Sashe 54
Daren Aurena Part 1 Complete Hausa Novel · about 5 min read
Wajen awanni biyu Jabir da Aliyu suna jiran su ga nurse ta fita ta shaida musu matarsu ta haihu amman shuru, chan sai ga nurses guda biyu d'aya ta fito daga cikin d'akin da aka shiga da Amatullahi d'aya kuma daga cikin d'akin da aka shiga da Khadijatullahi kowannansu fuskarta d'auke da murmushi "Congrats matarka ta haihu ta samu d'a namiji" Nurse d'in farko take fad'awa Aliyu d'ayar kuma ta ce Khadijatullahi ta haifi 'ya mace haka suka shiga d'akin suna farin ciki aka sallamesu suka dawo gida, nan 'yan barka suka cika gidan har aka rasa in ma za'aje gidan Amatullahi ko Khadijatullahi, ranar suna kuwa gidan Hajiya Mama suka ta ho gaba d'ayansu aka yi sunan a chan yarinyar Khadijatullahi ta ci sunan Mami (Asiya) Inda suke ce mata Mummy, d'an Amatullahi kuwa aka saka masa sunan Alhaji Mansur suke ce masa Pappy, inda a ranar sunan da daddare Nihal da Shahida suka haihu farin ciki gurin ahalin nan ba'a magana ji suke kamar su zuba ruwa a k'asa su sha, haka su ma ranar suna aka sha suna a gidan Hajiya Mama, Teemarh tana kwance kusa da Hajiya Mama duk ta rasa meke yi mata dad'i yau ta tashi da tsanancin ciwon kai ga kuma amai da ta ke yi komai ta ci sai ta amayoshi, gaba d'aya ta fita a hayyacinta Hajiya Mama ta ce mata ta tashi su je asibiti ta ce A'a ba sai sun je ba ta ji sauk'i, haka ta barta babu yadda ta iya da ita, Jabir ne ya yi sallama ya shigo falon Aliyu yana biye dashi a baya "Yawwah d'an nan zo ga matarka nan sai fama take da amai da ciwon kai amman ta k'i yarda akai ta asibiti" Jabir ya k'arasa gurin da Teemarh ta e kwance ya ce "Zahra tashi muje asibiti kin ta b'a ganin mutun bashi da lafiya ya zauna a gida","Ni fa na warke fa, kan ya daina min ciwo" Aliyu cie da tsokana ya ce "A'a fa Aunty Fatima kodai d'a muka samu ne" Teemarh ta kalleshi kawai bata ce masa komai ba, dan kuwa ita ta ma fitar da rai da samun haihuwa "Kin ga ni ki tashi ko kin warke ko baki warke ba mu je asibiti, idan kuma kika dage a kan ba za ki je ba hmmm!" Ya yi maganar yana d'aure fuska, haka Teemarh ta mik'e dak'yar ta yafa mayafi ta fita daga falon kamar wacce aka bugawa iska😅.
Jabir ya bi bayanta suka shiga mota suna zuwa asibitin gwajin farko aka tabbatar musi da cewa Teemarh ciki gareta murna gurin Teemarh ba'a magana, ita ma ta samu ciki shikenan ita ma tana zata samu baby kamar dai su Shahida, haka suka dawo gida Khadijatullahi take tambayar Jabir meke damun Teemarh anan yake fad'a mata ciki ne da ita shine yake wujijjigata.
*BAYAN WATA BIYAR😤*
Cikin Teemarh ya girma sosai haihuwa ko yau ko gobe haka dai kullum tana jikin Jabir ta narke tana ta zuba masa shagwab'a iri-iri shi kuma yana biye mata anan yake tuna mata yadda ta shiga damuwa kafin ta samu ciki ta dinga yin dariya ta ce "Wallahi darling ba ka san yadda nake son na ga nima ina da baby ba ne shiyasa ka ke tsokanata" Jabir ya ce "Na sani mana tunda kin ta yar min da hankali lokacin, dan da ana siyan haihuwa da zan je na siyo miki ita na kawo miki dan hankalinki ya kwanta","Allah sarki darling ai yanzu komai ya huce" Cikinta ta ji yana murd'a mata mararta kuma ta d'aure da sauri ta rik'e Jabir tana cewa "Darling cikina" Da sauri ya mik'e ya samu ya taimaka mata suka shiga fita daga d'akin a mota ya sakata ya ja suka nufi asibiti, suna zuwa aka shiga da Teemarh labour room inda ko mintina hamsin ba ta yi ba ta haihu 'Yarta mace haka aka sallamesu suka dawo gida zuciyoyinsu cike da farin ciki, ranar suna anan gidan akayi suna anyi bidiri babu laifi an ci an sha, aka sakawa yarinya sunan Halima.
Lado da Zaituna su ma sunyi aure inda yanzu suna da d'a mai suna Ahmad, Hafsa ma ta haihu ita ma d'a namiji sunansa Sabir, inda Inna Larai ta auri wani mai wanki da guga a layinsu, Malam Shu'aibu ma ya yi aure a chan gurin aikin na su ya had'u da wata mai kawo musu abinci inda ya yaba da hankalinta yasa ya aureta, Haka rayuwar bayin Allah suka cigaba da gudana cikin farin ciki da kwanciyar hankali, kowannan burinsa ya ga ya kyautatawa d'an uwansa, Inda 'yan uwan Mahaifinsu Khadijatullahi wad'anda suka gudu suka dawo garesu tare da neman yafiyarsu, suka koma gidan su Khadijatullahi da suka tashi daman babu abin da gidan ya yi.
Zaune suke a falo suna hira Jabir ya kalli matan na sa da yaransa ya ce "A duk lokacin da na kalleku ina jin wani farin ciki a cikin zuciyata kuma ina godewa Allah, Alhamdulillahi ala kulli halin" Teemarh ta ce "Gaskiya kam darling dole ka godewa Allah" Khadijatullahi ta ce "Allah mun gode maka Alhamdulillahi😌"
Nima anan zance Alhamdullahi rabbil'alamin, anan na kawo k'arshen wannan littafin mai suna daren aurena Allah ubangiji ya sa mu amfana da abin da na fad'akar, kuskuren da nayi Allah ubangiji ya yafe min🥲😣👏🏽
Nasan a cikin ku zaku ce, to ya akayi Jabir ya auri Khadijatullah bayan saki uku yayi Mata? Amman karku manta fa a addinance idan mutum ya saki matarsa saki uku a lokaci d'aya to wannan sakin guda d'aya ne.
*'Yar mutan zazzau ce💃🏽💃🏽*
Jabir ya bi bayanta suka shiga mota suna zuwa asibitin gwajin farko aka tabbatar musi da cewa Teemarh ciki gareta murna gurin Teemarh ba'a magana, ita ma ta samu ciki shikenan ita ma tana zata samu baby kamar dai su Shahida, haka suka dawo gida Khadijatullahi take tambayar Jabir meke damun Teemarh anan yake fad'a mata ciki ne da ita shine yake wujijjigata.
*BAYAN WATA BIYAR😤*
Cikin Teemarh ya girma sosai haihuwa ko yau ko gobe haka dai kullum tana jikin Jabir ta narke tana ta zuba masa shagwab'a iri-iri shi kuma yana biye mata anan yake tuna mata yadda ta shiga damuwa kafin ta samu ciki ta dinga yin dariya ta ce "Wallahi darling ba ka san yadda nake son na ga nima ina da baby ba ne shiyasa ka ke tsokanata" Jabir ya ce "Na sani mana tunda kin ta yar min da hankali lokacin, dan da ana siyan haihuwa da zan je na siyo miki ita na kawo miki dan hankalinki ya kwanta","Allah sarki darling ai yanzu komai ya huce" Cikinta ta ji yana murd'a mata mararta kuma ta d'aure da sauri ta rik'e Jabir tana cewa "Darling cikina" Da sauri ya mik'e ya samu ya taimaka mata suka shiga fita daga d'akin a mota ya sakata ya ja suka nufi asibiti, suna zuwa aka shiga da Teemarh labour room inda ko mintina hamsin ba ta yi ba ta haihu 'Yarta mace haka aka sallamesu suka dawo gida zuciyoyinsu cike da farin ciki, ranar suna anan gidan akayi suna anyi bidiri babu laifi an ci an sha, aka sakawa yarinya sunan Halima.
Lado da Zaituna su ma sunyi aure inda yanzu suna da d'a mai suna Ahmad, Hafsa ma ta haihu ita ma d'a namiji sunansa Sabir, inda Inna Larai ta auri wani mai wanki da guga a layinsu, Malam Shu'aibu ma ya yi aure a chan gurin aikin na su ya had'u da wata mai kawo musu abinci inda ya yaba da hankalinta yasa ya aureta, Haka rayuwar bayin Allah suka cigaba da gudana cikin farin ciki da kwanciyar hankali, kowannan burinsa ya ga ya kyautatawa d'an uwansa, Inda 'yan uwan Mahaifinsu Khadijatullahi wad'anda suka gudu suka dawo garesu tare da neman yafiyarsu, suka koma gidan su Khadijatullahi da suka tashi daman babu abin da gidan ya yi.
Zaune suke a falo suna hira Jabir ya kalli matan na sa da yaransa ya ce "A duk lokacin da na kalleku ina jin wani farin ciki a cikin zuciyata kuma ina godewa Allah, Alhamdulillahi ala kulli halin" Teemarh ta ce "Gaskiya kam darling dole ka godewa Allah" Khadijatullahi ta ce "Allah mun gode maka Alhamdulillahi😌"
Nima anan zance Alhamdullahi rabbil'alamin, anan na kawo k'arshen wannan littafin mai suna daren aurena Allah ubangiji ya sa mu amfana da abin da na fad'akar, kuskuren da nayi Allah ubangiji ya yafe min🥲😣👏🏽
Nasan a cikin ku zaku ce, to ya akayi Jabir ya auri Khadijatullah bayan saki uku yayi Mata? Amman karku manta fa a addinance idan mutum ya saki matarsa saki uku a lokaci d'aya to wannan sakin guda d'aya ne.
*'Yar mutan zazzau ce💃🏽💃🏽*