Sashe 21
Daren Aurena Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
D'akin Shahida ta shiga jikinta sai rawa yake yi, Shahida tana kwance a kan gadonta wani irin mugun bacci ne yake kok'arin kwasheta, ta ji shigowar Teemarh da sauri ta tashi tana cewa "Aunty Fatima meyafaru? Ba ki da lafiya ne?" tayi maganar cike da tsantsar damuwa ganin yadda jikin Teemarh sai rawa yake "Shahida lafiyata 'kalau, ina son na shiga toilet d'inki" da sauri Shahida ta sauko daga kan gadon ta bud'e mata toilet d'in, Teemarh ta shiga sai da ta rage kayan jikinta sannan ta sakarwa kanta ruwan sanyi, a hankali ta fara samun nutsuwa, ta d'auki kusan rabin awa a cikin toilet d'in sannan ta mayar da kayan jikinta ta fito, in da ta sami Shahida a tsaye ta zabga tagumi, Teemarh tayi murmushi tare da dafata tana cewa "K'anwata lafiya kike kuwa?" Shahida ta ce "Aunty Fatima na ga kin shigo ne kamar ba'a cikin hayyacinki kike ba" Wani irin k'ayatatcen murmushi tayi tare da cewa "Haba kawai dai na d'an shiga cikin damuwana amman yanzu k'alau nake","To alhamdulillahi"Shahida ta fad'a tana murmushi, daga nan suka koma a kan kujera Teemarh ta cewa Shahida ta kunna mata tashar da ake So k'addarar zuciya domin ta cigaba da kallo, Shahida ta ce mata "to" sannan ta kai mata tashar ai kuwa tayi sa'a ba'a gama episode d'in ba dan haka suka zauna suna kallo.
*'BANGAREN AMATULLAHI*
Lado ne da Amatullahi zaune a kan taburma suna hirar su ta masoya, Amatullahi ta kalli Lado sannan ta ce "Baby wai kwana biyu na ga Innah tana d'aukar kajinka tana siyarwa,lafiya kuwa?" hankalin Lado yayi matuk'ar tashi domin kuwa haka Innah ta ce masa mutuwa kajin suke yi amman kuma yanzu Amatullahi ta ce siyarwa take yi, Amatullahi kuwa tana sa ne ta fad'a masa domin kuwa ta ji lokacin da Innar take ce masa kajin mutuwa suke yi, ita kuma ta k'uduri niyyar sai ta fad'a masa gaskiya domin ya san wacece uwarsa.
Lado ya kalli Amatullahi ita ma shi take kallo ya ce "wai da gaske kike sweety Inna siyar min da kaji take yi?" Amatullahi ta ce "wallahi baby da gaske nake siyar da kajin take yi, amman ai nayi tunanin da sanin ka take siyarwa" hawaye ne ya fara zuba daga cikin idonsa yana fad'ar "Yanzu duk irin yadda nake yi wa Inna biyayya kuma nake nuna mata tsantsar soyayya, ina mata duk abin da take so dan ta ji dad'i amman tayi min haka ta yaudare ni" Amatullahi ta kawar da kan ta gefe tare da tab'e baki, zuciyarta fal farin ciki "wannan so min tab'i ne ma, yanzu aka fara wasan" ta fad'a a zuciyarta.
Lado ya mik'e yayi waje zuciyarsa na k'una kamar garwashin wuta, ji yake kamar ya bi Inna gidan baffa Usmanu domin yau a chan ta wuni, "amman bakomai ai zata dawo ta same sa, dan kuwa ba zai yarda ba da wannan ha'incin ba" yayi maganar a zuciyarsa.
Amatullahi kuwa Lado yana fita ta bi bayanshi da kallo tare da tintsirewa da wata iriyar mahaukaciyar dariya, "Kad'an ma ku ka fara gani wallahi, sai kun biya abin da ku kai min" ta fad'a a fili daga nan ta tashi tayi d'akinta ta kwanta tana rera wak'a zuciyarta fal da murna.
*BAYAN SATI BIYU💥*
Sauri sauri gudu gudu take ta isa gidan Hajiya Mama saboda yau ba ta samu ta fito da wuri ba, saboda jikin Khadijatullahi da yayi tsanani, tana isa gidan ta shiga da sallama d'auke a bakinta "Assalamu alaikum" Hajiya Mama da Alhaji Mansur suna zaune a tsakar gidan a kan taburma suna hirar su ta uwa da 'ya abin gwanin ban sha'awa suka amsa mata sallamar gaba d'ayansu "Wa'alaikumussalam" Aunty Murja ta k'arasa ta gaisar da su "Ina kwana Hajiya" Hajiya Mama ta amsa da "Lafiya k'alau Murjanatu yau kin dad'e nayi tunanin ba za ki zo ba ma" Aunty Murja ta ce "Wallahi Hajiya yau Khadijatullahi ce jikin nata yayi tsanani sosai shiyasa amman yanzu ta ji sauk'i", "Allah sarki, Allah ya bata lafiya" Hajiya Mama ta fad'a "Amin" Aunty Murja ta ce sannan ta kalli gurin da Alhaji Mansur ya ke zaune suka had'a ido shima gaisar da shi tayi sannan ta tashi ta shiga share gidan gaba d'aya sannan ta koma kitchen ta d'ebo kwanukan wanke-wanke sai da ta wanke su gaba d'aya suka fita tas, ta kife su gaba daya sannan ta dawo ta d'ora girki, wani littafi ta gani a kan window ta d'auke shi *Hajna* ta ga an rubutu da babba baki.
Duba sunan marubuciyar tayi sai ta ga *Queen Nasmarh* wani irin farin ciki ne ya kamata domin kuwa tana neman littafin sosai, Hajiya Mama ta kalleta tana cewa "to sarkin karance-karance za'a fara kenan" sunkuyar da kanta Aunty Murja tayi sannan ta ajiye littafin ta shige d'akin Hajiya Mama, Alhaji Mansur ya bi ta da kallo yana sak'a abubuwa da yawa a cikin ransa.
*'BANGAREN SAFWAN*
Gaba d'aya Safna ta chanzawa Safwan ba ta yi masa girki ta daina kula dashi ta daina gyara gidan haka zata bar gidan kaca-kaca kamar babu mutane a cikinsa duk tana yin haka ne dan Safwan ya hak'ura da k'ara auran saboda ta san duk abubuwan da ta daina yi Safwan yana son su sosai musamman kulawa da tsafta domin Safwan mutum ne mai son kulawa kuma baya son k'azanta.
Shi kuwa Safwan ya nuna mata kamar bai san abin da take yi ba duk da kuwa abubuwan da take yi suna matuk'ar k'ona masa rai, amman ya k'uduri niyyar sai ya koya mata hankali kuma aure ne zai k'ara shi babu fashi da zarar ya shawo kan Hafsa ta sauko, tunda daman Safna ce silar rabuwarsa da Hafsan, domin ta samu ta auri Safwan shine ta had'a baki da wani domin su b'ata Hafsan a gurin Safwan, daga k'arshe kuma Safwan ya gano gaskiyar.
Zaune yake a d'akinsa yana kallon wani new a tashar *BBC Hausa* Safna ta banko kofar ta shigo tana huci kamar wata tsohuwar zakanya, Kallo d'aya Safwan yayi mata ya d'auke kansa ya cigaba da kallonsa, a kansa ta tsaya tana kiran sunansa "Safwan!Safwan!!Safwan da kai na ke magana fa" wani irin kallo yayi mata jin irin yadda take kiransa cike da gadara ji yake kamar ya tsinka mata mari amman kuma hakan ba halinsa ba ne dukan mace, "Safna ina matuk'ar hak'urin zama da ke, amman ina baki shawarar karki bari ki kai ni k'arshe domin kuwa komai zai iya faruwa", "Safwan ai baka nemi zaman lafiya ba tunda har ka na shirin auro wata shashasha, mai halin dabbobi, kuma..............." ai bata k'arasa ba sai ji tayi Safwan ya da ka mata wata iriyar tsawa wacce sai da ta jijita ta tayi baya da sauri jikinta har tsima yake yi.
"Safna ki tausasa harshen ki, ka da ki sake ki zagi Hafsa domin kuwa yanzu nan zan yi miki abin da baki yi tunani ba, domin Hafsa rayuwata ce kuma zuciyata". Safna ta fita daga d'akin da gudu tana kuka, kai tsaye d'akinta ta huce ta fad'a a kan gado, maganar Safwan tana k'ara dawo mata a zuciya *Domin Hafsa rayuwata ce kuma zuciyata* tana kuka take cewa "wallahi Safwan ba ka isa ba ko ka k'i ko ka so da ni kad'ai zaka rayu". A haka dai bacci b'arawo ya sace ta.
*'BANGAREN AMARYA NIHAL😂*
Kwance take a kan gadonta hawaye yana zuba daga cikin idanuwanta ita dai lamarin Salis yana bata tsoro kullum idan ya kusanceta kafin ya gama sai ta suma kusan uku ko biyu, kuma gashi baya kusantarta sau d'aya sai dai sau uku safe, rana da kuma dare ko da kuwa ace yana d'akin uwar gidansa sai ya zo gurinta.
Sallamar da aka yi ne ya dawo da ita daga dogon tunanin da ta shiga, a zabure ta mik'e jikinta ya fara rawa hawaye suka fara zuba daga idanuwanta "Dan Allah Yaya Salis yayi hak'uri wallahi ba na jin dad'i yau" murmushi yayi sannan ya ce "Menene na kuka babyna haba dan Allah ki daina kin ji" ba ta ce mata komai ba sai kukan da take yi, hawa kan gadon yayi sannan ta kai hannunsa wuyanta yana cewa "Me ke damunki zazzab'i ko kuma me?" Cikin rawam murya ta ce "Zazzab'i", "Wayyo Allah babyna sorry bari in d'auko miki magani ki sha, ko kuma tashi mu tafi asibiti" mik'ewa tayi da sauri ta d'auki mayafinta ta yafa, Salis ya tashi kenan sai suka ji a turo kofar da sauri Talatu ce tare da yaronta, fuskarta d'auke da fushi.
"Munafikin Allah ta'ala shi ne kace min kana zuwa yanzu zaka dawo ashe gurin wannan shafaffiyar ka zo, bayan kuma kasan yau ba'a d'akinta ka ke ba", murmushi yayi sannan ya ce "Talatu kenan, to ai gurin matata na zo dan haka ba wani abu mugun abu na aikata ba", harara Talatu ta shiga wurga musu ji take kamar ta shak'e Nihal domin wani irin haushinta take ji, domin tun da ya aureta Salis ya rage yin sex da ita, wani lokacin ma ba'a son ransa yake kusantarta ba wanda a da ba haka yake mata ba, amman ta san maganinta zasu had'u da ita tana nan tana tara ta, Salis ta kalla sannan ta ce masa "Ka zo mu tafi to" Nihal ta kallesa sannan ta ce "Yaya Salis ka je kawai na ji sauk'i zan sha magani" ta fad'a sannan ta koma ta zauna a kan gadon, Salis ya fita daga d'akin tare da Talatu, Nihal tayi saurin zuwa ta kulle kofar ta saka key ta sauke ajiyar zuciya, tare da godewa Allah.
Haka ta koma kan gadon farin ciki fal zuciyarta ji take kamar ta zuba ruwa a k'asa ta sha, yau dai ta huta da wannan jarababben namijin (ni kuwa nace nihal daga baya kenan wai anyi sadaka da karuwa🤣😂).
*'BANGAREN ABBA*
*'BANGAREN AMATULLAHI*
Lado ne da Amatullahi zaune a kan taburma suna hirar su ta masoya, Amatullahi ta kalli Lado sannan ta ce "Baby wai kwana biyu na ga Innah tana d'aukar kajinka tana siyarwa,lafiya kuwa?" hankalin Lado yayi matuk'ar tashi domin kuwa haka Innah ta ce masa mutuwa kajin suke yi amman kuma yanzu Amatullahi ta ce siyarwa take yi, Amatullahi kuwa tana sa ne ta fad'a masa domin kuwa ta ji lokacin da Innar take ce masa kajin mutuwa suke yi, ita kuma ta k'uduri niyyar sai ta fad'a masa gaskiya domin ya san wacece uwarsa.
Lado ya kalli Amatullahi ita ma shi take kallo ya ce "wai da gaske kike sweety Inna siyar min da kaji take yi?" Amatullahi ta ce "wallahi baby da gaske nake siyar da kajin take yi, amman ai nayi tunanin da sanin ka take siyarwa" hawaye ne ya fara zuba daga cikin idonsa yana fad'ar "Yanzu duk irin yadda nake yi wa Inna biyayya kuma nake nuna mata tsantsar soyayya, ina mata duk abin da take so dan ta ji dad'i amman tayi min haka ta yaudare ni" Amatullahi ta kawar da kan ta gefe tare da tab'e baki, zuciyarta fal farin ciki "wannan so min tab'i ne ma, yanzu aka fara wasan" ta fad'a a zuciyarta.
Lado ya mik'e yayi waje zuciyarsa na k'una kamar garwashin wuta, ji yake kamar ya bi Inna gidan baffa Usmanu domin yau a chan ta wuni, "amman bakomai ai zata dawo ta same sa, dan kuwa ba zai yarda ba da wannan ha'incin ba" yayi maganar a zuciyarsa.
Amatullahi kuwa Lado yana fita ta bi bayanshi da kallo tare da tintsirewa da wata iriyar mahaukaciyar dariya, "Kad'an ma ku ka fara gani wallahi, sai kun biya abin da ku kai min" ta fad'a a fili daga nan ta tashi tayi d'akinta ta kwanta tana rera wak'a zuciyarta fal da murna.
*BAYAN SATI BIYU💥*
Sauri sauri gudu gudu take ta isa gidan Hajiya Mama saboda yau ba ta samu ta fito da wuri ba, saboda jikin Khadijatullahi da yayi tsanani, tana isa gidan ta shiga da sallama d'auke a bakinta "Assalamu alaikum" Hajiya Mama da Alhaji Mansur suna zaune a tsakar gidan a kan taburma suna hirar su ta uwa da 'ya abin gwanin ban sha'awa suka amsa mata sallamar gaba d'ayansu "Wa'alaikumussalam" Aunty Murja ta k'arasa ta gaisar da su "Ina kwana Hajiya" Hajiya Mama ta amsa da "Lafiya k'alau Murjanatu yau kin dad'e nayi tunanin ba za ki zo ba ma" Aunty Murja ta ce "Wallahi Hajiya yau Khadijatullahi ce jikin nata yayi tsanani sosai shiyasa amman yanzu ta ji sauk'i", "Allah sarki, Allah ya bata lafiya" Hajiya Mama ta fad'a "Amin" Aunty Murja ta ce sannan ta kalli gurin da Alhaji Mansur ya ke zaune suka had'a ido shima gaisar da shi tayi sannan ta tashi ta shiga share gidan gaba d'aya sannan ta koma kitchen ta d'ebo kwanukan wanke-wanke sai da ta wanke su gaba d'aya suka fita tas, ta kife su gaba daya sannan ta dawo ta d'ora girki, wani littafi ta gani a kan window ta d'auke shi *Hajna* ta ga an rubutu da babba baki.
Duba sunan marubuciyar tayi sai ta ga *Queen Nasmarh* wani irin farin ciki ne ya kamata domin kuwa tana neman littafin sosai, Hajiya Mama ta kalleta tana cewa "to sarkin karance-karance za'a fara kenan" sunkuyar da kanta Aunty Murja tayi sannan ta ajiye littafin ta shige d'akin Hajiya Mama, Alhaji Mansur ya bi ta da kallo yana sak'a abubuwa da yawa a cikin ransa.
*'BANGAREN SAFWAN*
Gaba d'aya Safna ta chanzawa Safwan ba ta yi masa girki ta daina kula dashi ta daina gyara gidan haka zata bar gidan kaca-kaca kamar babu mutane a cikinsa duk tana yin haka ne dan Safwan ya hak'ura da k'ara auran saboda ta san duk abubuwan da ta daina yi Safwan yana son su sosai musamman kulawa da tsafta domin Safwan mutum ne mai son kulawa kuma baya son k'azanta.
Shi kuwa Safwan ya nuna mata kamar bai san abin da take yi ba duk da kuwa abubuwan da take yi suna matuk'ar k'ona masa rai, amman ya k'uduri niyyar sai ya koya mata hankali kuma aure ne zai k'ara shi babu fashi da zarar ya shawo kan Hafsa ta sauko, tunda daman Safna ce silar rabuwarsa da Hafsan, domin ta samu ta auri Safwan shine ta had'a baki da wani domin su b'ata Hafsan a gurin Safwan, daga k'arshe kuma Safwan ya gano gaskiyar.
Zaune yake a d'akinsa yana kallon wani new a tashar *BBC Hausa* Safna ta banko kofar ta shigo tana huci kamar wata tsohuwar zakanya, Kallo d'aya Safwan yayi mata ya d'auke kansa ya cigaba da kallonsa, a kansa ta tsaya tana kiran sunansa "Safwan!Safwan!!Safwan da kai na ke magana fa" wani irin kallo yayi mata jin irin yadda take kiransa cike da gadara ji yake kamar ya tsinka mata mari amman kuma hakan ba halinsa ba ne dukan mace, "Safna ina matuk'ar hak'urin zama da ke, amman ina baki shawarar karki bari ki kai ni k'arshe domin kuwa komai zai iya faruwa", "Safwan ai baka nemi zaman lafiya ba tunda har ka na shirin auro wata shashasha, mai halin dabbobi, kuma..............." ai bata k'arasa ba sai ji tayi Safwan ya da ka mata wata iriyar tsawa wacce sai da ta jijita ta tayi baya da sauri jikinta har tsima yake yi.
"Safna ki tausasa harshen ki, ka da ki sake ki zagi Hafsa domin kuwa yanzu nan zan yi miki abin da baki yi tunani ba, domin Hafsa rayuwata ce kuma zuciyata". Safna ta fita daga d'akin da gudu tana kuka, kai tsaye d'akinta ta huce ta fad'a a kan gado, maganar Safwan tana k'ara dawo mata a zuciya *Domin Hafsa rayuwata ce kuma zuciyata* tana kuka take cewa "wallahi Safwan ba ka isa ba ko ka k'i ko ka so da ni kad'ai zaka rayu". A haka dai bacci b'arawo ya sace ta.
*'BANGAREN AMARYA NIHAL😂*
Kwance take a kan gadonta hawaye yana zuba daga cikin idanuwanta ita dai lamarin Salis yana bata tsoro kullum idan ya kusanceta kafin ya gama sai ta suma kusan uku ko biyu, kuma gashi baya kusantarta sau d'aya sai dai sau uku safe, rana da kuma dare ko da kuwa ace yana d'akin uwar gidansa sai ya zo gurinta.
Sallamar da aka yi ne ya dawo da ita daga dogon tunanin da ta shiga, a zabure ta mik'e jikinta ya fara rawa hawaye suka fara zuba daga idanuwanta "Dan Allah Yaya Salis yayi hak'uri wallahi ba na jin dad'i yau" murmushi yayi sannan ya ce "Menene na kuka babyna haba dan Allah ki daina kin ji" ba ta ce mata komai ba sai kukan da take yi, hawa kan gadon yayi sannan ta kai hannunsa wuyanta yana cewa "Me ke damunki zazzab'i ko kuma me?" Cikin rawam murya ta ce "Zazzab'i", "Wayyo Allah babyna sorry bari in d'auko miki magani ki sha, ko kuma tashi mu tafi asibiti" mik'ewa tayi da sauri ta d'auki mayafinta ta yafa, Salis ya tashi kenan sai suka ji a turo kofar da sauri Talatu ce tare da yaronta, fuskarta d'auke da fushi.
"Munafikin Allah ta'ala shi ne kace min kana zuwa yanzu zaka dawo ashe gurin wannan shafaffiyar ka zo, bayan kuma kasan yau ba'a d'akinta ka ke ba", murmushi yayi sannan ya ce "Talatu kenan, to ai gurin matata na zo dan haka ba wani abu mugun abu na aikata ba", harara Talatu ta shiga wurga musu ji take kamar ta shak'e Nihal domin wani irin haushinta take ji, domin tun da ya aureta Salis ya rage yin sex da ita, wani lokacin ma ba'a son ransa yake kusantarta ba wanda a da ba haka yake mata ba, amman ta san maganinta zasu had'u da ita tana nan tana tara ta, Salis ta kalla sannan ta ce masa "Ka zo mu tafi to" Nihal ta kallesa sannan ta ce "Yaya Salis ka je kawai na ji sauk'i zan sha magani" ta fad'a sannan ta koma ta zauna a kan gadon, Salis ya fita daga d'akin tare da Talatu, Nihal tayi saurin zuwa ta kulle kofar ta saka key ta sauke ajiyar zuciya, tare da godewa Allah.
Haka ta koma kan gadon farin ciki fal zuciyarta ji take kamar ta zuba ruwa a k'asa ta sha, yau dai ta huta da wannan jarababben namijin (ni kuwa nace nihal daga baya kenan wai anyi sadaka da karuwa🤣😂).
*'BANGAREN ABBA*