Sashe 48
Daren Aurena Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Kullum Zaituna sai ta kawo mata abinci da daddare bayan kowa ya kwanta kuma babu wanda ya tab'a kamata, Zaune take a tsakar gida wajen k'arfe 5:00pm na yamma tana daka yaji sai ga Lado ya shigo ko sallama bai yi ba, Kallo d'aya Zaituna tayi masa ta kawar da kanta dan tunda ta ga irin wulak'anci da ya ke yi wa mahaifiyarsa ta ji ta tsaneshi kwata-kwata, shi kuma Lado yana ganin Zaituna ya saki murmushi tare da k'arasowa gurin da take, wata 'yar k'aramar kujerar k'arfe ya ja ya zauna tare da kiran sunanta "Zaituna" Bata amsa masa ba sai ma cigaba da aikinta da tayi, shi kuma bai damu ba ya cigaba da yin magana "Shine jiya na aiko a kira ki, ki ka k'i zuwa ko?","A'a ni babu wanda ya zo ya kira ni" Tayi maganar ba tare da ta kalleshi ba "kina nufi Idi bai zo ya kira ki ba?","Idi ya zo amman kuma ni bai ce min kirana ake yi ba" Nan Lado ya shiga zabgawa Idi kira "Idi kai idi kana ina?" Da sauri Idi ya fito daga d'akinsu tare da zuwa ya tsugunna kusa da Lado "Ga ni Yaya" Lado ya d'aure fuska tare da cewa "Jiya da nace ka je ka kira min Zaituna ashe da ka je ba ka kirata ba, ka zo ka ce min ka kirata ta ce tana zuwa" Idi ya zaro ido ya ce "Wallahi Yaya na kirata ai gata nan ka tambayeta na san Aunty Zaituna ba ta k'arya za ta fad'a maka gaskiya" Zaituna ta ce "Eh ya kirana ni kawai bai yi niyyar zuwa ba ne" Lado ya kalleta sororo kamar wanda aka dasa shi dai a saninsa Zaituna ba ta da rashin kunya amman yau gashi ta kalli cikin kwayar idonsa tana gaya masa magana mara dad'i ji yayi kamarya d'auketa da mari amman kuma da ya tuna cewar yana sonta sosai kuma hakan zai iya jawowa a k'i bashi aurenta ya sa ya fasa, ya fara magana cikin tsawa.
"Ke Zaituna yaushe ki ka koyi raina na gaba da ke, wato wuyanki ya yi kaurin da har zan aika ki zo ina son ganinki ki k'i zuwa amman"........ "Ka ga Lado dan Allah dan annabi ka bar ni na sha iska, meye ruwanka da ni ko akwai abin da na tsare maka ne da har za ka ke fad'a min maganar da ka ga dama, ni ba zan tab'a yiwa wanda bai san darajar mahaifiyarsa biyayya ba, saboda haka zaka iya b'ace min da gani" Zaituna ta yi maganar cikin tsiwa tare da hurga masa harara, Lado ya tsaya sororo yana kallonta cike da mamaki, tunda suke da ita ba ta tab'a kallon cikin idonsa ta gaya masa maganar mara dad'i ba sai yau, kuma ba ta tab'a kiran sunansa ba sai dai ta ce masa Yaya amman yau gashi tana kiransa da asalin sunansa, "Zaituna ni ki ke gayawa wad'annan maganganun, kuma ki ke kirana da Lado" Ya yi maganar tare da tsare ta da ido zuciyarsa tana bugawa da k'arfi, wani irin kallon ta yi masa tare da cewa "Yo to menene sunanka idan ba Lado ba, kuma kai wanene da ba zan gaya maka gaskiya ba, ka je kayi wa mahaifiyarka biyayya ka bata hak'uri tun kafin dare ya yi maka" Tana gama fad'ar haka ta shige d'akinta da sauri tare da rufe kofa, shi kuwa Lado jikinsa a sanyaye ya mik'e ya nufa d'akinshi, zuciyarsa cike da bak'in ciki yana shiga d'akin ya zauna tare da zabga tagumi yana tunanin maganganun da Zaituna ta fad'a masa, ya d'auki kusan mintina talatin yana tunanin daga k'arshe ya kwanta a kan gadonsa tare da lumshe idanuwansa.
*'BANGAREN JABIR DA TEEMARH☹️*
Yau kusan kwana bakwai Jabir bai fito ko da falo ba, kullum yana d'aki yana kok'arin shawo kan Teemarh amman abin ya gagareshi, Teemarh ba ta da aiki sai dai ta zauna tai-ta yin kuka, fuskarta gaba d'aya ta kumbura tayi jajahur idanuwanta kuwa da kyar take iya bud'e su, saboda irin kukan da ta ke yi yasa su ka yi ciki-ciki, "Haba Daring ya kamata ki tsaya ki saurareni, wallahi akwai dalilin da yasa na je club ranar plss My Teemarh ki saurareni ba na son kina yin wannan koke-koken" Jabir wanda ya ke kusa da Teemarh a kan gado ya yi maganar fuskarsa tana nuna alamun damuwa, "Jabir na san baka so na dan Allah ka kyaleni" Teemarh wacce take kwance a kan gadon tana faman rera kuka tayi maganar cikin muryar kuka, "Wai wa ya ce miki ba na sonki, wallahi Teemarh ina sonki sosai dan Allah ki daina kukan nan, ki fad'a min abin da ki ke son nayi miki da zai saka ki yarda ina sonki" Teemarh ta d'ago fuskarta tare da zuba masa idanuwanta "Ka tabbatar duk abin da na fad'a maka za kai min" Jabir ya gyad'a kai tare da cewa "Indai hakan zai saka ki farin ciki, zan yi miki ko ma menene".
"Darling ina son ka daina zuwa club, duk abin da ka ke so ni zan yi maka shi koma menene,amman dan Allah ka daina zuwa club ba dan ni ba, dan Allah na rok'eka da girman Allah" Jabir ya yi shuru kamar ba zai yi magana ba, sai kuma ya ce "Na amince darling indai hakan zai sa ki yarda cewar ina sonki" Teemarh ta yi murmushi "Da gaske ka ke Darling" Jabir ya yi murmushi "Eh mana, da gaske na ke, babyn Jabir" Ajiyar zuciya Teemarh ta sauke tare da cewa "To darling na yarda kuma na san ba za ka k'arya min alk'awarina ba, yawwah Darling dan Allah ina son na je gidan Hajiya Mama yau na dad'e ban je ba" Jabir ya jawo Teemarh jikinsa yana shafata "To darling da yaushe za ki je","Ni ko yanzu ma" Jabir ya ce "Nop ba yanzu ba dai sai anjima" Teemarh ta ce "Allah ya kaimu" Jabir ya ce "Amin ya Allah" Nan ya shiga shafe jikin daga nan suka tsunduma duniyar soyayya.
_Habibaties ku yi min addu'a ba ni da lafiya cikina ke ciwo😭👏🏽_
*'BANGAREN AMATULLAHI🤣💃🏽*
Amatullahi ta je gurin club d'in su Jabir amman abin mamakin har ta gaji da tsayuwa amman ba ta ga jibtawar Jabir ba, anan take tambayar wani mai shago Jabir ya daina zuwa ne?, da yake kaf unguwar babu wanda bai san shi ba, saboda irin shaharar da ya yi wajen lalata yaran mutane, ya ba ta amsa da cewa yau kusan sati guda Jabir bai zo club d'in nan ba, kuma gaskiya na ji labarin cewar matarsa ce take son ta hana shi zuwa, Amatullahi tayi masa godiya ta nufi gidan Hajiya Mama zuciyarta cike da mamakin wace 'yar kasada ce ta auri Jabir, kuma da wad'anne irin kalmai ta ja ra'ayin d'an iskan nan ya daina zuwa club, k'wafa ta yi tare da cewa "Koma wacece ita ta ga za ta iya" A haka ta k'arasa gidan Hajiya Mama, Falon saukar bak'i ta shiga tare da zama ta kunna t.v tashar arewa 24 ta kai anan ta tarar ana yin wani film d'in hausa, film d'in ya yi matuk'ar jan ra'ayinta sosai, gaba d'aya ta maida hankalinta wajen kallon film d'in.
"Besty! Besty!! Besty!!!" Ta ji muryar Khadijatullahi tana kiranta, mik'ewa ta yi da sauri ta fita daga falon "Na'am Bestyna" Amatullahi ta yi maganar tana k'arasawa kusa da ita "Ina ki ka je? Tun d'azu ina ta faman nemanki" Murmushi Amatullahi ta yi "Yau Babana ya dawo ne, shine na je gurinshi" Khadijatullahi ta kafeta da ido, tabbas ta san Amatullahi ba gaskiya ta ke fad'a mata ba, dan tun suna k'anana indai Amatullahi ta yi magana tana iya gane cewar k'arya take fad'a ko kuma gaskiya "Yau kuma k'arya za ki yi min bestyna, ban yi tunanin za ki iya k'in fad'a min halin da ki ke ciki ba, na san ba gaskiya ki ke fad'a ba Baba bai dawo ba, dan in ya dawo zaki ce min na zo muje mu gaishe dashi" Da sauri Amatullahi ta kalli Khadijatullahi daman ta san zata iya gane cewar k'arya ta ke yi mata "Besty dan Allah ki fahimceni" Khadijatullahi ta ce "Ba na son ki ce min komai domin ba na gana da mak'aryaciya" Khadijatullahi tana gama fad'ar haka ta shige babban falon ta zauna a kan kujera tana kallon Aliyu tana sakar masa murmushi "Yaya Aliyu na bar ka kana ta jira na ko, dan Allah ka yi hak'uri" Aliyu ya bud'e baki zai yi magana Amatullahi ta shigo falon tare da zuwa gurin da Khadijatullahi ta ke zaune ta tsugunna "Haba besty kin san ban tab'a yi miki k'arya ba, wallahi bestyna gurin"....... Khadijatullahi ta dakatar da ita da hannu fuskarta a murtuk'e "Dan Allah ki tafi kawai ba na son ganinki".
"Ke Zaituna yaushe ki ka koyi raina na gaba da ke, wato wuyanki ya yi kaurin da har zan aika ki zo ina son ganinki ki k'i zuwa amman"........ "Ka ga Lado dan Allah dan annabi ka bar ni na sha iska, meye ruwanka da ni ko akwai abin da na tsare maka ne da har za ka ke fad'a min maganar da ka ga dama, ni ba zan tab'a yiwa wanda bai san darajar mahaifiyarsa biyayya ba, saboda haka zaka iya b'ace min da gani" Zaituna ta yi maganar cikin tsiwa tare da hurga masa harara, Lado ya tsaya sororo yana kallonta cike da mamaki, tunda suke da ita ba ta tab'a kallon cikin idonsa ta gaya masa maganar mara dad'i ba sai yau, kuma ba ta tab'a kiran sunansa ba sai dai ta ce masa Yaya amman yau gashi tana kiransa da asalin sunansa, "Zaituna ni ki ke gayawa wad'annan maganganun, kuma ki ke kirana da Lado" Ya yi maganar tare da tsare ta da ido zuciyarsa tana bugawa da k'arfi, wani irin kallon ta yi masa tare da cewa "Yo to menene sunanka idan ba Lado ba, kuma kai wanene da ba zan gaya maka gaskiya ba, ka je kayi wa mahaifiyarka biyayya ka bata hak'uri tun kafin dare ya yi maka" Tana gama fad'ar haka ta shige d'akinta da sauri tare da rufe kofa, shi kuwa Lado jikinsa a sanyaye ya mik'e ya nufa d'akinshi, zuciyarsa cike da bak'in ciki yana shiga d'akin ya zauna tare da zabga tagumi yana tunanin maganganun da Zaituna ta fad'a masa, ya d'auki kusan mintina talatin yana tunanin daga k'arshe ya kwanta a kan gadonsa tare da lumshe idanuwansa.
*'BANGAREN JABIR DA TEEMARH☹️*
Yau kusan kwana bakwai Jabir bai fito ko da falo ba, kullum yana d'aki yana kok'arin shawo kan Teemarh amman abin ya gagareshi, Teemarh ba ta da aiki sai dai ta zauna tai-ta yin kuka, fuskarta gaba d'aya ta kumbura tayi jajahur idanuwanta kuwa da kyar take iya bud'e su, saboda irin kukan da ta ke yi yasa su ka yi ciki-ciki, "Haba Daring ya kamata ki tsaya ki saurareni, wallahi akwai dalilin da yasa na je club ranar plss My Teemarh ki saurareni ba na son kina yin wannan koke-koken" Jabir wanda ya ke kusa da Teemarh a kan gado ya yi maganar fuskarsa tana nuna alamun damuwa, "Jabir na san baka so na dan Allah ka kyaleni" Teemarh wacce take kwance a kan gadon tana faman rera kuka tayi maganar cikin muryar kuka, "Wai wa ya ce miki ba na sonki, wallahi Teemarh ina sonki sosai dan Allah ki daina kukan nan, ki fad'a min abin da ki ke son nayi miki da zai saka ki yarda ina sonki" Teemarh ta d'ago fuskarta tare da zuba masa idanuwanta "Ka tabbatar duk abin da na fad'a maka za kai min" Jabir ya gyad'a kai tare da cewa "Indai hakan zai saka ki farin ciki, zan yi miki ko ma menene".
"Darling ina son ka daina zuwa club, duk abin da ka ke so ni zan yi maka shi koma menene,amman dan Allah ka daina zuwa club ba dan ni ba, dan Allah na rok'eka da girman Allah" Jabir ya yi shuru kamar ba zai yi magana ba, sai kuma ya ce "Na amince darling indai hakan zai sa ki yarda cewar ina sonki" Teemarh ta yi murmushi "Da gaske ka ke Darling" Jabir ya yi murmushi "Eh mana, da gaske na ke, babyn Jabir" Ajiyar zuciya Teemarh ta sauke tare da cewa "To darling na yarda kuma na san ba za ka k'arya min alk'awarina ba, yawwah Darling dan Allah ina son na je gidan Hajiya Mama yau na dad'e ban je ba" Jabir ya jawo Teemarh jikinsa yana shafata "To darling da yaushe za ki je","Ni ko yanzu ma" Jabir ya ce "Nop ba yanzu ba dai sai anjima" Teemarh ta ce "Allah ya kaimu" Jabir ya ce "Amin ya Allah" Nan ya shiga shafe jikin daga nan suka tsunduma duniyar soyayya.
_Habibaties ku yi min addu'a ba ni da lafiya cikina ke ciwo😭👏🏽_
*'BANGAREN AMATULLAHI🤣💃🏽*
Amatullahi ta je gurin club d'in su Jabir amman abin mamakin har ta gaji da tsayuwa amman ba ta ga jibtawar Jabir ba, anan take tambayar wani mai shago Jabir ya daina zuwa ne?, da yake kaf unguwar babu wanda bai san shi ba, saboda irin shaharar da ya yi wajen lalata yaran mutane, ya ba ta amsa da cewa yau kusan sati guda Jabir bai zo club d'in nan ba, kuma gaskiya na ji labarin cewar matarsa ce take son ta hana shi zuwa, Amatullahi tayi masa godiya ta nufi gidan Hajiya Mama zuciyarta cike da mamakin wace 'yar kasada ce ta auri Jabir, kuma da wad'anne irin kalmai ta ja ra'ayin d'an iskan nan ya daina zuwa club, k'wafa ta yi tare da cewa "Koma wacece ita ta ga za ta iya" A haka ta k'arasa gidan Hajiya Mama, Falon saukar bak'i ta shiga tare da zama ta kunna t.v tashar arewa 24 ta kai anan ta tarar ana yin wani film d'in hausa, film d'in ya yi matuk'ar jan ra'ayinta sosai, gaba d'aya ta maida hankalinta wajen kallon film d'in.
"Besty! Besty!! Besty!!!" Ta ji muryar Khadijatullahi tana kiranta, mik'ewa ta yi da sauri ta fita daga falon "Na'am Bestyna" Amatullahi ta yi maganar tana k'arasawa kusa da ita "Ina ki ka je? Tun d'azu ina ta faman nemanki" Murmushi Amatullahi ta yi "Yau Babana ya dawo ne, shine na je gurinshi" Khadijatullahi ta kafeta da ido, tabbas ta san Amatullahi ba gaskiya ta ke fad'a mata ba, dan tun suna k'anana indai Amatullahi ta yi magana tana iya gane cewar k'arya take fad'a ko kuma gaskiya "Yau kuma k'arya za ki yi min bestyna, ban yi tunanin za ki iya k'in fad'a min halin da ki ke ciki ba, na san ba gaskiya ki ke fad'a ba Baba bai dawo ba, dan in ya dawo zaki ce min na zo muje mu gaishe dashi" Da sauri Amatullahi ta kalli Khadijatullahi daman ta san zata iya gane cewar k'arya ta ke yi mata "Besty dan Allah ki fahimceni" Khadijatullahi ta ce "Ba na son ki ce min komai domin ba na gana da mak'aryaciya" Khadijatullahi tana gama fad'ar haka ta shige babban falon ta zauna a kan kujera tana kallon Aliyu tana sakar masa murmushi "Yaya Aliyu na bar ka kana ta jira na ko, dan Allah ka yi hak'uri" Aliyu ya bud'e baki zai yi magana Amatullahi ta shigo falon tare da zuwa gurin da Khadijatullahi ta ke zaune ta tsugunna "Haba besty kin san ban tab'a yi miki k'arya ba, wallahi bestyna gurin"....... Khadijatullahi ta dakatar da ita da hannu fuskarta a murtuk'e "Dan Allah ki tafi kawai ba na son ganinki".