Sashe 15
Daren Aurena Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Inna Larai ce zaune ita da Lado sun gama had'awa Amatullahi mak'irci gurin mahaifinta Malam Shu'aibu a kan cewa tana fita yawo kuma idan ta tafi makaranta ba ta dawowa sai chan dare wajen k'arfe goma za'a zo ayi parking d'in mota a sauketa a kofar gida, hankalin Malam Shu'aibu ya tashi dan haka ya buga sammako da dawo gidansa, ko da ya dawo ya tambaya ina Amatullahi suka ce tana cikin d'akinta, ya nufi d'akin yana kwad'a mata kira da sauri ta fito cikin wata doguwar rigar abaya plum colour ta yafa mayafin abayar rik'e da jakarta ta zuwa makaranta tayi kyau sosai sai kamshi take yi murmushi tayi ta tsugunna har k'asa ta gaisar da Abbanta, abin da ya bawa su Innah Larai mamaki sai suka ga Malam Shu'aibu yayi murmushi ya amsa gaisuwar da tayi yayi mata umarni da ta tashi tsaye ta mik'e, anan ya shiga tambayarta "Mamana meyasa idan kin je makaranta bakya dawowa da wuri sai goma na dare kuma ajiye ki ake yi a mota, kuma kika watsa Larai mai a fuska ita da Lado" cikin mamaki ta ce "Abbana ni kuma wallahi Abba kullum da wuri nake dawowa kuma ni da Khadijatullahi muke dawowa a adaidaita, kasan dai ba na kula kowane saurayi kai ma shaidata ne bare har in shiga motarsa wallahi zan iya dafa al'kur'ani ban tab'a shiga motar kowa ba kuma ban tab'a kai wa goma na dare a waje ba kuma Innah Larai da Lado sune suka ja duk abin da nayi musu anan ta fad'a masa duk abin da ya faru" ta k'arasa maganar tana kuka, anan Malam Shu'aibu ya shiga rarrashin 'yar tasa har tayi shuru ya kama hannunta suka yi hanyar waje, Amatullahi idanuwanta a kan su Inna Larai da fuskokinsu suka chanza saboda basu yi nasarar had'a uba da 'yar ba tasan tabbas sune suka had'a mata mak'ircin nan kuma wallahi ba za ta kyalesu ba sai ta rama (ni kuwa 'yar mutanan zazzau na ce su inna larai an taro match🤣) haka suka fita daga gidan mahaifinta na rik'e da hannunta a kofar gida suka tsaya mahaifina ta ya kalleta cike da so da k'auna "Mamana kiyi hak'uri nasan kina hak'uri zama dasu Larai daman nasan ni ba halinki ba ne, amman nasan yadda zan shawo kan abin" hannu ya zura a aljihu ta d'auko 2k (dubu biyu) ya mik'a mata sannan ya cigaba da magana "gashi nan kiyi amfani dashi dan ba lallai ki dawo ki same ni ba, zan koma chan companyn namu yanzu ma jirana ake yi" Amatullahi ta karb'a tare da yi masa godiya, ta nufi gidansu Khadijatullahi zuciyarta fal farin ciki domin kuwa taji dad'i da Abbana ta ya ce zai koma wannan zai bata damar had'a musu nata mak'irci amman kuma ita ba k'arya zata musu ba, a kan abin da suke aikatawa a gidan zata yi musu basu san dawa suke zancen ba ne, da wannan tunanin ta k'arasa gidansu Khadijatullahi ta tarar ita ma har ta gama shiryawa doguwar rigar abayar tasa komai iri d'aya haka suka yi wa Aunty Murja sallama suka nufi hanyar fita daga gidan.
Suna fitowa suka yi sa'a ga wani mai adaidaita zai fita daga layin suka tsayar dashi suka shiga Amatullahi ta ce "Baba poly zaka kai mu ta gadon k'aya" kasancewar mai adaidaitar tsoho ne, shiyasa ta ce masa Baba, ya amsa mata da "to" suna isa Khadijatullahi ta bud'e jakarta ta d'auko naira d'ari biyar wacce ita kenan da ita zata mik'awa mai adaidatan Amatullahi ta dakatar da ita da cewa "to Hajiyata ai sai ki bari in biya ko?" ta fad'a tana mik'awa mai adaidatan naira d'ari biyar tunda daman a haka ake kawo su makarantar, suka shiga makarantar suna zuwa suka tarar da Hafsa har tazo abin da ya basu mamaki shine abayar da Hafsa ta saka komai iri d'aya da tasu babu abin da ya bambanta k'arasawa gurinta suka yi Amatullahi ta ce "Besty Hafseyy yau fa kinsa mun shiga mamaki sosai" murmushi tayi ta ce "Saboda kayan da nasa irin naku ko?" Khadijatullahi ta ce "Wallahi kuwa komai irin d'aya" Hafsa ta ce "ba abin mamaki ba ne ai, saboda tun jiya da muka je gidanku na ga abayar Khadijatullahi a kan gado kawai naji jikina ya bani ita zaku saka yau sai na k'are mata kallo Allah yasa naga kwalliyar jikin abayar duk da cewa ba duk na gani ba, shine muna tafiya na tsaya na saya a wani super market, murmushi suka yi gaba d'ayansu sannan suka nufi hanyar ajinsu domin an kusan fara lecture, basu dad'e da shiga ba Malam ya shigo suka fara lectures.
••••••••••••••••••••••••••••••••••••••••••••••••••••••••••••••••••••••••••
*'BANGAREN GIDANSU JABIR*
Jabir ne tsaye a gaban madubi yana kallon kansa ya gama shirinsa tsaf cikin wasu kaya gajeren wando ne wanda ko guiwarsa bai kai ba sai wata farar riga wanda a bayanta an rubuta *JABIR D'AN TUWA* da manyan harafai gashin kansa ya kwanta luf sai shek'i yake yi, haka ya fito babban falo, babu kowa a falon dan haka ya nufi kofar fita daga falon, Jabir yana bud'e kofar falon Aliyu na fitowa daga d'akinsa kallo d'aya yayi masa ya d'auke kansa domin kuwa wani irin haushin Jabir d'in yake ji, shi kuwa Jabir bai ga Aliyu ba saboda ya riga ya fita daga falon, motarsa ya nufa ya shiga ya jaa ta da gudu mai gadi yayi saurin bud'e masa gate ya fita daga gidan wak'ar babban mawak'in yahudawa ya saka Ojoro wanda Omale yayi ya k'ure kid'an yana bin wak'ar a hankali, Club ya nufa yana isa farfagiyar club d'in ya tarar da wasu 'yammata su biyu a tsaye, fita yayi daga cikin motar ya nufi inda wad'annan 'yanmatan suke kai masha Allahu kyawawa ne ajin farko, sanye suke da wasu d'ammun riga da wando sun yafa wani d'an k'aramin mayafi, k'are musu kallo yayi bai tab'a ganinsu a club d'in ba "Yau akwai chilling kenan, wad'annan daga ganinsu sababbin hannu ne" ya fad'a a zuciyarsa a fili kuma ya ce "Hi bebs" cikin wata iriyar muryarsa ta shu'uman 'yan bariki, murmushi suka sannan suka ce Jabir d'an tuwa, bai yi mamakin jin sun fad'i sunansa ba domin kuwa Jabir yayi k'aurin suna gurin iskanci da shaye-shaye, murmushi yayi sannan ya ce "Sannunku bebs ya kamata ku fad'a min sunayenku domin nima nasani" d'aya daga ciki ta ce "sunana zulaihat amman zaka iya kirana da Zuly baby, sai ta nuna d'ayar ta ce wannan kuma sunanta Ummita" Jabir yayi kayatatcen murmushi sannan ya kama hannayensu yayi cikin hotel d'akinsa ya nufa ya bud'e sannan suka shiga gaba d'ayansu suka bage hajarsu a kan gado Jabir yana kwance a kan gadon su kuma sun kwanta a jikinsa suna shafa shi tare da kissing d'in jikinsa (tofa jama'a Jabir bai saduda ba, Allah dai ya kyauta) haka sukai ta aikata bad'ala har sai wajen k'arfen biyar da rabi sannan Jabir ya tashi daga kan su Zuly yayi wanka ya dawo ya fara kok'arin shiryawa Zuly da Ummita suka matso kusa dashi suka shiga shiryashi Jabir kuwa wani irin farin ciki ne ya kamashi tabbas wad'annan 'yammatan sun iya soyayya sai da suka gama tsaf sannan ya tashi ya bashi rabar 'yan dubu dubu ya fita daga d'akin Zuly da Ummita murna fal ciki dan tunda suke harkar bariki babu wanda ya tab'a basu dubu ashirin ma barantana har a basu rabar 'yan dubu dubu, shi kuwa Jabir ko cikin club d'in bai shiga ba ya shiga mota ya nufi layinsu Khadijatullahi.
~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~
*Poly🔱🏨*
Wajen k'arfe shida dai-dai aka tashi daga makarantar, su Khadijatullahi suka fito daga aji Hafsa ta hango Yaya Safwan a jikin motarsa ya hard'e hannunsa a k'irjinsa yana ta baza idanuwana ya ga inda zai hango Hafsa gefensa wani kyakkyawan yaro ne wanda shekarunsa ba zai huce 6 ba,kamanninsa d'aya da yaron, Hafsa cike da mamaki had'i da bak'in ciki take nunawa su Amatullahi gurin da Yaya Safwan d'in yake ta ce "kun ga wanchan tsohon azzalumin yazo tare da d'ansa" Kallonsa suka yi sannan Amatullahi ta ce "gurinki ina ga ya zo" tsaki Hafsa ta ja sannan ta ce "wannan kuma shi ya sani" Yaya Safwan ya hango Hafsa tare da wasu yammata su biyu da sauri ya kamata hannun Khalid suka nufi gurin da suke, Hafsa ce a tsakiyarsu dan haka yana isa gurin yayi musu sallama "Assalamu alaikum" Khadijatullahi da Amatullahi ne suka amsa masa sallamar "Wa'alaikumussalam" suka yi gaba domin su basu damar yin magana, Hafsa ganin haka ita ma ta bi su da sauri Khalid ya kama hannun Hafsan yana cewa "Mommy ki tsaya Abbana zai yi magana dake dan Allah" kallon yaron tayi kamar ta ture yaron sai kuma ta tsaya Safwan ya k'araso inda suke ya dafa kan Khalid tare da cewa "Nagode yarona" Safwan ya bud'e baki zai yi mata magana ta dakatar dashi da cewa "yanzu ina tare da bestyna ka bari ka zo gida muyi magana" tayi maganar ba tare da ta kalleshi ba, tafiya ta fara yi Khalid yana biye da ita tsayawa tayi tana kallonsa ta bud'e baki zata yi masa magana Khalid ya rigata da cewa "Mommy zan biki dan Allah karki ce A'a" Hafsa ta ce "Ka tambayi Abbanka idan ya bar ka sai mu tafi" Safwan ya ce "Haba babyna ai kema Khalid kamar 'dan ki ne dan haka zaki iya tafiya dashi zan zo in d'aukeshi daga nan sai muyi maganar" kama hannu Khalid d'in tayi sannan ta nufi inda su Khadijatullahi suke d'an har sun fita daga cikin makarantar tana zuwa gurin da su Amatullahi suke ta watsa musu harara sannan ta ce "Shine zaku wani tafi ku bar ni" Murmushi Amatullahi tayi sannan ta ce "Ahh mun tsaya ai dole mu baku guri domin a ji dad'in bawa flower ruwa sosai".
Suna fitowa suka yi sa'a ga wani mai adaidaita zai fita daga layin suka tsayar dashi suka shiga Amatullahi ta ce "Baba poly zaka kai mu ta gadon k'aya" kasancewar mai adaidaitar tsoho ne, shiyasa ta ce masa Baba, ya amsa mata da "to" suna isa Khadijatullahi ta bud'e jakarta ta d'auko naira d'ari biyar wacce ita kenan da ita zata mik'awa mai adaidatan Amatullahi ta dakatar da ita da cewa "to Hajiyata ai sai ki bari in biya ko?" ta fad'a tana mik'awa mai adaidatan naira d'ari biyar tunda daman a haka ake kawo su makarantar, suka shiga makarantar suna zuwa suka tarar da Hafsa har tazo abin da ya basu mamaki shine abayar da Hafsa ta saka komai iri d'aya da tasu babu abin da ya bambanta k'arasawa gurinta suka yi Amatullahi ta ce "Besty Hafseyy yau fa kinsa mun shiga mamaki sosai" murmushi tayi ta ce "Saboda kayan da nasa irin naku ko?" Khadijatullahi ta ce "Wallahi kuwa komai irin d'aya" Hafsa ta ce "ba abin mamaki ba ne ai, saboda tun jiya da muka je gidanku na ga abayar Khadijatullahi a kan gado kawai naji jikina ya bani ita zaku saka yau sai na k'are mata kallo Allah yasa naga kwalliyar jikin abayar duk da cewa ba duk na gani ba, shine muna tafiya na tsaya na saya a wani super market, murmushi suka yi gaba d'ayansu sannan suka nufi hanyar ajinsu domin an kusan fara lecture, basu dad'e da shiga ba Malam ya shigo suka fara lectures.
••••••••••••••••••••••••••••••••••••••••••••••••••••••••••••••••••••••••••
*'BANGAREN GIDANSU JABIR*
Jabir ne tsaye a gaban madubi yana kallon kansa ya gama shirinsa tsaf cikin wasu kaya gajeren wando ne wanda ko guiwarsa bai kai ba sai wata farar riga wanda a bayanta an rubuta *JABIR D'AN TUWA* da manyan harafai gashin kansa ya kwanta luf sai shek'i yake yi, haka ya fito babban falo, babu kowa a falon dan haka ya nufi kofar fita daga falon, Jabir yana bud'e kofar falon Aliyu na fitowa daga d'akinsa kallo d'aya yayi masa ya d'auke kansa domin kuwa wani irin haushin Jabir d'in yake ji, shi kuwa Jabir bai ga Aliyu ba saboda ya riga ya fita daga falon, motarsa ya nufa ya shiga ya jaa ta da gudu mai gadi yayi saurin bud'e masa gate ya fita daga gidan wak'ar babban mawak'in yahudawa ya saka Ojoro wanda Omale yayi ya k'ure kid'an yana bin wak'ar a hankali, Club ya nufa yana isa farfagiyar club d'in ya tarar da wasu 'yammata su biyu a tsaye, fita yayi daga cikin motar ya nufi inda wad'annan 'yanmatan suke kai masha Allahu kyawawa ne ajin farko, sanye suke da wasu d'ammun riga da wando sun yafa wani d'an k'aramin mayafi, k'are musu kallo yayi bai tab'a ganinsu a club d'in ba "Yau akwai chilling kenan, wad'annan daga ganinsu sababbin hannu ne" ya fad'a a zuciyarsa a fili kuma ya ce "Hi bebs" cikin wata iriyar muryarsa ta shu'uman 'yan bariki, murmushi suka sannan suka ce Jabir d'an tuwa, bai yi mamakin jin sun fad'i sunansa ba domin kuwa Jabir yayi k'aurin suna gurin iskanci da shaye-shaye, murmushi yayi sannan ya ce "Sannunku bebs ya kamata ku fad'a min sunayenku domin nima nasani" d'aya daga ciki ta ce "sunana zulaihat amman zaka iya kirana da Zuly baby, sai ta nuna d'ayar ta ce wannan kuma sunanta Ummita" Jabir yayi kayatatcen murmushi sannan ya kama hannayensu yayi cikin hotel d'akinsa ya nufa ya bud'e sannan suka shiga gaba d'ayansu suka bage hajarsu a kan gado Jabir yana kwance a kan gadon su kuma sun kwanta a jikinsa suna shafa shi tare da kissing d'in jikinsa (tofa jama'a Jabir bai saduda ba, Allah dai ya kyauta) haka sukai ta aikata bad'ala har sai wajen k'arfen biyar da rabi sannan Jabir ya tashi daga kan su Zuly yayi wanka ya dawo ya fara kok'arin shiryawa Zuly da Ummita suka matso kusa dashi suka shiga shiryashi Jabir kuwa wani irin farin ciki ne ya kamashi tabbas wad'annan 'yammatan sun iya soyayya sai da suka gama tsaf sannan ya tashi ya bashi rabar 'yan dubu dubu ya fita daga d'akin Zuly da Ummita murna fal ciki dan tunda suke harkar bariki babu wanda ya tab'a basu dubu ashirin ma barantana har a basu rabar 'yan dubu dubu, shi kuwa Jabir ko cikin club d'in bai shiga ba ya shiga mota ya nufi layinsu Khadijatullahi.
~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~
*Poly🔱🏨*
Wajen k'arfe shida dai-dai aka tashi daga makarantar, su Khadijatullahi suka fito daga aji Hafsa ta hango Yaya Safwan a jikin motarsa ya hard'e hannunsa a k'irjinsa yana ta baza idanuwana ya ga inda zai hango Hafsa gefensa wani kyakkyawan yaro ne wanda shekarunsa ba zai huce 6 ba,kamanninsa d'aya da yaron, Hafsa cike da mamaki had'i da bak'in ciki take nunawa su Amatullahi gurin da Yaya Safwan d'in yake ta ce "kun ga wanchan tsohon azzalumin yazo tare da d'ansa" Kallonsa suka yi sannan Amatullahi ta ce "gurinki ina ga ya zo" tsaki Hafsa ta ja sannan ta ce "wannan kuma shi ya sani" Yaya Safwan ya hango Hafsa tare da wasu yammata su biyu da sauri ya kamata hannun Khalid suka nufi gurin da suke, Hafsa ce a tsakiyarsu dan haka yana isa gurin yayi musu sallama "Assalamu alaikum" Khadijatullahi da Amatullahi ne suka amsa masa sallamar "Wa'alaikumussalam" suka yi gaba domin su basu damar yin magana, Hafsa ganin haka ita ma ta bi su da sauri Khalid ya kama hannun Hafsan yana cewa "Mommy ki tsaya Abbana zai yi magana dake dan Allah" kallon yaron tayi kamar ta ture yaron sai kuma ta tsaya Safwan ya k'araso inda suke ya dafa kan Khalid tare da cewa "Nagode yarona" Safwan ya bud'e baki zai yi mata magana ta dakatar dashi da cewa "yanzu ina tare da bestyna ka bari ka zo gida muyi magana" tayi maganar ba tare da ta kalleshi ba, tafiya ta fara yi Khalid yana biye da ita tsayawa tayi tana kallonsa ta bud'e baki zata yi masa magana Khalid ya rigata da cewa "Mommy zan biki dan Allah karki ce A'a" Hafsa ta ce "Ka tambayi Abbanka idan ya bar ka sai mu tafi" Safwan ya ce "Haba babyna ai kema Khalid kamar 'dan ki ne dan haka zaki iya tafiya dashi zan zo in d'aukeshi daga nan sai muyi maganar" kama hannu Khalid d'in tayi sannan ta nufi inda su Khadijatullahi suke d'an har sun fita daga cikin makarantar tana zuwa gurin da su Amatullahi suke ta watsa musu harara sannan ta ce "Shine zaku wani tafi ku bar ni" Murmushi Amatullahi tayi sannan ta ce "Ahh mun tsaya ai dole mu baku guri domin a ji dad'in bawa flower ruwa sosai".