana tuk'i amman gaba d'aya hankalinsa baya kan titin ya lula tunanin Khadijatullahi da kuma yaronsa Affan, Jabir bai yi aune ba sai ji yayi ya daki wata k'atuwar mota, wanda haka ya yi sanadiyar motarsa ta fad'a cikin wani babban rami ta kama da wuta gaba d'aya motar ta cinye, Innalillahi wa inna'ilaihiraju'un mutanan gurin suke ta faman fad'a koda suka lek'a ramin basu ga alamar akwai mutum ba, dan kuwa komai a cikin motar ya k'one kurmus, da yake wasu a gurin sun san motar Jabir nan aka samu wanda yake da number wayar Alhaji Mansur nan suke fad'a masa Jabir ya yi hatsari kuma gaba d'aya motar ta k'one kuma yana cikin motar, Alhaji Mansur ana fad'a masa haka ya zube a k'asa tare da rushewa da kuka, Aunty Murja ta k'araso tana tambayarsa menene, ya kwashe duk abin aka fad'a masa ya fad'a mata yana kuka "Shikenan yanzu yarona ya mutu, ina tsananin son Jabir kamar raina amman yanzu ya mutu ya bar ni" Aunty Murja gaba d'aya hankalinta ya tashi, haka dai tai-ta rarrashin Alhaji Mansur har ya yi shuru, nan ya d'auki wayarsa ya kira Aliyu, Aliyu wanda yake zaune a falon Hajiya Mama suna hira ya ji wayarsa ta d'auki ruri ya yi tunanin Jabir ne, amman da ya kalli screen d'in wayar ya ga number Abba, ya d'aga jin muryar Abba a chan k'asa k'asa yasa Aliyu ya saka wayar a speaker don ya ji abin da Abban zai ce masa "Aliyu kazo yanzu, Allah ya yi wa d'an uwanka rasuwa a hanyarsa ta dawowa gida ya yi hatsari motar gaba d'aya ta k'one kuma yana cikin motar" Mik'ewa Aliyu ya yi jikinsa na rawa hawaye suka shiga zubo masa, nan da nan gumi ya dinga keto masa ya jik'ashi shark'af "A'a Abba d'an uwana bai mutu ba, yana raye ba zan yarda ba wallahi ba zan yarda ba" Aliyu ya yi maganar tare da yin jifa da wayar, Shahida kuwa hannu ta d'ora akai tare da kurma wani uban ihu "Mun shiga uku yayanmu ya mutu, innalillahi wa'inna ilaihi raju'un" Aliyu kuwa fita ya yi da sauri ya shiga motarsa ya nufi gurin da Jabir d'in ya yi hatsari.
Ya na zuwa gurin nan ya nufi gurin rumin gadan-gadan, da yake akwai hanyar da ake bi a shiga cikin ramin Aliyu yana shiga ramin ya nufi gurin motar Jabir da ta k'one, yana kuka jikinsa ya yi sanyi domin ganin irin yadda motar ta k'one tabbas ya san ya rasa d'an uwansa dan gaba d'aya motar ta zama toka, nishin da ya ji a bayansa ne yasa ya juya da sauri, Aliyu ya mik'e ganin Jabir a kwance cikin jini rumgumeshi ya yi yana jin wani irin farin ciki yana shiga zuciyarsa, d'aukarsa ya yi cak suka fita daga cikin ramin a mota ya sakashi ya nufi asibitin Abbansu, suna isa asibitin Aliyu ya fito daga cikin motar, wasu nurses guda goma suka nufo shi suna tura gadon da ake d'aukar mara lafiya idan an kawoshi, Aliyu ya fito da Jabir ya d'ora shi a kan gadon, nurses d'in suka tura gadon Aliyu yana bin bayansu har aka shiga da Jabir emergency room, Sai a lokacin Aliyu ya dawo cikin hayyacinsa ya zaro 'yar k'aramar wayarsa ya kira Abba ya fad'a masa Jabir bai mutu ba yanzu ma suna asibiti dashi, sannan ya kira Shahida ita ma ya fad'a mata, ko minti goma ba'ayi ba sai ga su Hajiya Mama da Abba sun shigo cikin asibitin suka yo kan Aliyu suna tambayarsa "Ina Jabir d'in" Nan yake nuna musu d'akin da aka shiga da Jabir "Alhamdulillahi Allah mun gode maka, ya ubangiji ka tashi kafad'un wannan bawan na ka" Hajiya Mama ta yi maganar tana kuka, dukansu suka amsa da "Amin" Khadijatullahi ta ce "Yaya Aliyu ka tabbatar Jabir bai mutu ba" Ta yi maganar cikin yanayin damuwa "Eh Dija Mijinki bai mutu ba" Khadijatullahi ta kalli Aliyu cike da mamaki amman ba ta iya cewa komai ba, Teemarh ce ta rumgume Khadijatullahi tana kuka "Dan Allah Khadija ki taimakawa mijina ki yafe masa, ina da tabbacin sanadiyar tunaninki ne yasa ya yi hatsarin nan" Khadijatullahi gaba d'aya ta rud'e ta ma kasa magana, sai bin mutune da ta ke yi da ido, haka dai suka nemi guri kowa ya zauna, kowannansu ka kalli fuskarsa zaka ga tarin damuwa da tashin hankali mara misaltuwa.
*'BANGAREN LADO DA INNA LARAI💃🏽💞*
Durk'ushe yake a gaba mahaifiyar ta sa yana kuka yana neman gafararta "Dan Allah Innata ki yi hak'uri da duk abubuwan da nayi miki ki yafe min na san tabbas ban kyauta miki ba, na zalince ki ni ba d'a na gari ba ne" Inna Larai tayi murmushi ta ce "Bakomai Lado na yafe maka, abin da na shuka ne nake girbarsa" Lado ya ce "Nagode Innata Allah ya saka miki da alkhairi, ki tashi muje d'akina ni zan koma d'akinsu Lawal" Inna Larai ta mik'e Lado tana gaba Lado yana bin ta a baya, ta shiga d'akin Lado, kayansa ya shiga tattarawa yana kaiwa d'akinsu Lawal har ya gama ya zauna suka d'an yi hira da Innar ta sa, daga k'arshe ya yi mata sallama ya fita.
Yana fita su ka yi kicibus da Zaituna, kallonsa tayi cike da girmamawa tana sakar masa murmushi "Yaya dan Allah kayi hak'uri ka yafe min, ban yi maka rashin kunya dan"............. "Yi shuru Zaituna meyasa ki ke ba ni hak'uri, ai gaskiya kika fad'a min kuma nagode da kika dawo da ni hanya madaidaiciya, kuma insha Allahu zan gyara kuskuren da nayi a baya" Murmushi Zaituna tayi ta ce "Indai kayi hakan ni kuma na amince zan aureka, domin kuwa kasan Ina tsananin son Inna" Zaituna tayi maganar tana rufe fuskarta, Lado ya ji matuk'ar dad'in kalaman Zaituna wani farin ciki ya shiga tsarga masa, ita kuma Zaituna ganin kallon da Ladon ya ke yi mata yasa ta shige d'akin da Inna Larai take da gudu tana dariya, shima ya nufi d'akin su Lawal yana jin dad'i a cikin zuciyarsa.
*BAYAN KWANA BIYU✌🏽*
Aka saka ranar auren Zaituna da Lado wata d'aya farin ciki gurin wad'annan masoyan ba'a magana, nan suka shiga nunawa junansu wata iriyar sabuwar k'auna kamar su cinye junansu, kullum suna tare Lado yana zuba mara ruwan kalaman soyayya, ni kuwa er mutan zazzau nace Lado ya za ka yi mana haka Amatullahi fa😅Karka manta ita ce tsohuwar zuma🤣.
*BAYAN AWANNI GOMA SHA BIYAR🤧*
Da taimakon Allah Likitoci su ka yi nasarar, ceto rayuwar Jabir bayan gwagwarmayar da suka sha, kafin su yi nasarar ceto rayuwarsa dan gaba d'aya likitocin jikinsu ya yi sanyi ganin irin yadda jini yake zuba kamar famfo daga jikin Jabir, dakyar suka samu suka yi masa aiki har jinin ya tsaya, Doctor Isham ne ya fito daga d'akin yana gyara rigar jikinsa da sauri Alhaji Mansur ya taresa yana tambayarsa "Ya jikin Jabir" Murmushi Doctor Isham yayi ya ce "Alhamdullahi da taimakon ubangiji mun yi nasarar ceto rayuwar Jabir, yanzu dai mun yi masa allurai nan da awa d'aya zai iya farfad'owa" Kowannansu ya shiga furta "Alhamdulillahi" Doctor Isham ya nufi office d'insa, Nihal ce ta shigo asibitin da gudu tana kuka dan Shahida ta kirata ta fad'a mata Jabir ya yi hatsari "Abbanmu ina Yaya Jabir d'in yake" Abba ya ce "Ki kwantar da hankalinki yana nan lafiya" Shiga d'akin su ka yi gaba d'ayansu, zama su ka yi a kan kujerun dake d'akin suna kallon yadda Jabir d'in ya ji raunika a jikinsa, masu kuka nayi masu tagumi da jimami nayi.
Bayan awa d'aya Jabir ya fara motsi da 'yan yatsun hannunsa tare da kiran sunan Khadijatullahi, ras gaban Khadijatullahi ya yi mummunan bugu, duk da irin yadda ta tsani Jabir yanzu kam wani irin tausayinsa take ji saboda ganin irin yadda gaba d'aya kamanninsa suka chanza "Na'am" Ta amsa tana zubar da wasu zafafan hawaye, hannun Teemarh ta kama suka k'arasa gurin gadon zama su ka yi a kan gadon, Jabir a hankali ya bud'e idanuwansa ya dorasu a kan Teemarh "Zahra" Ya kira sunanta a hankali, duk da irin yadda Teemarh take cikin tashin hankali sai da tayi mamakin a ina Jabir yasan sunan da danginta ne kawai suke fad'a mata "Na'am" Cikin wata iriyar wahalalliyar murya ya ce "Ina Khadijatullahi?" Khadijatullahi ta ce "Gani nan" Ya juya a hankali dan Khadijatullahi ta zauna ta wajen kansa ita kuma Teemarh ta wajen k'afafuwansa, hannuwanta ya kama yana kok'arin fashewa da kuka "Dan Allah ki yafe min, nasan ban kyauta miki ba kuma"......... "Na yafe maka tuntuni Allah ya yafe mana ga baki d'aya" Khadijatullahi ta k'atseshi daga k'arasa maganar da zai yi "Nagode sosai, ina yarona?" Khadijatullahi ta karb'i Affan daga hannun Amatullahi ta ajiyeshi kusa da Jabir tana cewa "Gashi nan" Hannun Affan ya rik'e yana murmushi, gaba d'aya su Abba sun ji matuk'ar dad'in yadda Khadijatullahi tayi wa Jabir kuma sun san nan da 'yan lokaci kad'an burinsu zai cika, wasu kawar da k'iyayyar da Khadijatullahi ta ke yi wa Jabir.
Ya na zuwa gurin nan ya nufi gurin rumin gadan-gadan, da yake akwai hanyar da ake bi a shiga cikin ramin Aliyu yana shiga ramin ya nufi gurin motar Jabir da ta k'one, yana kuka jikinsa ya yi sanyi domin ganin irin yadda motar ta k'one tabbas ya san ya rasa d'an uwansa dan gaba d'aya motar ta zama toka, nishin da ya ji a bayansa ne yasa ya juya da sauri, Aliyu ya mik'e ganin Jabir a kwance cikin jini rumgumeshi ya yi yana jin wani irin farin ciki yana shiga zuciyarsa, d'aukarsa ya yi cak suka fita daga cikin ramin a mota ya sakashi ya nufi asibitin Abbansu, suna isa asibitin Aliyu ya fito daga cikin motar, wasu nurses guda goma suka nufo shi suna tura gadon da ake d'aukar mara lafiya idan an kawoshi, Aliyu ya fito da Jabir ya d'ora shi a kan gadon, nurses d'in suka tura gadon Aliyu yana bin bayansu har aka shiga da Jabir emergency room, Sai a lokacin Aliyu ya dawo cikin hayyacinsa ya zaro 'yar k'aramar wayarsa ya kira Abba ya fad'a masa Jabir bai mutu ba yanzu ma suna asibiti dashi, sannan ya kira Shahida ita ma ya fad'a mata, ko minti goma ba'ayi ba sai ga su Hajiya Mama da Abba sun shigo cikin asibitin suka yo kan Aliyu suna tambayarsa "Ina Jabir d'in" Nan yake nuna musu d'akin da aka shiga da Jabir "Alhamdulillahi Allah mun gode maka, ya ubangiji ka tashi kafad'un wannan bawan na ka" Hajiya Mama ta yi maganar tana kuka, dukansu suka amsa da "Amin" Khadijatullahi ta ce "Yaya Aliyu ka tabbatar Jabir bai mutu ba" Ta yi maganar cikin yanayin damuwa "Eh Dija Mijinki bai mutu ba" Khadijatullahi ta kalli Aliyu cike da mamaki amman ba ta iya cewa komai ba, Teemarh ce ta rumgume Khadijatullahi tana kuka "Dan Allah Khadija ki taimakawa mijina ki yafe masa, ina da tabbacin sanadiyar tunaninki ne yasa ya yi hatsarin nan" Khadijatullahi gaba d'aya ta rud'e ta ma kasa magana, sai bin mutune da ta ke yi da ido, haka dai suka nemi guri kowa ya zauna, kowannansu ka kalli fuskarsa zaka ga tarin damuwa da tashin hankali mara misaltuwa.
*'BANGAREN LADO DA INNA LARAI💃🏽💞*
Durk'ushe yake a gaba mahaifiyar ta sa yana kuka yana neman gafararta "Dan Allah Innata ki yi hak'uri da duk abubuwan da nayi miki ki yafe min na san tabbas ban kyauta miki ba, na zalince ki ni ba d'a na gari ba ne" Inna Larai tayi murmushi ta ce "Bakomai Lado na yafe maka, abin da na shuka ne nake girbarsa" Lado ya ce "Nagode Innata Allah ya saka miki da alkhairi, ki tashi muje d'akina ni zan koma d'akinsu Lawal" Inna Larai ta mik'e Lado tana gaba Lado yana bin ta a baya, ta shiga d'akin Lado, kayansa ya shiga tattarawa yana kaiwa d'akinsu Lawal har ya gama ya zauna suka d'an yi hira da Innar ta sa, daga k'arshe ya yi mata sallama ya fita.
Yana fita su ka yi kicibus da Zaituna, kallonsa tayi cike da girmamawa tana sakar masa murmushi "Yaya dan Allah kayi hak'uri ka yafe min, ban yi maka rashin kunya dan"............. "Yi shuru Zaituna meyasa ki ke ba ni hak'uri, ai gaskiya kika fad'a min kuma nagode da kika dawo da ni hanya madaidaiciya, kuma insha Allahu zan gyara kuskuren da nayi a baya" Murmushi Zaituna tayi ta ce "Indai kayi hakan ni kuma na amince zan aureka, domin kuwa kasan Ina tsananin son Inna" Zaituna tayi maganar tana rufe fuskarta, Lado ya ji matuk'ar dad'in kalaman Zaituna wani farin ciki ya shiga tsarga masa, ita kuma Zaituna ganin kallon da Ladon ya ke yi mata yasa ta shige d'akin da Inna Larai take da gudu tana dariya, shima ya nufi d'akin su Lawal yana jin dad'i a cikin zuciyarsa.
*BAYAN KWANA BIYU✌🏽*
Aka saka ranar auren Zaituna da Lado wata d'aya farin ciki gurin wad'annan masoyan ba'a magana, nan suka shiga nunawa junansu wata iriyar sabuwar k'auna kamar su cinye junansu, kullum suna tare Lado yana zuba mara ruwan kalaman soyayya, ni kuwa er mutan zazzau nace Lado ya za ka yi mana haka Amatullahi fa😅Karka manta ita ce tsohuwar zuma🤣.
*BAYAN AWANNI GOMA SHA BIYAR🤧*
Da taimakon Allah Likitoci su ka yi nasarar, ceto rayuwar Jabir bayan gwagwarmayar da suka sha, kafin su yi nasarar ceto rayuwarsa dan gaba d'aya likitocin jikinsu ya yi sanyi ganin irin yadda jini yake zuba kamar famfo daga jikin Jabir, dakyar suka samu suka yi masa aiki har jinin ya tsaya, Doctor Isham ne ya fito daga d'akin yana gyara rigar jikinsa da sauri Alhaji Mansur ya taresa yana tambayarsa "Ya jikin Jabir" Murmushi Doctor Isham yayi ya ce "Alhamdullahi da taimakon ubangiji mun yi nasarar ceto rayuwar Jabir, yanzu dai mun yi masa allurai nan da awa d'aya zai iya farfad'owa" Kowannansu ya shiga furta "Alhamdulillahi" Doctor Isham ya nufi office d'insa, Nihal ce ta shigo asibitin da gudu tana kuka dan Shahida ta kirata ta fad'a mata Jabir ya yi hatsari "Abbanmu ina Yaya Jabir d'in yake" Abba ya ce "Ki kwantar da hankalinki yana nan lafiya" Shiga d'akin su ka yi gaba d'ayansu, zama su ka yi a kan kujerun dake d'akin suna kallon yadda Jabir d'in ya ji raunika a jikinsa, masu kuka nayi masu tagumi da jimami nayi.
Bayan awa d'aya Jabir ya fara motsi da 'yan yatsun hannunsa tare da kiran sunan Khadijatullahi, ras gaban Khadijatullahi ya yi mummunan bugu, duk da irin yadda ta tsani Jabir yanzu kam wani irin tausayinsa take ji saboda ganin irin yadda gaba d'aya kamanninsa suka chanza "Na'am" Ta amsa tana zubar da wasu zafafan hawaye, hannun Teemarh ta kama suka k'arasa gurin gadon zama su ka yi a kan gadon, Jabir a hankali ya bud'e idanuwansa ya dorasu a kan Teemarh "Zahra" Ya kira sunanta a hankali, duk da irin yadda Teemarh take cikin tashin hankali sai da tayi mamakin a ina Jabir yasan sunan da danginta ne kawai suke fad'a mata "Na'am" Cikin wata iriyar wahalalliyar murya ya ce "Ina Khadijatullahi?" Khadijatullahi ta ce "Gani nan" Ya juya a hankali dan Khadijatullahi ta zauna ta wajen kansa ita kuma Teemarh ta wajen k'afafuwansa, hannuwanta ya kama yana kok'arin fashewa da kuka "Dan Allah ki yafe min, nasan ban kyauta miki ba kuma"......... "Na yafe maka tuntuni Allah ya yafe mana ga baki d'aya" Khadijatullahi ta k'atseshi daga k'arasa maganar da zai yi "Nagode sosai, ina yarona?" Khadijatullahi ta karb'i Affan daga hannun Amatullahi ta ajiyeshi kusa da Jabir tana cewa "Gashi nan" Hannun Affan ya rik'e yana murmushi, gaba d'aya su Abba sun ji matuk'ar dad'in yadda Khadijatullahi tayi wa Jabir kuma sun san nan da 'yan lokaci kad'an burinsu zai cika, wasu kawar da k'iyayyar da Khadijatullahi ta ke yi wa Jabir.