Sashe 38
Daren Aurena Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Sanye take da wata doguwar riga tana share d'akin rigar tayi matuk'ar kamata sosai, ji tayi an bud'e kofar d'akin da sauri ta d'ago kai suka had'a ido da Jabir wanda yake tsaye a bakin kofar ya hard'e hannuwansa a k'irjinsa yana kallonta yana murmushi, a hankali kuma ya tako zuwa inda take "Love d'inta sannunki da aiki" Kallonsa tayi kamar ba za ta yi magana ba sai kuma ta ce "yawwa sannunka" Sannan ta cigaba da yin sharar sai da ta gama share d'akin gaba d'aya sannan ta zauna a ksn kujera ta kunna t.v, tashar Arewa 24 ta kai ta tarar ana yin episode d'in *k'addarar rayuwa* wani irin murmushi tayi dan tana bala'in son film d'in, Jabir yana kallonta dan yana tsaye a gurin da ta huce ta barshi ya k'i motsawa.
Sai da aka gama episode d'in ta juya dan ta ga inda Jabir d'in yayi dan ta ga yau bai takura mata ba, dan tayi tunanin ma ko ya fita daga d'akin ne, mamaki ya kamata ganinshi a tsaye kamar wani soja a gurin da ta huce shi kuma idanuwansa yana kanta, abin har ya so ya ba ta dariya amman ta shanye tare da cewa "menene ka ke yi a tsaye ko dai soja ka dawo ne ban sani ba?" Zuwa yayi ya zauna kusa da ita "ba dole na zama sojan k'arfi da yaji ba Love d'ita tana fushi da ni, kuma na rasa yadda zan yi nasa ta fahimci cewa ina sonta, amman ita ta fifita kallon film fiye da mijinta" Murmushi tayi sannan ta ce "hmmm Jabir kenan yaudararka wacece ban sani ba kai kan ka kasani na sanka sosai fiye da yadda baka tunani, na san wannan nacin da kake min akwai buk'atar da kake so ka cimma a kai na, dan haka wallahi ni ba zan tab'a yarda da kai ba".
Wata iriyar muguwar ajiyar zuciya ya sauke tabbas shi kansa yasan Teemarh ta san halinsa sosai, kuma yasan dole sai ya samu wannan k'alubalan wajen shawo kanta amman kuma dole sai ya tabbatar ya sa ta yarda da cewa yana sonta dan ya samu buk'atarsa a gurin Teemarh "Teemarh, nasan cewa ba za ki tab'a yarda da ni ba saboda irin abubuwan da nayi miki amman dan Allah ina so ki ba ni dama dan na tabbatar miki da cewa ina sonki","ko kuma kana son jikina ko?" Teemarh ta fad'a tana kallonsa ido cikin ido, Jabir ya rasa me zai ce mata kawai sai ya tashi ya fita wai shi a dole ya nuna mata yayi fushi, ita kuma Teemarh tab'e baki tayi sannan ta kwanta a kan kujera tana chatting, a haka har bacci ya kwasheta.
*'BANGAREN BAFFAN SALIS🚴🏽♀️💕*
Washe gari kamar yadda yayi wa Mama alk'awari da misalin k'arfe 2:00pm na yamma bayan yayi sallar azahar ya nufi gidan Alhaji Mansur, yana isa mai gadi yayi masa iso Alhaji Mansur ya cewa mai gadin ya kai shi falon bak'i gashi nan zuwa, haka ya fita ya shiga da Baffa falon bak'i, ba'a fi minti d'aya ba sai ga Alhaji Mansur ya shigo falon bakinsa d'auke da sallama "Assalamu alaikum" Da sauri Baffa ya tashi tsaye tare da amsa masa sallama "Wa'aikumussalam ranka ya dad'e" D'aure fuska Alhaji Mansur yayi tare da cewa "Amman ka ba ni mamaki sosai, ta ya za'ai ka na zaune ina shigowa ka tashi tsaye, raina yayi matuk'ar b'aci sosai" Baffa cikin girmamawa ya ce "Allah ya huci zuciyarka insha Allahu zan kiyaye gaba" Murmushi Alhaji Mansur yayi sannan ya ce "Allah ya sa, zaka iya zama" Ya fad'a yana nuna masa kujera".
Zama yayi sannan suka gaisa Baffa ya fara fad'a masa abin da ya kawo shi "da farko dai Alhaji ina mai ba ku hak'uri a kan irin abin da Mahaifiyar Salis tayi muku na sa ni bata kyauta ba kuma na ji matuk'ar kunyarka saboda na san anyi muku ba dai-dai ba, amman ina mai neman alfarmar da Nihal ta dawo d'akinta" Alhaji Mansur ya gyara zamansa sannan ya ce "Haba dan Allah sirikina saboda haka ne daman ka zo har nan, ai na ga Salis ba sakinta yayi ba dan haka insha Allahu gobe zan dawo da ita har asibitin kuma dan Allah kayi wa Salis d'in ya jiki kafin na zo" Baffa yayi wa Abba godiya sosai sannan ya tashi ya tafi shima Abba ya koma d'akin Hajiya Asiya dan yau anan yake.
*'BANGAREN ALIYU💃🏽💕*
Dawowarsa kenan daga gidan Musaddik sai ga Nihal da Shahida sun shigo d'akin sun zauna kusa dashi, kallonsu yayi tare da sakar musu murmushi ya ce " 'yan biyu meya faru?" Nihal ta ce "Yaya Haidar gurinka muka zo" Kallonsu yayi sannan ya ce "To gani nan 'yan k'annai na" Shahida ta ce "Yaya Aliyu Haidar wa ka ke so?" Kallonta yayi kamar ba zai yi magana ba sai kuma ya ce "Khadijatullahi" Waro ido Nihal tayi tare da fashewa da kukan tausayin d'an uwana ta tabbas daman ta so ta fahimci haka saboda irin yadda yake yi mata, amman ta ya ya Khadijatullahi zata karb'i soyayyarsa bayan ta tsani kowane namiji kuma tana ganin irin yadda Khadijatullahi take nuna tsantsar k'iyayyarta a kan Yayan na su.
"Haba darling sister idan kina kukan nan sai zuciyata ta k'arye ai" Aliyu yayi maganar zuciyarsa nayi masa zafi, Shahida ta ce "Yaya Aliyu Haidar ai dole tayi kuka, kai ma kasan dai Khadijatullahi irin yadda ta tsaneka sosai ta ya za'a ta so ka, Yaya Aliyu Haidar wallahi ni............" Sai kuma ita ma ta saka kuka, hankalinsa yayi matuk'ar tashi shima yasan ya d'aukowa kan sa babban aiki amman kuma ba laifinsa ba ne laifin zuciyarsa ne, rarrashinsu ya shiga yi sannan ya samu su ka yi shiru, nan da suka d'aukar masa alk'awarin zasu taimaka masa har sai Khadijatullahi ta so shi, suka shiga kwantar masa da hankali ganin irin yadda ya damu sosai, Aliyu cikin raunanniyar muryarsa ya ce "Nagode muku sosai darling sisters, na san kun damu da ni kuma na san na d'aukowa kai na babban aiki, shiyasa na ce muku ku ta ya ni da addu'a","Insha Allah zamu ta ya ka kuma zamu taimaka maka wajen ganin Khadijatullahi ta so ka" Nan dai suka yi masa alk'awari kala-kala a kan Khadijatullahi sai sun san yadda su ka yi ta so shi.
*'BANGAREN ASIYA👹*
Yau ya kasance za'a fad'i wanda zai kawo musu wanda za'a sha jininshi bayan sun gama tsaface-tsafacensu Wannan saurayin da har yau ban san sunansa ba ya mik'e ya gama zagaye su sannan ya zo gaban Hajiya Asiya ya tsaya tare da mik'a mata wata laya ta karb'a sannan ya ce "me za ki kawo mana kishiyarki da kuma mijinki dan muna buk'atar shan jininsu" Hajiya Asiya tayi tare da cewa.
"Alhaji kuma? Gaskiya ba zan iya ba da mijina ba" Ta yi maganar tana kallonshi ido cikin ido, ransa yayi matuk'ar b'aci cikin muryar da ta ke bayyanar da tsantsar b'acin rai ta ce "To idan kuwa ba za ki kawo shi mu sha jininsa ba to ki tabbatar da cewa lokacin mutuwarki yayiii dan kuwa za mu sha jininki, gobe da daddare mu ke buk'atar ki kawo su idan kuwa ba ki kawo su gaba d'aya ba to tabbas zan kasheki ne" Ya k'arasa maganar yana dora mata wata iriyar zagegiyar wuk'a a wuyanta, gabanta ne ya shiga fad'uwa, haka dai suka gama kowa ya fito dan tafiya gidansa, Hajiya Suhaima ce ta biyo bayan Hajiya Asiya wacce har ta bud'e motarta zata shiga kiran sunanta tayi da k'arfi "Asiya" Juyawa Hajiya Asiya tayi ranta a b'ace a halin yanzu wata iryar muguwar tsanar Hajiya Suhaima ta ke ji, domin kuwa ita ta ja mata ta kawota nan gidan, ita tayi tunanin ai gurin wani boka za su je ya gama musu da Aunty Murja.
"Menene?" Ta yi maganar tana wurga mata wani irin kallo, wata iriyar dariya Hajiya Suhaima ta fashe da ita tana cewa "Ke daman kina tunanin cewa zaki sha jinin iyayen wasu, mazajen wasu, da kuma 'yaya da k'annan wasu ki ce wai ke ba za'a sha na mijinki ba, to wallahi ba ki isa ba, dole sai mun sha jinin mijinki, kuma ni ba haka na so ba, na so ace jinin wannan tambad'adden d'an naki a ka ce, amman mu je zuwa na san wata rana dole sai mun sha jinin d'an tsinanniya" Wani irin mahaukacin mari Hajiya Asiya ta zabgawa Suhaima hagu da dama sai da ta jera mata kusan sau biyar, sannan ta ce "To wawiya dabba ki sa ni burinki ba zai tab'a cika ba, dan kuwa ko Abban Jabir ba za ku sha jininsa ba ballantana yarona Jabir, ke ce tsohuwar mahaukaciya da har zaki iya ba da mahaifiyarki tabbas asara da tab'ewa su tabbata a gareki shashasha jaka mara tunani" Tana gama fad'ar haka ta shige motarta ta ja da k'arfi ta nufi gidanta.
Wannan saurayin ya saki murmushi ya ce "Asiya kenan kina wasa da Jafar uban matsafa amman Allah ya kaimu gobe za ki ga aiki da cikawa, kar Allah ya sa ki kawo su ki ga abin da zai faru da ke" Yana gama fad'ar haka shi ma ya tafi gidansa, Hajiya Suhaima kuwa nan ta kuduri niyyar sai ta lalata Ahalin Asiya gaba d'aya, ta jima tana sake-sake sannan ta nufi motarta ta ja ta bar gurin, zuciyarta fal bak'in ciki.
*'BANGAREN AMATULLAHI👰🏼♀*
Sai da aka gama episode d'in ta juya dan ta ga inda Jabir d'in yayi dan ta ga yau bai takura mata ba, dan tayi tunanin ma ko ya fita daga d'akin ne, mamaki ya kamata ganinshi a tsaye kamar wani soja a gurin da ta huce shi kuma idanuwansa yana kanta, abin har ya so ya ba ta dariya amman ta shanye tare da cewa "menene ka ke yi a tsaye ko dai soja ka dawo ne ban sani ba?" Zuwa yayi ya zauna kusa da ita "ba dole na zama sojan k'arfi da yaji ba Love d'ita tana fushi da ni, kuma na rasa yadda zan yi nasa ta fahimci cewa ina sonta, amman ita ta fifita kallon film fiye da mijinta" Murmushi tayi sannan ta ce "hmmm Jabir kenan yaudararka wacece ban sani ba kai kan ka kasani na sanka sosai fiye da yadda baka tunani, na san wannan nacin da kake min akwai buk'atar da kake so ka cimma a kai na, dan haka wallahi ni ba zan tab'a yarda da kai ba".
Wata iriyar muguwar ajiyar zuciya ya sauke tabbas shi kansa yasan Teemarh ta san halinsa sosai, kuma yasan dole sai ya samu wannan k'alubalan wajen shawo kanta amman kuma dole sai ya tabbatar ya sa ta yarda da cewa yana sonta dan ya samu buk'atarsa a gurin Teemarh "Teemarh, nasan cewa ba za ki tab'a yarda da ni ba saboda irin abubuwan da nayi miki amman dan Allah ina so ki ba ni dama dan na tabbatar miki da cewa ina sonki","ko kuma kana son jikina ko?" Teemarh ta fad'a tana kallonsa ido cikin ido, Jabir ya rasa me zai ce mata kawai sai ya tashi ya fita wai shi a dole ya nuna mata yayi fushi, ita kuma Teemarh tab'e baki tayi sannan ta kwanta a kan kujera tana chatting, a haka har bacci ya kwasheta.
*'BANGAREN BAFFAN SALIS🚴🏽♀️💕*
Washe gari kamar yadda yayi wa Mama alk'awari da misalin k'arfe 2:00pm na yamma bayan yayi sallar azahar ya nufi gidan Alhaji Mansur, yana isa mai gadi yayi masa iso Alhaji Mansur ya cewa mai gadin ya kai shi falon bak'i gashi nan zuwa, haka ya fita ya shiga da Baffa falon bak'i, ba'a fi minti d'aya ba sai ga Alhaji Mansur ya shigo falon bakinsa d'auke da sallama "Assalamu alaikum" Da sauri Baffa ya tashi tsaye tare da amsa masa sallama "Wa'aikumussalam ranka ya dad'e" D'aure fuska Alhaji Mansur yayi tare da cewa "Amman ka ba ni mamaki sosai, ta ya za'ai ka na zaune ina shigowa ka tashi tsaye, raina yayi matuk'ar b'aci sosai" Baffa cikin girmamawa ya ce "Allah ya huci zuciyarka insha Allahu zan kiyaye gaba" Murmushi Alhaji Mansur yayi sannan ya ce "Allah ya sa, zaka iya zama" Ya fad'a yana nuna masa kujera".
Zama yayi sannan suka gaisa Baffa ya fara fad'a masa abin da ya kawo shi "da farko dai Alhaji ina mai ba ku hak'uri a kan irin abin da Mahaifiyar Salis tayi muku na sa ni bata kyauta ba kuma na ji matuk'ar kunyarka saboda na san anyi muku ba dai-dai ba, amman ina mai neman alfarmar da Nihal ta dawo d'akinta" Alhaji Mansur ya gyara zamansa sannan ya ce "Haba dan Allah sirikina saboda haka ne daman ka zo har nan, ai na ga Salis ba sakinta yayi ba dan haka insha Allahu gobe zan dawo da ita har asibitin kuma dan Allah kayi wa Salis d'in ya jiki kafin na zo" Baffa yayi wa Abba godiya sosai sannan ya tashi ya tafi shima Abba ya koma d'akin Hajiya Asiya dan yau anan yake.
*'BANGAREN ALIYU💃🏽💕*
Dawowarsa kenan daga gidan Musaddik sai ga Nihal da Shahida sun shigo d'akin sun zauna kusa dashi, kallonsu yayi tare da sakar musu murmushi ya ce " 'yan biyu meya faru?" Nihal ta ce "Yaya Haidar gurinka muka zo" Kallonsu yayi sannan ya ce "To gani nan 'yan k'annai na" Shahida ta ce "Yaya Aliyu Haidar wa ka ke so?" Kallonta yayi kamar ba zai yi magana ba sai kuma ya ce "Khadijatullahi" Waro ido Nihal tayi tare da fashewa da kukan tausayin d'an uwana ta tabbas daman ta so ta fahimci haka saboda irin yadda yake yi mata, amman ta ya ya Khadijatullahi zata karb'i soyayyarsa bayan ta tsani kowane namiji kuma tana ganin irin yadda Khadijatullahi take nuna tsantsar k'iyayyarta a kan Yayan na su.
"Haba darling sister idan kina kukan nan sai zuciyata ta k'arye ai" Aliyu yayi maganar zuciyarsa nayi masa zafi, Shahida ta ce "Yaya Aliyu Haidar ai dole tayi kuka, kai ma kasan dai Khadijatullahi irin yadda ta tsaneka sosai ta ya za'a ta so ka, Yaya Aliyu Haidar wallahi ni............" Sai kuma ita ma ta saka kuka, hankalinsa yayi matuk'ar tashi shima yasan ya d'aukowa kan sa babban aiki amman kuma ba laifinsa ba ne laifin zuciyarsa ne, rarrashinsu ya shiga yi sannan ya samu su ka yi shiru, nan da suka d'aukar masa alk'awarin zasu taimaka masa har sai Khadijatullahi ta so shi, suka shiga kwantar masa da hankali ganin irin yadda ya damu sosai, Aliyu cikin raunanniyar muryarsa ya ce "Nagode muku sosai darling sisters, na san kun damu da ni kuma na san na d'aukowa kai na babban aiki, shiyasa na ce muku ku ta ya ni da addu'a","Insha Allah zamu ta ya ka kuma zamu taimaka maka wajen ganin Khadijatullahi ta so ka" Nan dai suka yi masa alk'awari kala-kala a kan Khadijatullahi sai sun san yadda su ka yi ta so shi.
*'BANGAREN ASIYA👹*
Yau ya kasance za'a fad'i wanda zai kawo musu wanda za'a sha jininshi bayan sun gama tsaface-tsafacensu Wannan saurayin da har yau ban san sunansa ba ya mik'e ya gama zagaye su sannan ya zo gaban Hajiya Asiya ya tsaya tare da mik'a mata wata laya ta karb'a sannan ya ce "me za ki kawo mana kishiyarki da kuma mijinki dan muna buk'atar shan jininsu" Hajiya Asiya tayi tare da cewa.
"Alhaji kuma? Gaskiya ba zan iya ba da mijina ba" Ta yi maganar tana kallonshi ido cikin ido, ransa yayi matuk'ar b'aci cikin muryar da ta ke bayyanar da tsantsar b'acin rai ta ce "To idan kuwa ba za ki kawo shi mu sha jininsa ba to ki tabbatar da cewa lokacin mutuwarki yayiii dan kuwa za mu sha jininki, gobe da daddare mu ke buk'atar ki kawo su idan kuwa ba ki kawo su gaba d'aya ba to tabbas zan kasheki ne" Ya k'arasa maganar yana dora mata wata iriyar zagegiyar wuk'a a wuyanta, gabanta ne ya shiga fad'uwa, haka dai suka gama kowa ya fito dan tafiya gidansa, Hajiya Suhaima ce ta biyo bayan Hajiya Asiya wacce har ta bud'e motarta zata shiga kiran sunanta tayi da k'arfi "Asiya" Juyawa Hajiya Asiya tayi ranta a b'ace a halin yanzu wata iryar muguwar tsanar Hajiya Suhaima ta ke ji, domin kuwa ita ta ja mata ta kawota nan gidan, ita tayi tunanin ai gurin wani boka za su je ya gama musu da Aunty Murja.
"Menene?" Ta yi maganar tana wurga mata wani irin kallo, wata iriyar dariya Hajiya Suhaima ta fashe da ita tana cewa "Ke daman kina tunanin cewa zaki sha jinin iyayen wasu, mazajen wasu, da kuma 'yaya da k'annan wasu ki ce wai ke ba za'a sha na mijinki ba, to wallahi ba ki isa ba, dole sai mun sha jinin mijinki, kuma ni ba haka na so ba, na so ace jinin wannan tambad'adden d'an naki a ka ce, amman mu je zuwa na san wata rana dole sai mun sha jinin d'an tsinanniya" Wani irin mahaukacin mari Hajiya Asiya ta zabgawa Suhaima hagu da dama sai da ta jera mata kusan sau biyar, sannan ta ce "To wawiya dabba ki sa ni burinki ba zai tab'a cika ba, dan kuwa ko Abban Jabir ba za ku sha jininsa ba ballantana yarona Jabir, ke ce tsohuwar mahaukaciya da har zaki iya ba da mahaifiyarki tabbas asara da tab'ewa su tabbata a gareki shashasha jaka mara tunani" Tana gama fad'ar haka ta shige motarta ta ja da k'arfi ta nufi gidanta.
Wannan saurayin ya saki murmushi ya ce "Asiya kenan kina wasa da Jafar uban matsafa amman Allah ya kaimu gobe za ki ga aiki da cikawa, kar Allah ya sa ki kawo su ki ga abin da zai faru da ke" Yana gama fad'ar haka shi ma ya tafi gidansa, Hajiya Suhaima kuwa nan ta kuduri niyyar sai ta lalata Ahalin Asiya gaba d'aya, ta jima tana sake-sake sannan ta nufi motarta ta ja ta bar gurin, zuciyarta fal bak'in ciki.
*'BANGAREN AMATULLAHI👰🏼♀*