Sashe 49
Daren Aurena Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Hawaye ne suka shiga zubowa Amatullahi, ta mik'e tana goge hawayen na ta da gefen hijabinta "Ke Amatullahi dawo ki zauna" Aliyu ya yi maganar lokacin da Amatullahi take shirin fita daga falon, juyowa ta yi ta koma ta zauna dan ita sam ba ta ma kula da Aliyu yana falon ba, "Meya had'aku?" Ya yi maganar yana kallon Khadijatullahi wacce ita ma shi take kallo "Hmmm!" Abin da Khadijatullahi ta ce kenan "Yaya Aliyu ni ban tab'a yi mata k'arya ba, wallahi da gaske na ke yi maka" Amatullahi ta yi maganar tana kuka "Ai yau kuma kin yi min, kuma ni ba na mu'amala da mak'aryaci" Khadijatullhi ta yi maganar tana hararar Amatullahi, Aliyi ya ce "To ya isa haka, Amatullahi me ki ka yi mata?" Amatullahi ta ce "Ni Yaya Aliyu gurin Jabir na je" Wata iriyar zabura Khadijatullahi ta yi "Me ki ka je yi gurin wannan shegen d'an iskan" Nan Amatullahi ta bata labarin duk abin da take shirin yi wa Jabir d'in domin d'aukar mata fansa ta dora da cewa "Kuma duk zuwan da na ke yi sau d'aya na samu na fara isar masa da sakona, yau kuma da na je shine me shagon ya ke ce min ya daina zuwa club d'in saboda matarsa" Khadijatullahi ta matso kusa da Amatullahi ta rumgumeta tana kuka "Besty meyasa baki fad'a min ba, ki ka yi min shuru kin san wannan d'an iskan, kuma kin san halinsa, bai kamata kina saka kanki a tsari saboda ni ba, dan Allah ki daina saboda idan wani abu ya sameki ba zan tab'a iya yafewa kaina ba" Amatullahi ta d'agota tana goge mata hawayen fuskarta "Ki daina kuka ya isa haka, ka da kanki ya yi ciwo" Murmushi Khadijatullahi ta yi "To na dena dan Allah ki yi hak'uri da"..... Rufe mata baki Amatullahi ta yi "Dan Allah ki manta da komai ai ya wuce, bari na baku wajen ko kuna hirarku na katse ku, Yaya Aliyu a sha soyayya lafiya" Ta yi maganar tana dariya tare da fita daga falon.
_Masu son daren aurena daga farko zuwa inda aka tsaya ya yi min magana ta wannan number 08122188717_
"My Heartbeat wallahi kun burgeni sosai, tunda na ke ban tab'a ganin k'awaye irin ku ba, kuna son junanku kuna tsananin k'aunar junanku, Allah ubangiji ya bar ku tare" Aliyu ya yi maganar yana murmushi "Amin Yayana" Khadijatullahi ta yi maganar ita ma tana sakar masa murmushi, nan suka shiga yin hirarsu irin ta masoya sun kai kusan rabin awa suna hira daga nan su ka yi sallama, Aliyu ya tafi gidan abokinsa musaddik.
⏰5pm
K'arfe biyar na yamma dai-dai Teemarh ta isa gidan Hajiya Mama "Assalamu alaikum" Ta yi sallama tare da shiga cikin gidan, su ka yi ido biyu da Shahida "Laaa Aunty Fatima ke ce" Murmushi Teemarh ta yi tare da k'arasawa gurin da Hajiya Mama ta ke zaune ta tsugunna har k'asa tana gaisheta "Ina wuni Hajiya","Lafiya lau ina d'an duniyar mijin na ki?" Teemarh ta sunkuyar da kai tare da cewa " Yana gida" Tashi ta yi ta koma kusa da Shahida tana cewa "Hmm! Ai babu abin da za ki ce min" Dariya Shahida ta yi ta ce "Ki yi hak'uri Aunty Fatima akasi aka samu, kuma kin san gidan Hajiya Mama idan ka zo,to fa sai ka yi da gaske zaka iya fita" Teemarh ta ce "Gaskiya kam ga Aliyu ma ya k'i dawowa" Teemarh ta kalli su Khadijatullahi ta ce " Sannunku 'yan uwa ya ku ke" Murmushi su ka yi "Lafiya alhamdullahi" Suka amsa a tare "Wai Aunty Fati ina Yaya Jabir" Teemarh ta ce "Yana gida wallahi", "Wannan ita ce matar Jabir" Amatullahi ta yi tambayar tare da kafe Teemarh da ido, ita ma Teemarh jiyowa ta yi tana kallon Amatullahi tana murmushi, Shahida ta ce "Eh mana ita ce, sunanta Aunty Fatima" Amatullahi ta ce "Ohhh lallai kam, kin cika 'yar kasada" Ta yi maganar ciki-ciki, Teemarh ta ce "Sistoo magana ki ke yi ne?" Amatullahi ta yi murmushin yak'e tare da cewa "A'a fa, lazimi na ke yi" Khadijatullahi dariya ce ta kwace mata dan ta ji abin da Amatullahi ta ce, kuma ga maganar da ta fad'awa Teemarh "Tabbas Lazimi kike bestyna" Amatullahi ta kalleta tana murmushi "Bestyna abin k'aunata,me ya baki dariya kuma?" Khadijatullahi ta ce "No! Bakomai, kawai dai lazimin ki ne ya ba ni dariya, ya kamata ki nutsu sosai" Hararar wasa Amatullahi ta hurga mata, tare da d'auko wata hirar ta daban dan ta san indai ta biyewa Khadijatullahi to Teeamarh zata iya fahimtar inda zancensu ya nufa.
Har wajen k'arfe 10pm na dare Teemarh tana gidan Hajiya Mama, Hajiya Mama da ta ga ba ta da niyyar tafiya ta ce "Yau Fatima kwana za ki yi ne?" Teemarh wacce take kwance a kan doguwar kujera ta ce "A'a Hajiya yau zan tafi" Hajiya Mama ta ce "To ikon Allah yaushe za ki tafi kenan, kin san k'arfe nawa yanzu kuwa?" Dariya Teemarh ta yi ta ce "Hajiya Mama na sani mana k'arfe goma har da 'yan mintina, ai Yaya Jabir ne ya ce zai zo ya d'auke ni" Tana rufe bakinta sai ga Jabir ya yi sallama ya shigo falon "Assalamu alaikum" Karaf su ka yi ido biyu da Khadijatullahi, duk da irin yadda ta chanza masa, amman ba zan tab'a mantawa da wannan fuskar ba "Khadijatullahi" Ya kira sunanta a gigice gumi yana k'aryo masa, Yaron da ke kan cinyar Khadijatullahi ya k'urawa ido, shima Affan kallonsa yake yana dariyarsu irin ta yara, yana gwarancinsa don yanzu watan Affan biyar "Kenan wannan yaron nawa ne" Yayi maganar a zuciyarsa, Teemarh ta mik'e ta k'araso gurin da yake tsaya ta ce "Darling lafiya kuwa? Ka santa ne?" Bai kalli inda Teemarh take ba, dan har lokacin idanuwansa suna kan Khadijatullahi da Affan, Amatullahi ta ce "Fatima kina son jin irin rashin mutuncin da mijinki yayi wa 'yar uwata ne?" Da sauri Teemarh ta juya tana kallon Amatullahi ta ce "Meya faru ni na rasa gane kan wannan abin" Amatullahi tayi gajeren murmushi tare da cewa "To yanzu zan warware miki komai, wannan shaid'anin mijin na ki ya auri 'yar uwata, bayan ya gama biyan buk'atarsa da ita ya saketa a cikin daren nan, bai tausaya mata ba, kuma wannan yaron da yake kan cinyarta, d'an wannan shaid'anin mijin na ki ne" Teemarh ta zaro ido domin ta san Jabir ya tab'a yin aure, amman ba ta tab'a yin tunanin ta tambayesa ina matarsa ba, "kina nufin Dijah matar Jabir ce" Cikin muryar b'acin rai Khadijatullahi ta ce "Karki k'ara ce min matarsa domin ni, ba matarsa ba ce Allah ubangiji ya kiyayeni na auri wannan tak'adirin d'an iskan, wancan lokacin da na aureshi akan babu yadda na iya ne" Jabir dai bai iya yin koda motsi daga inda yake ba, barantana har ya iya magana, Hajiya Mama wacce take zaune ta zuba musu idanuwa tana kallonsu ta ce "Kai Jabir shigowa za ka yi ne, ko kuma tsayuwar za ka yi ta yi ne kamar wani gunki" Dakyar Jabir ya fara tafiya gaba d'aya jikinsa a sanyaye yake, Zama ya yi kan kujera nadamar abin da ya yi wa Khadijatullahi ta shiga zuciyarsa, wani irin zafi yake ji a cikin zuciyarsa wanda bai san dalilin jin sa ba, "Hajiya Mama Dan Allah"...... Hajiya Mama ta yi saurin dakatar dashi da cewa "Jabir yanzu dare ya yi ka d'auki matarka ku tafi gida, gobe idan Allah ya kaimu sai mu yi magana" Jabir bai musa mata ba ya amsa mata da "to" Sannan ya mik'e ya nufi hanyar fita daga d'akin, ya juyo ya kalli gurin da Khadijatullahi take, sannan ya fita daga falon, Teemarh ta d'auki Jakarta da mayafinta ta bi bayansa, ita ma jikinta a sanyaye ya ke.
Jabir yana zuwa wajen motar ya bud'e ya shiga, Teemarh ta shiga motar tare da kallonsa zuciyarta a cunkushe "Darling" Ta kira sunanshi muryarta a sanyaye, juyowa ya yi yana kallonta ba tare da ya ce komai ba, sai hawaye da yake zubowa daga cikin idanuwansa zuwa kan kuncinsa, hannunta ta saka tana goge masa hawayen tana yi masa murmushin yak'e "Ka daina kuka ka ji darling insha Allahu komai zai yi dai-dai" Jabir ya sauke ajiyar zuciya "Darling na san nayi wa Khadijatullahi abubuwan da basu dace ba, ban kyauta mata ba sam, idan har ba ta yake min ba tabbas ba zan tab'a yafewa kai na ba" Teemarh ta ce "Karka ce haka darling insha Allahu Dija zata yafe maka ka ji, yanzu tana cikin b'acin rai shiyasa,amman ka barta zuwa d'an wani lokaci kafin nan ta sauko" Murmushin jin dad'i ya yi tare da rumgume Teemarh "Nagode darling nagode sosai, da fatan zaki taimaka min wajen ganin Khadijatullahi ta yafe min","Insha Allahu" Teemarh tayi maganar tana murmushi, haka Jabir ya ja motar duk da cewar ba ya jin dad'in zuciyarsa, amman haka ya daure domin baya son ganin Teemarh cikin damuwa.
*'BANGAREN HAJIYA ASIYA*
_Masu son daren aurena daga farko zuwa inda aka tsaya ya yi min magana ta wannan number 08122188717_
"My Heartbeat wallahi kun burgeni sosai, tunda na ke ban tab'a ganin k'awaye irin ku ba, kuna son junanku kuna tsananin k'aunar junanku, Allah ubangiji ya bar ku tare" Aliyu ya yi maganar yana murmushi "Amin Yayana" Khadijatullahi ta yi maganar ita ma tana sakar masa murmushi, nan suka shiga yin hirarsu irin ta masoya sun kai kusan rabin awa suna hira daga nan su ka yi sallama, Aliyu ya tafi gidan abokinsa musaddik.
⏰5pm
K'arfe biyar na yamma dai-dai Teemarh ta isa gidan Hajiya Mama "Assalamu alaikum" Ta yi sallama tare da shiga cikin gidan, su ka yi ido biyu da Shahida "Laaa Aunty Fatima ke ce" Murmushi Teemarh ta yi tare da k'arasawa gurin da Hajiya Mama ta ke zaune ta tsugunna har k'asa tana gaisheta "Ina wuni Hajiya","Lafiya lau ina d'an duniyar mijin na ki?" Teemarh ta sunkuyar da kai tare da cewa " Yana gida" Tashi ta yi ta koma kusa da Shahida tana cewa "Hmm! Ai babu abin da za ki ce min" Dariya Shahida ta yi ta ce "Ki yi hak'uri Aunty Fatima akasi aka samu, kuma kin san gidan Hajiya Mama idan ka zo,to fa sai ka yi da gaske zaka iya fita" Teemarh ta ce "Gaskiya kam ga Aliyu ma ya k'i dawowa" Teemarh ta kalli su Khadijatullahi ta ce " Sannunku 'yan uwa ya ku ke" Murmushi su ka yi "Lafiya alhamdullahi" Suka amsa a tare "Wai Aunty Fati ina Yaya Jabir" Teemarh ta ce "Yana gida wallahi", "Wannan ita ce matar Jabir" Amatullahi ta yi tambayar tare da kafe Teemarh da ido, ita ma Teemarh jiyowa ta yi tana kallon Amatullahi tana murmushi, Shahida ta ce "Eh mana ita ce, sunanta Aunty Fatima" Amatullahi ta ce "Ohhh lallai kam, kin cika 'yar kasada" Ta yi maganar ciki-ciki, Teemarh ta ce "Sistoo magana ki ke yi ne?" Amatullahi ta yi murmushin yak'e tare da cewa "A'a fa, lazimi na ke yi" Khadijatullahi dariya ce ta kwace mata dan ta ji abin da Amatullahi ta ce, kuma ga maganar da ta fad'awa Teemarh "Tabbas Lazimi kike bestyna" Amatullahi ta kalleta tana murmushi "Bestyna abin k'aunata,me ya baki dariya kuma?" Khadijatullahi ta ce "No! Bakomai, kawai dai lazimin ki ne ya ba ni dariya, ya kamata ki nutsu sosai" Hararar wasa Amatullahi ta hurga mata, tare da d'auko wata hirar ta daban dan ta san indai ta biyewa Khadijatullahi to Teeamarh zata iya fahimtar inda zancensu ya nufa.
Har wajen k'arfe 10pm na dare Teemarh tana gidan Hajiya Mama, Hajiya Mama da ta ga ba ta da niyyar tafiya ta ce "Yau Fatima kwana za ki yi ne?" Teemarh wacce take kwance a kan doguwar kujera ta ce "A'a Hajiya yau zan tafi" Hajiya Mama ta ce "To ikon Allah yaushe za ki tafi kenan, kin san k'arfe nawa yanzu kuwa?" Dariya Teemarh ta yi ta ce "Hajiya Mama na sani mana k'arfe goma har da 'yan mintina, ai Yaya Jabir ne ya ce zai zo ya d'auke ni" Tana rufe bakinta sai ga Jabir ya yi sallama ya shigo falon "Assalamu alaikum" Karaf su ka yi ido biyu da Khadijatullahi, duk da irin yadda ta chanza masa, amman ba zan tab'a mantawa da wannan fuskar ba "Khadijatullahi" Ya kira sunanta a gigice gumi yana k'aryo masa, Yaron da ke kan cinyar Khadijatullahi ya k'urawa ido, shima Affan kallonsa yake yana dariyarsu irin ta yara, yana gwarancinsa don yanzu watan Affan biyar "Kenan wannan yaron nawa ne" Yayi maganar a zuciyarsa, Teemarh ta mik'e ta k'araso gurin da yake tsaya ta ce "Darling lafiya kuwa? Ka santa ne?" Bai kalli inda Teemarh take ba, dan har lokacin idanuwansa suna kan Khadijatullahi da Affan, Amatullahi ta ce "Fatima kina son jin irin rashin mutuncin da mijinki yayi wa 'yar uwata ne?" Da sauri Teemarh ta juya tana kallon Amatullahi ta ce "Meya faru ni na rasa gane kan wannan abin" Amatullahi tayi gajeren murmushi tare da cewa "To yanzu zan warware miki komai, wannan shaid'anin mijin na ki ya auri 'yar uwata, bayan ya gama biyan buk'atarsa da ita ya saketa a cikin daren nan, bai tausaya mata ba, kuma wannan yaron da yake kan cinyarta, d'an wannan shaid'anin mijin na ki ne" Teemarh ta zaro ido domin ta san Jabir ya tab'a yin aure, amman ba ta tab'a yin tunanin ta tambayesa ina matarsa ba, "kina nufin Dijah matar Jabir ce" Cikin muryar b'acin rai Khadijatullahi ta ce "Karki k'ara ce min matarsa domin ni, ba matarsa ba ce Allah ubangiji ya kiyayeni na auri wannan tak'adirin d'an iskan, wancan lokacin da na aureshi akan babu yadda na iya ne" Jabir dai bai iya yin koda motsi daga inda yake ba, barantana har ya iya magana, Hajiya Mama wacce take zaune ta zuba musu idanuwa tana kallonsu ta ce "Kai Jabir shigowa za ka yi ne, ko kuma tsayuwar za ka yi ta yi ne kamar wani gunki" Dakyar Jabir ya fara tafiya gaba d'aya jikinsa a sanyaye yake, Zama ya yi kan kujera nadamar abin da ya yi wa Khadijatullahi ta shiga zuciyarsa, wani irin zafi yake ji a cikin zuciyarsa wanda bai san dalilin jin sa ba, "Hajiya Mama Dan Allah"...... Hajiya Mama ta yi saurin dakatar dashi da cewa "Jabir yanzu dare ya yi ka d'auki matarka ku tafi gida, gobe idan Allah ya kaimu sai mu yi magana" Jabir bai musa mata ba ya amsa mata da "to" Sannan ya mik'e ya nufi hanyar fita daga d'akin, ya juyo ya kalli gurin da Khadijatullahi take, sannan ya fita daga falon, Teemarh ta d'auki Jakarta da mayafinta ta bi bayansa, ita ma jikinta a sanyaye ya ke.
Jabir yana zuwa wajen motar ya bud'e ya shiga, Teemarh ta shiga motar tare da kallonsa zuciyarta a cunkushe "Darling" Ta kira sunanshi muryarta a sanyaye, juyowa ya yi yana kallonta ba tare da ya ce komai ba, sai hawaye da yake zubowa daga cikin idanuwansa zuwa kan kuncinsa, hannunta ta saka tana goge masa hawayen tana yi masa murmushin yak'e "Ka daina kuka ka ji darling insha Allahu komai zai yi dai-dai" Jabir ya sauke ajiyar zuciya "Darling na san nayi wa Khadijatullahi abubuwan da basu dace ba, ban kyauta mata ba sam, idan har ba ta yake min ba tabbas ba zan tab'a yafewa kai na ba" Teemarh ta ce "Karka ce haka darling insha Allahu Dija zata yafe maka ka ji, yanzu tana cikin b'acin rai shiyasa,amman ka barta zuwa d'an wani lokaci kafin nan ta sauko" Murmushin jin dad'i ya yi tare da rumgume Teemarh "Nagode darling nagode sosai, da fatan zaki taimaka min wajen ganin Khadijatullahi ta yafe min","Insha Allahu" Teemarh tayi maganar tana murmushi, haka Jabir ya ja motar duk da cewar ba ya jin dad'in zuciyarsa, amman haka ya daure domin baya son ganin Teemarh cikin damuwa.
*'BANGAREN HAJIYA ASIYA*