← Book details Daren Aurena Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 26 OF 54

Sashe 26

Daren Aurena Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Shi kuwa Alhaji Mansur a tsakar gidan ya shimfid'a taburma suka zauna da Hajiya Mama suna hirarsu ta d'a da uwa, su Amatullahi da Khadijatullahi ne suka yi sallama domin yau sun ji Aunty Murjan ta dad'e sosai ba ta dawo ba shiyasa suka biyo bayanta "Lale da zuwa 'yan tagwaye wato yau kun ji auntyn ta ku shuru ba ta dawo ba ko?" Hajiya Mama tayi tunanin Amatullahi da Khadijatullahi 'yan biyu ne shiyasa take ce musu tagwaye"Eh Hajiya mun ga har yanzu k'arfe sha biyu na rana kuma idan ta koma tana dawowa k'arfe biyu shiyasa muka zo mu taimaka mata da aikin" Amatullahi ta fad'a sannan suka tsugunna suka gaishe da Hajiya Mama da Alhaji Mansur.

Suka amsa fuskarsu cike da fara'a Hajiya Mama ta dora da cewa "Ai kuwa daga yau tare da ku zamu dinga zama domin kuwa Auntynku yau an d'aura mata aure anjima kad'an za'ayi walima tana d'aki wanka take yi" Khadijatullahi ta d'ago da sauri tana mamaki "An d'aura mata aure kuma?","Eh Khadija" Hajiya Mama ta bata amsa a takaice, Amatullahi kuwa murna ce ta isheta "Kai Hajiya Mama amman na ji dad'i ya kamata na yi miki kyautar goro" Amatullahi ta fad'a tana murmushi, duk da yanayin da Khadijatullahi take ciki domin tsoro take kar ayi wa Aunty Murjan abin da Jabir yayi mata a daren aurensu sai da maganar Amatullahi ta bata da dariya ta ce "Hajiya karki yarda so take ta mayar da ke tsohuwa kuma fa tasan kin fi ta jii da kuruciya" Alhaji Mansur dariya yayi sosai sannan ya ce "Lallai 'yan k'annan nan na wa sai na zane ku Hajiyan ku ke yi wa tsiya haka" Hajiya Mama ta ce "Kyalesu ai Allah ya kawo mu, zasu fara yi min tsiya" Gaba d'ayansu dariya suka yi sosai.

Nan Hajiya Mama take fad'a musu cewa Alhaji Mansur shi ne ya auri Aunty Murja, sai a lokacin hankalin Khadijatullahi ya d'an kwanta domin ta fahimci Alhaji Mansur d'in ba zai tab'a iya aika irin abin da Jabir yayi mata ba, haka dai sukai ta wasa da dariya abin gwanin ban sha'awa.

*'BANGAREN GIDANSU JABIR😂*

Zaune suke a falo gaba d'ayansu suna kallon film d'in Tarkon k'auna a tasha arewa 24 Shahida da ke zaune a kan kujera one sitter ta d'auki remote ta chanza tasha zuwa Tauraruwa tv,Hajiya Asiya ta bud'e baki cike da masifa zata fara zazzagawa Shahida masifa sai ji tayi ana sanar da d'aurin auren Alhaji Mansur da Aunty Murja tare da katin Walimar da za'ayi a gidan Hajiya Mama da misalin k'arfe 2:00pm na rana.

A zabure Hajiya Asiya da Jabir suka tashi bakin Hajiya Asiya na rawa ta fara cewa "me nake ji a cikin t.v Abban Jabir yayi aure" Fad'uwa tayi k'asa sumammiya, Jabir kuwa zage-zage ya shiga yii, Aliyu ne ya d'auko ruwan sanyi ya watsawa Hajiya Asiya a fuska nan ta farfad'o wani irin kuka ta fashe dashi "na shiga uku innalillahi wa inna'ilaihi raju'un Alhaji ya kashe min rayuwa ya lalata min duk wani burina wallahi duk wacce tayi gangancin zuwa gidan nan da sunan kishiyata sai na kasheta wallahi sai na illatata sai dai a fita da gawarta wannan gidan da kuma Abban Jabir nawa ne ni kad'ai babu wata shegiyar da ta isa na had'a miji da ita, kuma wannan munafikar uwarta sa wallahi sai na yi mata abin da ba za ta tab'a mantawa da ni ba" Tana kuka take maganar.

Aliyu da Shahida kuwa tashi suka yi kowannan su ya nufi d'akinshi, Teemarh kuwa tashi tayi tare da fashewa da wata iriyar mahaukaciyar dariya "kai ya ubangiji yau ban san wane irin farin ciki na ke ciki ba, gaskiya zan je walima na ta ya Abba farin ciki, gwanda da yayi auren wannan shine abin da ya dace da jakar uwa irin ki" Tana gama fad'ar haka ta wuce d'akinta domin shiryawa zuwa walimar bikin Abba.

Jabir ya ji haushin maganganun da Teemarh ta fad'awa Maminshi amman yanzu ba ta ita yake ba, domin kuwa suna cikin tashin hankali shi da mahaifiyarsa, haka dai suka zauna kowan ne daga cikinsu zuciyarsa kamar zata fashe saboda bak'in ciki musamman Hajiya Asiya.

(ni kuwa nace Alhaji Mansur ka yi min dai-dai😂😂Hajiya Asiya Allah ya k'ara😹💃🏽💃🏽yau akwai shagali a gidan Hajiya Mama💃🏽💃🏽ina kuke Ummu juwairiyya djamila da dai sauransu ana gayyatar ku fa💃🏽💃🏽)

*'BANGAREN LADO DA INNA LARAI😹*

Lado ya tadawa Inna Larai hankali a kan sai ta biya shi kud'insa gaba d'aya ya chanza mata, kullum cikin bala'i yake mata ita kuma Inna Larai ba ta san inda zata samu kud'i ta biya shi ba domin kuwa akalla kud'in zai kai naira dubu goma sha biyu, Lado kuwa ko bacci ba ya iyawa dan har zazzab'i yayi saboda kud'insa dakyar Inna Larai ta lallab'ashi a kan zata ce Malam Shu'aibu ya turo mata da kud'i idan ya turo mata sai ta biya shi, Lado bai yarda ba har sai da Inna Larai ta je wajen masu kira, ta basu number Malam Shu'aibu suka kira shi ta fad'a masa cewa tana buk'atar kud'i naira dubu sha biyar domin katangar d'akinta ta fad'i ta kira masu gyara sun gyara amman kuma ba ta da kud'in da za ta biya su, Malam Shu'aibu ya ce zai turo mata da kud'in a cikin satin nan sai ta biya masu gyaran, sannan Lado ya hak'ura zuwa lokacin da Malam Shu'aibu zai turo kud'in.

*'BANGAREN NIHAL🥳*

Tun da suka koma gidan Nihal ta shiga nunawa Mijinta Salis soyayya a waje d'aya suke samun matsala idan zai kwanta da ita dan kullum sai sun yi fad'a da ita duk da cewa Salis d'in shima yana kok'arin ganin ya nunawa Nihal d'in soyayya amman shi yana da k'arfin sha'awa ba zai iya jurewa ba, yau ma kamar kullum tana kwance a kan gado tana bacci sai jin mutum ta yi a jikinta yana ta tsotsarta kuka ta saka ta fara rok'onsa "Dan Allah Yaya Salis kabarni haka na d'azu ma bai warke ba, wallahi zan iya mutuwa" Yau kam Salis ya zo da mutunci rarrashinta ya shiga yii cikin wata iriyar murya mai narkar da zuciya "Haba babyna ki yi hak'uri kinji ba zan miki da zafi ba, zan miki a hankali ba za ki ji zafi ba, kin san dai ina sonki ba na son abin da zai dinga saka ki kuka kema kuma na san kina sona ba za ki so ace na shiga wahala ba, ki taimaka min kinji babyna" ya k'arasa maganar cikin muryar tausayi.

Nihal ta kalleshi sosai cikin sanyi murya ta ce "da gaske ba za ka min da zafi ba?" kai ya gyad'a mata alamar "eh" Nihal tayi murmushi sannan ta ce "Ok babyn baby go ahead" Murmushi yayi sosai tare da cewa "to babyn baby na gode da aka bani izini". Haka Salis yayi ta bin ta a hankali har sai da ya gama shan zumarta sannan ya sauka daga kanta tare suka yi wanka sun d'auki kusan awa guda suna wankan kamar ba zasu fito ba, bayan sun fito suka shirya cikin wasu riga da wando pink colour komai iri d'aya ne, sun yi kyau sosai zama suka yi a falo suna kallo, nan Salis yake shaida mata Abba yau ya k'ara aure abin ya girgizata sosai, amman kuma a wani b'angaren ta ta ya Abban farin ciki sabida ta san zaman hak'uri yake da ita.

Talatu kuwa tunda ta koma gidansu ita da yaronta take ta kulla makirci iri-iri tana zuwa tana kai wa mahaifiyar Salis d'in labarai a kan Nihal d'in karuwa ce saboda an rasa waye zai aureta shiyasa a ka mak'alawa Salis aurenta tun Mama bata yarda har ta saka akai mata binkice a kan Nihal d'in aka tabbatar mata da cewa Nihal ta tab'a karuwanci dan saboda haka ne ma a ka yi mata aure, ran Mama ya b'aci sosai nan ta shirya ta nufi gidan Salis tana zuwa gidan ta shiga falon babu ko sallama a zaune ta tarar dasu suna kallo tashi suka yi suna mata sannu da zuwa.

Wata uwar harara ta shiga hurgawa Nihal d'in cikin masifa ta shiga cewa "To munafuka tsohuwar kilaki asirinki ya tonu wato kin je kin gama yawon iskancinki shine zaki zo ki mak'alewa yarona to wallahi ba'a nan gidan ba dan yanzun nan ba sai anjima ba Salis zai sake ki ki je ki cigaba da yawon barikin na ki" tana gama fad'ar haka ta juyo kan Salis tana cewa "ka saketa ko kuma na tsine maka",Salis ya shiga tashin hankali ya shiga kok'arin rarrashin Mama amman sam ta tubure a kan ko ya saketa ko ta tsine masa.

Nihal tana kuka ta kalli Salis tana cewa "Yaya Salis ka bi umarnin da Mama ta ba ka, ba na so na zama silar rabuwarka da mahaifiyarka ka sake ni kawai na sani kana sona sosai nima ina sonka amman ya zama dole mu rabu da juna" Salis ya rintse ido zuciyarsa nayi masa zafi cikin rawar murya ya ce "Nihal ki je gida" Luuuuuu ya fad'i k'asa sumamme Nihal ta saka kuka ta nufeshi amman Mama ta daka mata tsawa tare da cewa "ki tafi gidan ubanki, ba ya buk'atarki" Haka Nihal ta shiga d'aki ta had'a kayanta a akwati ta fito tana jan akwatin gidan Hajiya Mama ta nufa tana kuka, a zaune ta tarar da ita tare da Abbansu da wasu 'yanmata guda biyu a jikin Hajiya Mamar ta fad'a tare da fashewa da kuka tana fad'in.
"Hajiya Mama na shiga uku dan Allah ki taimaka min" Tayi maganar tana k'ara sautin kukanta, Hajiya Mama ta ce "meya faru takwarata","Hajiya ta raba ni da Yaya Salis, Hajiya ta ce sai ya sake ni ba za ta yarda ya kuma zama da ni a matsayin matarsa ba" Kuka take yi sosai har sai da kan ta ya fara sara Mata, Hajiya Mama cike da tashin hankali ta ce "wacece wannan da d'anyen hukunci","Maminsa ce"Nihal ta bata amsa tana cigaba da kuka.
Chapter 26 · 0% Book details