Sashe 44
Daren Aurena Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Suna isa gidan Aliyu yayi parking sannan ya fito daga cikin motar cikin takunsa na isa da tak'ama ya zagayo ya bud'ewa Khadijatullahi motar ta fito su Shahida ma suka fito suka shige cikin gidan, Aliyu ya kalli Khadijatullahi ya ce "My heartbeat idan kin shiga gida kin huta ki zo falon bak'i ina son ganinki keda yarona","To Yaya Aliyu" Tayi maganar a sanyaye tare da nufar hanyar shiga gidan, shima ya bi bayanta zuciyarsa cike da farin ciki, ta huce zuwa falo, shi kuma Aliyu ya shige d'akinsa.
Wajen k'arfe 8:00pm na dare sai ga Khadijatullah ta nufi falon bak'i tana rumgume da Affan a k'irjinta, ta shiga falon bakinta d'auke da sallama "Assalamu alaikum" Ido biyu ta yi da Aliyu yana zaune yana kallon bbc hausa "Wa'alaikissalam Matata" Ya amsa mata sallamar ciki muryarsa me jan hankalin mutane da kuma rud'a 'yammata.
Khadijatullah ta shiga ta zauna a kan kujera tare da kwantar da Affan Wanda yake shan baccinsa hankalinsa kwance, Aliyu ya tashi daga gurin da yake ya koma kujerar da Khadijatullah take zaune, ya zauna da yake kujerar ta zaman mutum uku ce, Affan ya d'auka tare da sumbatarsa a kuncinsa, kallon Khadijatullah yayi ya ce "My wife to be, ya gajiya","ba gajiya" Ta ce a takaice.
"Khadijatullah wallahi ina sonki sosai, Dan Allah ki karb'i soyayyata, nayi miki Alk'awarin ba zan tab'a bari ki tozarta ba, Kuma ba zan yi miki irin abin da Yaya Jabir yayi miki ba, saboda ni da shi ba halinmu d'aya dashi ba, zaki iya gwada ni ta kowacce hanya domin ki tabbatar da abin da nake fad'a miki".
"Yaya Aliyu Ina tsoro kada.............." Sai ta fashe da kuka mai cin rai,hankalin Aliyu ya tashi "Final choice meyafaru?Dan Allah ki daina kukan nan haka" Shuru tayi tana sauke ajiyar zuciya ta ce "Yaya Aliyu kayi min Alk'awarin ba za ka tab'a cutar da ni ba, kuma idan munyi aure za ka rik'eni da amana" Murmushi yayi ya ce "Indai wannan ne matsalarki Matata kada ki damu, Kuma nayi miki Alk'awarin ba zan tab'a cutar da ke ba","To na amince da soyayyarka Yaya Aliyu".
"Da gaske babyna" Khadijatullah ta gyad'a masa kai alamar eh, anan fa Aliyu ya shiga zuba mata kalaman soyayya, sai wajen k'arfe 8:45pm sannan Aliyu ya rakata har bakin kofar falo ya mik'a mata Affan sannan su ka yi sallama ya koma d'akinsa ita kuma ta shige falon, kai tsaye bedroom ta nufa ta kwanta, bacci Mai nauyi yayi awon gaba da ita.
*'BANGAREN TEEMARH DA JABIR😂*
Zaune suke a kan kujera suna kallon *so k'addarar zuciya* Arewa 24 Jabir ya janyo Teemarh jikinsa tana shafata, Yana sumbatar kuncinta kallonsa Teemarh tayi tare da cewa "Dan Allah darling ka bari mu gama yin kallon nan, sai mu yi abin da ya dace","A'a darling yanzu nake so please ki tafi mu kwanta".
"Ya salam darling Dan Allah........." Toshe bakinta yayi sannan ya d'auketa cak ya kai ta kan gado, kayan jikinta ya shiga kok'arin cire Mata, Teemarh ta saka kuka tana cewa "Darling Wai meyasa ba ka son, farin cikina kawai Kai burinka ka samu abin da daga gareni" Jabir Wanda yake kok'arin zame Mata riga jin abin da Teemarh take fad'a yasa ya tashi daga kanta, kayansa ya mayar jikinsa ya fita daga d'akin a fusace, Teemarh ta saka kuka, ita ma ta mayar da kayanta ta bi bayansa da sauri, Amman Bata ga koda k'eyar Jabir ba, barantana shi, durk'ushewa tayi a k'asa tana kuka, ji tayi an d'agota da sauri ta juya tare da tashi tsaye tana ci gaba da yin kukan, Aunty Murja ta kalleta sosai sannan ta ce "Fatima meyafaru ki ke kuka?","Bakomai Mummy" Teemarh tayi maganar cikin shash-shekar kuka, "ba za ki iya fad'a min damuwarki ba Fatima" Kukan Teemarh ya tsananta ta ce "Darling ne" Tayi maganar tana goge hawayen fuskarta.
Aunty Murja ta ce "koma Mai yayi miki bai kamata ace kin zo kina yin kuka ba, ya kamata ki zauna ki nutsu ki kirasa, sai ku tattauna a kan matsalarku, ta haka ne za ku fuskanci juna" Teemarh tayi murmushi ta ce "Nagode Mummy zan yi amfani da shawararki insha Allahu" Daga nan kowannan su ya koma d'akinsa, Teemarh ta d'auki wayarta ta shiga kiran layin Jabir Amman a kashe wayar take Dan haka ta zauna ta cigaba da yin kallonta Amman zuciyarta tana gurin Jabir.
*'BANGAREN SAFNA😔👏🏽*
Safna ta fito da gudu daga d'akinta tana murmushi suka had'a ido da Safwan ta matso kusa dashi zata rumgumeshi, yayi saurin tureta yana cewa "karki matso kusa da ni" Yayi maganar fuskarsa a d'aure, Safna ta ce "Ruhina ka yi hak'uri na tuba ba zan k'ara ba, Amman Dan Allah karka hukunta ta wannan hanyar ka yi min duk abin da ya dace da ni ka ji Ruhina" Kallonta yayi kamar ba zai yi magana ba sai Kuma ya ce "Akwai sharad'ai guda uku da zan fad'a miki, idan har ki ka amince dasu to shikenan komai zai huce" Safna ta ce "wad'anne sharad'ai ne?" Zama Safwan yayi ita kuma ta tsaya tana son jin wane sharad'i ne wannan "sharad'i na farko shine karki sa ke yin kishi a kan Hafsa ina son ki d'auketa tamkar Zahra k'anwarki wacce ku ka fito ciki d'aya, Sharad'i na biyu kuma karki sa ke yi min zancen yaushe Khalid zai dawo saboda ni nasan gurin da na kai shi babu abin da za'ayi masa na kuntatawa Sharad'i na uku kuma karki sa ke yi min maganar Hafsa idan muna tare da ke, idan kin yarda da su za ki iya zuwa" Safwan yayi maganar tare da bud'e hannayensa alamar Safnan ta zo jikinsa.
Hawaye ne suka shiga gangaro mata a hankali ta fara tafiya kamar mai sand'a, ta fad'a jikinsa tare da rushewa da wani irin kuka, tana tsananin jin kewar yaronta amman kuma anyi mata katangar k'arfe dashi, tana ji tana gani ba ta da damar da za ta tambayi yaronta, sai ya zama laifi, "na amince da sharad'anka ruhina amman dan Allah ka kawo min yarona koda sau d'aya ne na ganshi, idan na ganshi ba zan sake cewa a kawo min shi ba nayi maka alk'awari" Tausayinta ya kamashi amman ya zama dole yayi haka, domin ya k'ara saka son Hafsa a cikin zuciyar Safna "to shikenan zan kawo miki shi gobe insha Allahu","to nagode" Safna ta fad'a cikin rawar murya, daga nan suka dora soyayyarsu daga inda suka tsaya.
*Team Khadijatullahi where you😂😂yau fa ta gwangwaje ku da kalamai masu dad'i*
*'BANGAREN HAJIYA ASIYA DA ALHAJI MUKHTAR🤔*
Sai da Hajiya Asiya ta kwana biyu sannan ta farfad'o wajen k'arfe 8:00am na safe Alhaji Mukhtar yana zaune kusa da ita ya zuba mata ido yana kallonta cike da so da k'aunarta, a hankali ta fara bud'e idanuwanta ta zuba su a saman d'akin abubuwan da suka faru suka shiga fad'o mata hawaye na zuba daga idanuwanta, yanzu shikenan ta san gurin wad'annan wahalallun iyayen nata zata koma ta ci gaba da shan wahala, Alhaji Mukhtar ya saki murmushi tare da kiran sunanta "Asiya" A hankali ta juya ta kalli mai kiran na ta ganin Alhaji Mukhtar yayi matuk'ar ba ta mamaki tare da jefo masa tambayoyi "Ina ne nan? Me na zo yi nan? Waya kawo ni? Ina yarana? Ina Abban Jabir" Murmushi yayi mai cin rai jin ta ambaci sunan mijinta amman ya danne ya fara ba ta amsoshinta "kina asibiti ne, na je gidan tsafi ne na tarar da ke kwance cikin jini shine ya d'aukoki na kawoki, kuma tun da na kawoki babu wanda ya zo gurinki amman gaskiya nayi mamaki sosai yaranki ko mijinki babu wanda ya nemeki kenan hakan na nufin basa buk'atarki a rayuwarsu, ko kuma basu damu da ke ba?".
Hawaye Hajiya Asiya tashi zubarwa tana cewa "A'a yarana suna sona sosai ba za su iya juya min baya ba kuma"............"To gashi sun juya miki kuwa tunda yau kusan kwananki goma babu wanda ya zo asibitin nan kuma har gidan na je amman su ka yi min rashin mutunci suka ce basa sonki a rayuwarsu" Alhaji Muhktar ya fad'a cikin yanayin damuwa dan kuwa ya fad'i haka ne kawai dan Hajiya Asiya ta ji haushi kar ta ce zata koma gidan mijin na ta, dan kuwa shi bai ma san ina ne gidan Hajiya Asiyan ba, kuma bai san waye mijin na ta ba.
"Yanzu haka su Jabir za su yi min ban yi tunanin haka daga garesu ba kuma nima insha Allahu zan fita a rayuwarsu kamar yadda nima suka fita a rayuwata" Hajiya Asiya tayi magana tare da goge hawayen fuskarta, Alhaji Mukhtar kuwa murmushi yayi ganin cikin k'ank'anin lokaci yayi nasarar raba tsakanin Hajiya Asiya da mijinta da kuma yaranta yanzu shikenan dole yasan shi za ta bi ya kai ta gidansa ya samu ya biya buk'atarsa da ita dan a iya zaman da su ka yi da ita ya fuskanci cewar Hajiya Asiya macece mai shegen son kud'in tsiya, dan haka ya san da zarar yana sakar mata kud'i to bashi da wata damuwa,haka dai yayi ta rarrashinta tare da cusa mata tsanar yaranta da kuma mijinta.
*'BANGAREN INNA LARAI DA LADO😂😣*
Tun ranar da Inna Larai ta dawo gida, yaronta da iyayenta suka d'auki karan tsana suka dora mata domin sun ji labarin irin abin da ta aikata domin a cewarsu kaf danginsu babu mazinaci, dan haka suka cireta daga cikinsu wani d'an k'aramin d'aki suka ba ta wanda ake kiwon kaji a cikinsa, kaji ne gaba d'aya a cikin d'akin dan su kansu kajin ma d'akin yayi musu kad'an, a haka amman Inna Larai take rab'awa take zama duk a takure, ga shi sunyi mata gargad'in kar su sake su ga k'afarta a waje idan har ba su suka bata izinin ta fito ba, ba'a ba ta aminci sai kowa ya ci ragowar da aka rage shi za'a gefa mata a jikinta ya zube kajin su yo kanta su yi ta caccakarta sun cin abincin, wata ran kuwa ba za su bata ba haka zata wuni da kwana ba ta ci abinci ba.
Wajen k'arfe 8:00pm na dare sai ga Khadijatullah ta nufi falon bak'i tana rumgume da Affan a k'irjinta, ta shiga falon bakinta d'auke da sallama "Assalamu alaikum" Ido biyu ta yi da Aliyu yana zaune yana kallon bbc hausa "Wa'alaikissalam Matata" Ya amsa mata sallamar ciki muryarsa me jan hankalin mutane da kuma rud'a 'yammata.
Khadijatullah ta shiga ta zauna a kan kujera tare da kwantar da Affan Wanda yake shan baccinsa hankalinsa kwance, Aliyu ya tashi daga gurin da yake ya koma kujerar da Khadijatullah take zaune, ya zauna da yake kujerar ta zaman mutum uku ce, Affan ya d'auka tare da sumbatarsa a kuncinsa, kallon Khadijatullah yayi ya ce "My wife to be, ya gajiya","ba gajiya" Ta ce a takaice.
"Khadijatullah wallahi ina sonki sosai, Dan Allah ki karb'i soyayyata, nayi miki Alk'awarin ba zan tab'a bari ki tozarta ba, Kuma ba zan yi miki irin abin da Yaya Jabir yayi miki ba, saboda ni da shi ba halinmu d'aya dashi ba, zaki iya gwada ni ta kowacce hanya domin ki tabbatar da abin da nake fad'a miki".
"Yaya Aliyu Ina tsoro kada.............." Sai ta fashe da kuka mai cin rai,hankalin Aliyu ya tashi "Final choice meyafaru?Dan Allah ki daina kukan nan haka" Shuru tayi tana sauke ajiyar zuciya ta ce "Yaya Aliyu kayi min Alk'awarin ba za ka tab'a cutar da ni ba, kuma idan munyi aure za ka rik'eni da amana" Murmushi yayi ya ce "Indai wannan ne matsalarki Matata kada ki damu, Kuma nayi miki Alk'awarin ba zan tab'a cutar da ke ba","To na amince da soyayyarka Yaya Aliyu".
"Da gaske babyna" Khadijatullah ta gyad'a masa kai alamar eh, anan fa Aliyu ya shiga zuba mata kalaman soyayya, sai wajen k'arfe 8:45pm sannan Aliyu ya rakata har bakin kofar falo ya mik'a mata Affan sannan su ka yi sallama ya koma d'akinsa ita kuma ta shige falon, kai tsaye bedroom ta nufa ta kwanta, bacci Mai nauyi yayi awon gaba da ita.
*'BANGAREN TEEMARH DA JABIR😂*
Zaune suke a kan kujera suna kallon *so k'addarar zuciya* Arewa 24 Jabir ya janyo Teemarh jikinsa tana shafata, Yana sumbatar kuncinta kallonsa Teemarh tayi tare da cewa "Dan Allah darling ka bari mu gama yin kallon nan, sai mu yi abin da ya dace","A'a darling yanzu nake so please ki tafi mu kwanta".
"Ya salam darling Dan Allah........." Toshe bakinta yayi sannan ya d'auketa cak ya kai ta kan gado, kayan jikinta ya shiga kok'arin cire Mata, Teemarh ta saka kuka tana cewa "Darling Wai meyasa ba ka son, farin cikina kawai Kai burinka ka samu abin da daga gareni" Jabir Wanda yake kok'arin zame Mata riga jin abin da Teemarh take fad'a yasa ya tashi daga kanta, kayansa ya mayar jikinsa ya fita daga d'akin a fusace, Teemarh ta saka kuka, ita ma ta mayar da kayanta ta bi bayansa da sauri, Amman Bata ga koda k'eyar Jabir ba, barantana shi, durk'ushewa tayi a k'asa tana kuka, ji tayi an d'agota da sauri ta juya tare da tashi tsaye tana ci gaba da yin kukan, Aunty Murja ta kalleta sosai sannan ta ce "Fatima meyafaru ki ke kuka?","Bakomai Mummy" Teemarh tayi maganar cikin shash-shekar kuka, "ba za ki iya fad'a min damuwarki ba Fatima" Kukan Teemarh ya tsananta ta ce "Darling ne" Tayi maganar tana goge hawayen fuskarta.
Aunty Murja ta ce "koma Mai yayi miki bai kamata ace kin zo kina yin kuka ba, ya kamata ki zauna ki nutsu ki kirasa, sai ku tattauna a kan matsalarku, ta haka ne za ku fuskanci juna" Teemarh tayi murmushi ta ce "Nagode Mummy zan yi amfani da shawararki insha Allahu" Daga nan kowannan su ya koma d'akinsa, Teemarh ta d'auki wayarta ta shiga kiran layin Jabir Amman a kashe wayar take Dan haka ta zauna ta cigaba da yin kallonta Amman zuciyarta tana gurin Jabir.
*'BANGAREN SAFNA😔👏🏽*
Safna ta fito da gudu daga d'akinta tana murmushi suka had'a ido da Safwan ta matso kusa dashi zata rumgumeshi, yayi saurin tureta yana cewa "karki matso kusa da ni" Yayi maganar fuskarsa a d'aure, Safna ta ce "Ruhina ka yi hak'uri na tuba ba zan k'ara ba, Amman Dan Allah karka hukunta ta wannan hanyar ka yi min duk abin da ya dace da ni ka ji Ruhina" Kallonta yayi kamar ba zai yi magana ba sai Kuma ya ce "Akwai sharad'ai guda uku da zan fad'a miki, idan har ki ka amince dasu to shikenan komai zai huce" Safna ta ce "wad'anne sharad'ai ne?" Zama Safwan yayi ita kuma ta tsaya tana son jin wane sharad'i ne wannan "sharad'i na farko shine karki sa ke yin kishi a kan Hafsa ina son ki d'auketa tamkar Zahra k'anwarki wacce ku ka fito ciki d'aya, Sharad'i na biyu kuma karki sa ke yi min zancen yaushe Khalid zai dawo saboda ni nasan gurin da na kai shi babu abin da za'ayi masa na kuntatawa Sharad'i na uku kuma karki sa ke yi min maganar Hafsa idan muna tare da ke, idan kin yarda da su za ki iya zuwa" Safwan yayi maganar tare da bud'e hannayensa alamar Safnan ta zo jikinsa.
Hawaye ne suka shiga gangaro mata a hankali ta fara tafiya kamar mai sand'a, ta fad'a jikinsa tare da rushewa da wani irin kuka, tana tsananin jin kewar yaronta amman kuma anyi mata katangar k'arfe dashi, tana ji tana gani ba ta da damar da za ta tambayi yaronta, sai ya zama laifi, "na amince da sharad'anka ruhina amman dan Allah ka kawo min yarona koda sau d'aya ne na ganshi, idan na ganshi ba zan sake cewa a kawo min shi ba nayi maka alk'awari" Tausayinta ya kamashi amman ya zama dole yayi haka, domin ya k'ara saka son Hafsa a cikin zuciyar Safna "to shikenan zan kawo miki shi gobe insha Allahu","to nagode" Safna ta fad'a cikin rawar murya, daga nan suka dora soyayyarsu daga inda suka tsaya.
*Team Khadijatullahi where you😂😂yau fa ta gwangwaje ku da kalamai masu dad'i*
*'BANGAREN HAJIYA ASIYA DA ALHAJI MUKHTAR🤔*
Sai da Hajiya Asiya ta kwana biyu sannan ta farfad'o wajen k'arfe 8:00am na safe Alhaji Mukhtar yana zaune kusa da ita ya zuba mata ido yana kallonta cike da so da k'aunarta, a hankali ta fara bud'e idanuwanta ta zuba su a saman d'akin abubuwan da suka faru suka shiga fad'o mata hawaye na zuba daga idanuwanta, yanzu shikenan ta san gurin wad'annan wahalallun iyayen nata zata koma ta ci gaba da shan wahala, Alhaji Mukhtar ya saki murmushi tare da kiran sunanta "Asiya" A hankali ta juya ta kalli mai kiran na ta ganin Alhaji Mukhtar yayi matuk'ar ba ta mamaki tare da jefo masa tambayoyi "Ina ne nan? Me na zo yi nan? Waya kawo ni? Ina yarana? Ina Abban Jabir" Murmushi yayi mai cin rai jin ta ambaci sunan mijinta amman ya danne ya fara ba ta amsoshinta "kina asibiti ne, na je gidan tsafi ne na tarar da ke kwance cikin jini shine ya d'aukoki na kawoki, kuma tun da na kawoki babu wanda ya zo gurinki amman gaskiya nayi mamaki sosai yaranki ko mijinki babu wanda ya nemeki kenan hakan na nufin basa buk'atarki a rayuwarsu, ko kuma basu damu da ke ba?".
Hawaye Hajiya Asiya tashi zubarwa tana cewa "A'a yarana suna sona sosai ba za su iya juya min baya ba kuma"............"To gashi sun juya miki kuwa tunda yau kusan kwananki goma babu wanda ya zo asibitin nan kuma har gidan na je amman su ka yi min rashin mutunci suka ce basa sonki a rayuwarsu" Alhaji Muhktar ya fad'a cikin yanayin damuwa dan kuwa ya fad'i haka ne kawai dan Hajiya Asiya ta ji haushi kar ta ce zata koma gidan mijin na ta, dan kuwa shi bai ma san ina ne gidan Hajiya Asiyan ba, kuma bai san waye mijin na ta ba.
"Yanzu haka su Jabir za su yi min ban yi tunanin haka daga garesu ba kuma nima insha Allahu zan fita a rayuwarsu kamar yadda nima suka fita a rayuwata" Hajiya Asiya tayi magana tare da goge hawayen fuskarta, Alhaji Mukhtar kuwa murmushi yayi ganin cikin k'ank'anin lokaci yayi nasarar raba tsakanin Hajiya Asiya da mijinta da kuma yaranta yanzu shikenan dole yasan shi za ta bi ya kai ta gidansa ya samu ya biya buk'atarsa da ita dan a iya zaman da su ka yi da ita ya fuskanci cewar Hajiya Asiya macece mai shegen son kud'in tsiya, dan haka ya san da zarar yana sakar mata kud'i to bashi da wata damuwa,haka dai yayi ta rarrashinta tare da cusa mata tsanar yaranta da kuma mijinta.
*'BANGAREN INNA LARAI DA LADO😂😣*
Tun ranar da Inna Larai ta dawo gida, yaronta da iyayenta suka d'auki karan tsana suka dora mata domin sun ji labarin irin abin da ta aikata domin a cewarsu kaf danginsu babu mazinaci, dan haka suka cireta daga cikinsu wani d'an k'aramin d'aki suka ba ta wanda ake kiwon kaji a cikinsa, kaji ne gaba d'aya a cikin d'akin dan su kansu kajin ma d'akin yayi musu kad'an, a haka amman Inna Larai take rab'awa take zama duk a takure, ga shi sunyi mata gargad'in kar su sake su ga k'afarta a waje idan har ba su suka bata izinin ta fito ba, ba'a ba ta aminci sai kowa ya ci ragowar da aka rage shi za'a gefa mata a jikinta ya zube kajin su yo kanta su yi ta caccakarta sun cin abincin, wata ran kuwa ba za su bata ba haka zata wuni da kwana ba ta ci abinci ba.