Sashe 39
Daren Aurena Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Tafiya ta ke yi cikin nutsuwa da kuma aji, a haka har ta isa club d'in da Jabir ya ke zuwa, nesa da club d'in ta tsaya,daga gurin da take ana iya hango cikin club d'in ta jima tana raba ido ta ga ta ina zata hango Jabir amman babu alamar Jabir a gurin ta shafe kusan awa d'aya tana tsaye sai chan ta hango Jabir ya fito daga hotel yana rumgume da wata budurwa da alama ta sha ta bugu sosai "Shege d'an gidan mahaukaciya, wallahi na juyo gareka sai ka gommace kid'a da karatu" Wani yaro ne ya zo hucewa ta yi saurin kiransa "kai yaro dan Allah zo" Zuwa yaron yayi tare da cewa "ga ni" Wata takadda ta ba shi, sannan ta nuna masa Jabir tare da cewa "Wanchan za ka kaiwa wannan takaddar dan Allah" karb'a yayi tare da cewa "to zan ba shi" Yaron ya nufi gurin da Jabir yake sai da Amatullahi ta tabbatar yaron ya ba wa Jabir wannan takaddar sannan ta juya ta nufi gidansu dan ta ga halin da 'yan gidan su ke.
Amatullahi irin yadda take bibiyar Jabir ko mahaifiyarsa Hajiya Asiya ba ta yi masa, dan kuwa duk guraren da ya ke zuwa sai da ta bincikosu kuma duk motsin da yake yi tana sane dashi dan kuwa ya d'auki aniyyar d'aukarwa Khadijatullahi fansar abin da yayi mata sai ta tabbatar da wulak'antasa ta hana shi sukuni, tana shiga gidan ta tarar da abin da ya bata tsoro Inna Larai ta gani tare da Malam d'an ladi mai guga sun fito daga d'akin Inna Larai wani irin ihu ta fasa tare da fita waje ta tsaya dai-dai kofar gidan tana cigaba da kurma ihu, ai kuwa mutane su ka yi kanta suna tambayarta meya faru? "Inna Larai da Malam d'an Ladi mai guga na gani sun fito daga d'aki" Ta yi maganar tana kuka, ai kuwa nan jama'a su ka shiga gidan suka tarar da su Inna Larai da Malam d'an Ladi a tsaye duk sun rud'e dan sun san yau asirinsu ya gama tonuwa, dukan Malam d'an Ladi suka shiga yi ba ji ba gani, Inna Larai ta shige d'aki tare da kulle kofar tana kuka.
Amatullahi kuwa wayar wani Adamu ta ara ta kira Mahaifinta ba fad'a masa komai ba bu abin da ta b'oye masa, hankalinsa ya tashi anan take ya ce ta ba wa Inna Larai ta ce ai ta shiga d'aki ta kulle ya ce to ki ce mata ta gaggauta fitar min daga gida na saketa saki uku, ba na buk'atar sa ke ganinta, a rayuwata yana gama fad'ar haka ya kashe wayar zuciyarsa na yi masa zafi, Adamu ta ba wa wayarsa tare da shiga gidan dan kuwa ba za ta bar Inna Larai ta k'ara ko da minti biyar ba a gidan, d'akinta ta nufa ta d'auko wani k'arfe mai tsini sannan ta nufi d'akin Inna Larai tana buga kofar d'akin da k'arfi tare da cewa "to tsinanniya tsohuwar 'yar bariki ki bud'e kofar nan ki bar mana gida dan Babana ya sake ki saki uku, sai ki je ki cigaba da yin karuwancin na ki a chan wani gurin amman ba'a gidan nan ba" Tana magana tana buga kofar kuma irin bugun da ta ke yi wa kofar ba na wasa ba ne, Inna Larai jin abin da Amatullahi ta ce ta fashe da kuka tare da saka kayanta a buhu ta bud'e kofar dan ta san halin Amatullahi ba ta k'i ta k'arya kofar ba kuma ta yi mata rashin mutunci.
Hanyar fita daga gidan Inna Larai ta nufa tana jin kunyar kanta saboda irin mugayen maganganun da 'yan unguwar ta su suke fad'a mata Amatullahi ta bi ta a baya tana zungurarta da k'arfen tana cewa "Allah ya ra ka taki gona, sai a bi wani sarkin ba dai Yarima ba" Jama'a Unguwar kuwa bayan sun gama yi wa Malam d'an Ladi duka suka cukumeshi sau police station, Amatullahi ta ja kofar gidan ta mukulle da mukulli sannan ta nufi gidan Hajiya Mama ranta fas, dan kuma a rana d'aya ta jefi tsuntsu biyu da dutse d'aya.
*'BANGAREN HAFSA, SAFWAN DA SAFNA😉*
A yau aka saka ranar Safwan da Hafsa wata hud'u aka saka, ta kira Shahida ta fad'a mata sannan ta ce ta fad'awa su bestynta, Shahida ta yi mata murna tare da yi mata Allah ya sanya Alkhairin Hafsa ta amsa da Amin, daga nan suka kashe wayar, tana ajiye wayar ko minti biyar ba'a yi ba wayar ta shiga ruri da sauri ta d'auki wayar tare da kallom screen d'in wayar Hayatee ta gani murmushi tayi tare da d'aga wayar ta kara a kunne tare da cewa "Assalamu alaikum Yayana" Daga chan b'angaren Safwan wanda yake cikin office d'in ya ce "Wa'alaikumussalam Amaryata" Rufe fuskarta Hafsa ta yi kamar yana ganinta ba tare da ta ce komai ba, Safwan yayi ta tsokanarta, amman Hafsa yau kam ba ta biye masa ba, dan wata iriyar kunyarsa take ji dan har ba ta so ya zo dan ba za ta iya fita ba, a haka dai suka d'an d'auki d'an lokaci suna waya daga nan suka kashe wayar.
A b'angaren Safna kuwa tun da safe take aikin kuka dan kuwa ta san rabuwarta da Safwan ta zo, saboda a cewarta idan ya auri Hafsa ya zama ba na ta ba, sai da ta ji kanta ya fara yi mata ciwo sannan ta kwanta a kan doguwar kujera wani irin bacci ne mai nauyi ya kwasheta dan kuwa daman rabonta da bacci tun shekarar jiya dan jiya yadda ta ga rana haka ta ga dare, sai wajen k'arfe 5:00pm na yamma ta farka wanka ta yi sannan ta saka wata doguwar riga pink wacce aka yi wa gaban rigar kwalliya da duwatsu manya manya, dawowa tayi ta kwanta dan kuwa bacci ne a idanuwanta baccin ne ya kwasheta.
Safwan ne ya shigo falon da sallama, idanuwansa suka sauka a kan Safna wacce take bacci fuskarta ya k'urawa ido yana jin tausayin matarta sa ganin yadda fuskarta ta kumbura fuskarta tayi jajawur, k'arasa yayi kusa da ita tare da shafar fuskarta a hankali "Ruhina" Ya kira sunanta a hankali jin ba ta farka ba yasa ya d'auketa cak ya kai ta kan gado ya kwanta da ita, toilet ya shiga shi ma yayi wanka ya dawo ya kwanta a kusa da ita yana cigaba da shafata a haka shi ma bacci ya kwashe shi.
*'BANGAREN SALIS🤗*
Kamar yadda Abba ya ce zai kai Nihal Asibitin haka kuwa a ka yi da ya je yayi wa Hajiya Mama bayani ba ta k'i ba, dan kuwa yanzu ta san Mama ta yi nadamar abin da tayi wa Nihal d'in, haka Nihal su ka yi sallama da su Khadijatullahi, ta bi bayan Abba suka bar gidan tana jin kewar 'yan uwan na ta a cikin zuciyarta, su na isa asibitin Abba ya fito daga motar ita ma ta fito Abba ya huce gaba tana bin sa a baya har suka isa cikin d'akin, Baffa da Mama duk suna d'akin Nihal ta tsugunna har k'asa ta gaisar da su, sannan ta sami wajen kusa da Mama ta zauna, Mama da Abba suka gaisa da Abba cikin mutunta juna Abba yayi musu ya me jiki su ka amsa masa da cewa "Da sauk'i" Suka d'an tab'a hira daga nan Abba yayi musu sallama ya nufi hanyar fita daga asibitin Baffa sai da ya taka masa har gaban motarsa sannan ya dawo, ya tarar da Mama ta rumgume Nihal tana kuka tana ba ta hak'uri.
Murmushi Nihal yayi tare da cewa "Haba Mama ai ke d'in kamar mahaifiyata ce dan haka, wallahi ni ban ji haushin abin da ki ka yi min ba, kuma ki daina ba ni hak'uri, dan ba na so kin ji Mamana" Ita ma murmushin ta yi sannan ta d'ago Nihal d'in tana murmushi tare da cewa "Nagode sosai yarinyata" Fita Mama da Baffa su ka yi daga d'akin dan su ba wa Nihal d'in damar ganin Mijin na ta, ai kuwa abin Mamaki Mama su na fita Salis ya mik'e zaune tare da kashewa Nihal ido yana murmushi "Babyn baby ya kika ga wannan drama" Zaro ido Nihal tayi tana k'arewa Salis d'in kallo zuciyarta fal mamaki "kenan Salis k'aryar rashin lafiya yayi dan ta dawo" Nihal dariya tayi tare da cewa "Gaskiya babyna wannan drama tana da abin burgewa amman kuma sauran kad'an zuciyata ta buga" Dirowa yayi daga kan gadon ya tako har gurin da take yana cewa "Ai kuwa gwanda da ba ta buga ba, domin babynki yana lafiya ya ji sauk'i fiye da yadda kike tunani kawai wannan wani wasan kwaikwayo na yi tare da taimakon su Dr Maryam dan ki dawo gareni" Janyo shi tayi tare da kissing d'insa a goshi tana cewa "gaskiya Baby ina sonka da yawa ba ka ji dad'in da na ji ba, da muka k'ara kasancewa tare da juna dan har na fitar da ran sake zama da kai darling" Ta k'arasa maganar hawaye na zuba daga idanuwanta.
Goge mata ya shiga yi tare da gaya mata kalamai masu dad'i da kwanta da zuciya har ta yi shuru sai kuma ta kallesa tana murmushi ta ce "yanzu baby meye abu na gaba da za mu yi, dan gaskiya ya kamata ka warke haka" Tayi maganar tana dariya, dariyar yayi mishi sannan ya ce "zuwa gobe zan warke daga d'aya kuma za'a sallame mu kamar yadda mu ka tsara da su Dr Maryam, "Allah ya kaimu babyna" Ya amsa da "Amin" daga nan suka cigaba da hirar soyayyar su zuciyoyinsu cike da farin ciki.
*'BANGAREN JABIR😂*
Amatullahi irin yadda take bibiyar Jabir ko mahaifiyarsa Hajiya Asiya ba ta yi masa, dan kuwa duk guraren da ya ke zuwa sai da ta bincikosu kuma duk motsin da yake yi tana sane dashi dan kuwa ya d'auki aniyyar d'aukarwa Khadijatullahi fansar abin da yayi mata sai ta tabbatar da wulak'antasa ta hana shi sukuni, tana shiga gidan ta tarar da abin da ya bata tsoro Inna Larai ta gani tare da Malam d'an ladi mai guga sun fito daga d'akin Inna Larai wani irin ihu ta fasa tare da fita waje ta tsaya dai-dai kofar gidan tana cigaba da kurma ihu, ai kuwa mutane su ka yi kanta suna tambayarta meya faru? "Inna Larai da Malam d'an Ladi mai guga na gani sun fito daga d'aki" Ta yi maganar tana kuka, ai kuwa nan jama'a su ka shiga gidan suka tarar da su Inna Larai da Malam d'an Ladi a tsaye duk sun rud'e dan sun san yau asirinsu ya gama tonuwa, dukan Malam d'an Ladi suka shiga yi ba ji ba gani, Inna Larai ta shige d'aki tare da kulle kofar tana kuka.
Amatullahi kuwa wayar wani Adamu ta ara ta kira Mahaifinta ba fad'a masa komai ba bu abin da ta b'oye masa, hankalinsa ya tashi anan take ya ce ta ba wa Inna Larai ta ce ai ta shiga d'aki ta kulle ya ce to ki ce mata ta gaggauta fitar min daga gida na saketa saki uku, ba na buk'atar sa ke ganinta, a rayuwata yana gama fad'ar haka ya kashe wayar zuciyarsa na yi masa zafi, Adamu ta ba wa wayarsa tare da shiga gidan dan kuwa ba za ta bar Inna Larai ta k'ara ko da minti biyar ba a gidan, d'akinta ta nufa ta d'auko wani k'arfe mai tsini sannan ta nufi d'akin Inna Larai tana buga kofar d'akin da k'arfi tare da cewa "to tsinanniya tsohuwar 'yar bariki ki bud'e kofar nan ki bar mana gida dan Babana ya sake ki saki uku, sai ki je ki cigaba da yin karuwancin na ki a chan wani gurin amman ba'a gidan nan ba" Tana magana tana buga kofar kuma irin bugun da ta ke yi wa kofar ba na wasa ba ne, Inna Larai jin abin da Amatullahi ta ce ta fashe da kuka tare da saka kayanta a buhu ta bud'e kofar dan ta san halin Amatullahi ba ta k'i ta k'arya kofar ba kuma ta yi mata rashin mutunci.
Hanyar fita daga gidan Inna Larai ta nufa tana jin kunyar kanta saboda irin mugayen maganganun da 'yan unguwar ta su suke fad'a mata Amatullahi ta bi ta a baya tana zungurarta da k'arfen tana cewa "Allah ya ra ka taki gona, sai a bi wani sarkin ba dai Yarima ba" Jama'a Unguwar kuwa bayan sun gama yi wa Malam d'an Ladi duka suka cukumeshi sau police station, Amatullahi ta ja kofar gidan ta mukulle da mukulli sannan ta nufi gidan Hajiya Mama ranta fas, dan kuma a rana d'aya ta jefi tsuntsu biyu da dutse d'aya.
*'BANGAREN HAFSA, SAFWAN DA SAFNA😉*
A yau aka saka ranar Safwan da Hafsa wata hud'u aka saka, ta kira Shahida ta fad'a mata sannan ta ce ta fad'awa su bestynta, Shahida ta yi mata murna tare da yi mata Allah ya sanya Alkhairin Hafsa ta amsa da Amin, daga nan suka kashe wayar, tana ajiye wayar ko minti biyar ba'a yi ba wayar ta shiga ruri da sauri ta d'auki wayar tare da kallom screen d'in wayar Hayatee ta gani murmushi tayi tare da d'aga wayar ta kara a kunne tare da cewa "Assalamu alaikum Yayana" Daga chan b'angaren Safwan wanda yake cikin office d'in ya ce "Wa'alaikumussalam Amaryata" Rufe fuskarta Hafsa ta yi kamar yana ganinta ba tare da ta ce komai ba, Safwan yayi ta tsokanarta, amman Hafsa yau kam ba ta biye masa ba, dan wata iriyar kunyarsa take ji dan har ba ta so ya zo dan ba za ta iya fita ba, a haka dai suka d'an d'auki d'an lokaci suna waya daga nan suka kashe wayar.
A b'angaren Safna kuwa tun da safe take aikin kuka dan kuwa ta san rabuwarta da Safwan ta zo, saboda a cewarta idan ya auri Hafsa ya zama ba na ta ba, sai da ta ji kanta ya fara yi mata ciwo sannan ta kwanta a kan doguwar kujera wani irin bacci ne mai nauyi ya kwasheta dan kuwa daman rabonta da bacci tun shekarar jiya dan jiya yadda ta ga rana haka ta ga dare, sai wajen k'arfe 5:00pm na yamma ta farka wanka ta yi sannan ta saka wata doguwar riga pink wacce aka yi wa gaban rigar kwalliya da duwatsu manya manya, dawowa tayi ta kwanta dan kuwa bacci ne a idanuwanta baccin ne ya kwasheta.
Safwan ne ya shigo falon da sallama, idanuwansa suka sauka a kan Safna wacce take bacci fuskarta ya k'urawa ido yana jin tausayin matarta sa ganin yadda fuskarta ta kumbura fuskarta tayi jajawur, k'arasa yayi kusa da ita tare da shafar fuskarta a hankali "Ruhina" Ya kira sunanta a hankali jin ba ta farka ba yasa ya d'auketa cak ya kai ta kan gado ya kwanta da ita, toilet ya shiga shi ma yayi wanka ya dawo ya kwanta a kusa da ita yana cigaba da shafata a haka shi ma bacci ya kwashe shi.
*'BANGAREN SALIS🤗*
Kamar yadda Abba ya ce zai kai Nihal Asibitin haka kuwa a ka yi da ya je yayi wa Hajiya Mama bayani ba ta k'i ba, dan kuwa yanzu ta san Mama ta yi nadamar abin da tayi wa Nihal d'in, haka Nihal su ka yi sallama da su Khadijatullahi, ta bi bayan Abba suka bar gidan tana jin kewar 'yan uwan na ta a cikin zuciyarta, su na isa asibitin Abba ya fito daga motar ita ma ta fito Abba ya huce gaba tana bin sa a baya har suka isa cikin d'akin, Baffa da Mama duk suna d'akin Nihal ta tsugunna har k'asa ta gaisar da su, sannan ta sami wajen kusa da Mama ta zauna, Mama da Abba suka gaisa da Abba cikin mutunta juna Abba yayi musu ya me jiki su ka amsa masa da cewa "Da sauk'i" Suka d'an tab'a hira daga nan Abba yayi musu sallama ya nufi hanyar fita daga asibitin Baffa sai da ya taka masa har gaban motarsa sannan ya dawo, ya tarar da Mama ta rumgume Nihal tana kuka tana ba ta hak'uri.
Murmushi Nihal yayi tare da cewa "Haba Mama ai ke d'in kamar mahaifiyata ce dan haka, wallahi ni ban ji haushin abin da ki ka yi min ba, kuma ki daina ba ni hak'uri, dan ba na so kin ji Mamana" Ita ma murmushin ta yi sannan ta d'ago Nihal d'in tana murmushi tare da cewa "Nagode sosai yarinyata" Fita Mama da Baffa su ka yi daga d'akin dan su ba wa Nihal d'in damar ganin Mijin na ta, ai kuwa abin Mamaki Mama su na fita Salis ya mik'e zaune tare da kashewa Nihal ido yana murmushi "Babyn baby ya kika ga wannan drama" Zaro ido Nihal tayi tana k'arewa Salis d'in kallo zuciyarta fal mamaki "kenan Salis k'aryar rashin lafiya yayi dan ta dawo" Nihal dariya tayi tare da cewa "Gaskiya babyna wannan drama tana da abin burgewa amman kuma sauran kad'an zuciyata ta buga" Dirowa yayi daga kan gadon ya tako har gurin da take yana cewa "Ai kuwa gwanda da ba ta buga ba, domin babynki yana lafiya ya ji sauk'i fiye da yadda kike tunani kawai wannan wani wasan kwaikwayo na yi tare da taimakon su Dr Maryam dan ki dawo gareni" Janyo shi tayi tare da kissing d'insa a goshi tana cewa "gaskiya Baby ina sonka da yawa ba ka ji dad'in da na ji ba, da muka k'ara kasancewa tare da juna dan har na fitar da ran sake zama da kai darling" Ta k'arasa maganar hawaye na zuba daga idanuwanta.
Goge mata ya shiga yi tare da gaya mata kalamai masu dad'i da kwanta da zuciya har ta yi shuru sai kuma ta kallesa tana murmushi ta ce "yanzu baby meye abu na gaba da za mu yi, dan gaskiya ya kamata ka warke haka" Tayi maganar tana dariya, dariyar yayi mishi sannan ya ce "zuwa gobe zan warke daga d'aya kuma za'a sallame mu kamar yadda mu ka tsara da su Dr Maryam, "Allah ya kaimu babyna" Ya amsa da "Amin" daga nan suka cigaba da hirar soyayyar su zuciyoyinsu cike da farin ciki.
*'BANGAREN JABIR😂*