← Book details Ciki Da Gaskiya Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 29 OF 83

Sashe 29

Ciki Da Gaskiya Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Sosai hankalinsa nakan aikin dayakeyi, ta ajiye tiren kusadashi, ahankali tace, "bismillah".
Batareda ya kalletaba yace, "zauna anan ki d'ora bisa cinyarki, yay maganar yana nuna mata gefensa, dayake akan doguwar kujera yake zaune.
Bayanda zatayi dole ta zauna kamar yanda yace, yanzuma bai kalletaba yace, ''saiki ciyar dani, Aramawa kura aniyarta".
Idanu Aysha tazaro waje, sannan tace, ''wayyo ya khaleel, nifa....nifa wlhy"....
Juyowa yayi yana kallonta, saita kasa cigaba da maganar, yajanye idonsa yamaida kan laptop d'in, "ashe babu dad'i ke nake baki kici, oya maza kan aikinki, kuma banda k'atuwar lauma".
"Nifa na k'oshi, tayi maganar a shagwa6e".
Yata6e bakinsa, "hummm, kuma bazai hanani abinda nayi niyyaba ba, gwamma kicima kisan cikikayi kika biya".
Dama abinda take gudu kenan, taci Kazan yace kuma saita biyashi kamar ranar.
Jin tayi shiru yajuyo ya kalleta, dariya tabashi yanda tayi wani kwale-kwale da idanu, aransa yace, " sai tsiwa ga tsoro". Afili kuma yace, ''infa tahuce yazama sau biyu kenan, kuma babu k'oraf.......".
......aibama tabari yakai k'arshen maganarba, tad'ibo Takawo bakinsa.....
"Hhm, d'uran k'arfi zakimin?".
"wlhy kaifa ya khaleel d'inan........
Tayi shiru takasa k'arasawa.
"Nifa ya khaleel me?, dukdai yanda kikai dani, haka zanyi dake agado, garama kibini a sannu ehe, kuma kidaina cemin wani ya khaleel, daga yau *_Sadauki!_* nakeso.
Idon aysha yacika da kwallah, danjin wannan k'arfa-k'arfa, itadai addu'arta ALLAH yasa wasa yakeyi, ba irin abun shekaran jiya yake nufin mataba".
Haka tacigaba dabashi naman abaki ahankali, shikuma yanata aikinsa a laptop hankali kwance, yayinda ak'asan zuciyarsa yakejin wani nishad'i da sarauta, yana lura da Aysha ko sau d'aya bataci namanba.
Dariya yayi a zuciyarsa, yana tunanin dama akwai abinda zai tsoratar da Aysha haka harta iya danne kwad'ayinta? Dan yaga ko ice-cream bata kallaba, baice da ita k'alaba, har saida ya tabbatar ya k'oshi sannan yace, "Alhmdllh dainamin d'ura hakanan, karna kasa sunnah anjima".
Ita bamata fahimci Inda zancensa ya dosaba, tamik'e zata maida kayan kichin yace, "dawo aii ba'a gamaba".
Dawowatayi tazauna, duk tsoronsa ya gama kamata, mamakinma wad'annan abubuwan dayakeyi take ita.
Kunsan Mintina 3 sannan ya ajiye laptop d'in gefe yajuyo sosai yana fuskantarta, tiren yakar6a yamaida kan cinyarsa fuskarsa k'unshe da murmushin mugunta yad'ebo naman yakai bakinta.
''ALLAH Na k'oshi ya k...... Amin Sadauki....ta canja maganar tata saboda uwar harara daya balla mata".
"Kinga gwamma ma kici, Dan babu d'aga k'afa babu alfarma, Niba cazanyi kibiyaniba aii, da zuciya d'aya nabaki".
d'ago idanunta tayi takallesa Dan tabbatar da gaskiyar maganarsa, ya jinjina mata kai yana lumshe idanu, dukda ba yandda tayi dashiba dai tabud'e bakinta ya bata, haka yayta bata naman saida yaga taci da yawa sannan ya k'yaleta.
Ruwan data kawo ya wanke hannunsa aciki, yad'auki cup yazuba fura, ita kuma yamik'a mata ice-cream yana fad'in nasan anan kikafi kauri".
Da mamakin furicinsa tace, " kamar ya?".
"Kamar yanda kika Sani, yay maganar batareda ya kalletaba, saima k'ok'arin canja tasha dayakeyi a TV, yamaida NTA domin kallon labarai.
Tunanin Aysha yafara canjawa akan ya khaleel, tafara Zargin anya kuwa baisan Wani abuba Dangane da ita?.
Ganin kallon datake masa yad'an juyo ya kalleta sannan yamaida hankalinsa kan TV, "yayadai kike kallona?, konayi wani abun mamakine?".
"A'a Aysha tafad'a tana girgiza kanta a sanyaye, daga nan babu Wanda yasake tankawa, kowa da abinda yakeyi, yanashan fura yana kallon labarai, itama tanashan ice-ceam tana kallon labaran.
Harsuka gama kallon labarai babu wata hira data kuma Shiga tsakaninsu, ya khaleel ya tattare kayansa waje d'aya, azatonta zai tashine yashiga d'aki, saitaga yazame ya kwantar da Kansa saman cinyarta.
Aysha tazaro idanu waje, amma takasa yin magana.
Shima bai tankaba, dukda yana kallon mamakinta ta gefen ido.
Canja tashar yayi yamaida wisal Hausa TV , Tafseer akeyi, hankalinsa yamaida kan tvn.
Itama Aysha saita maida hankalinta akan wa'azin.
Sai kusan 11:30pm aka kammala tafseer d'in, ya khaleel yamik'e yana fad'in Alhmdllh, Malam mungode, ALLAH yabiyaku.
Itadai Aysha batace komaiba, yakwashi kayansa yashige d'akinsa.
Itama d'an kaye-kaye tayi tashige nata d'akin.
Kowannensu yay shirin barci, hankalin Aysha kwance ta kwanta, tunda tasan ta kulle d'akinta, ko ya khaleel yayi yunk'urin shigowa babu dama.
Takuma tura key d'in k'ark'ashin filo, sannan ta gyara kwanciya tanamai jin dad'in yima ya khaleel wayo.

Nace, "hummm, aysha kenan.🤣.lol.

______________________________
Abin duniya ya ishi momy, ko barcin kirki bata iyayi, yanzuma tana zaunene shiru, gama wayarsu kenan da hajia khaltum, take sanar mata anrufe mata account d'inta, yanzunnan sak'o yashigo mata.
Momy tace, "Aminiya garin Yaya hakan tafaru kuma?".
"Wlhy bansaniba aminiya, amma insha ALLAH da safe zanje na bincika, inaga bawata matsala baceba mai yawa".
"To shikenan ALLAH ya kaimu, saidai ina miki albishir Ibrahim ya amince da auren Aleeya, nama sanar masa zuwanta k'asar".
"Alhmdllh, kinga munsami bakin zaren, yanzu saimuyima tufk'ar hanci".
"Gaskiyane aminiya".
Sunyi sallama kenan Momy tajiyo kamar motsi.
Da sauri tamik'e ta lek'a window d'inta, mufeedah ta hango sanye cikin dogon hijjabi, tana tafiya cikin sand'a a tsakanin motoci.
Gaban Momy yafad'i, dasauri tafita zuwa tsakar gidan, lokacin data fito har mufida taje k'ofar gate tana tashin d'an gwari dake gyangyad'i yabud'e mata gate.
" Dan ubanki INA zakije a darennan?".
Maganar Momy tasaka mufeedah juyowa arikice, tuni jikinta yafara 6ari, wlh...wlh....wlhy momy credit zanje Na sayo, shine nazo tashin d'an gwari yasayimin.......
Tsawa Momy tadaka mata, "kimin shiru 'Yar iskar yarinya, yanzunan mufeeda nizaki tonama asiri agidannan?, da mutuncina dakomai".
"Momy Dan ALLAH karkice haka wlhy gaskiya nafad'a mik....."
Bata k'arasaba taji saukar mari a face d'inta, da Sauri tadafe kunci Dan Marin kan yashigeta, Momy tanuna mata hanya.
Suna shiga falo ta fisge hijjabin jikin mufeeda.
Sallalallami Momy takamayi, Dan ganin tambad'ad'd'iyar shigar dake jikin mufeedah, tuni jikin Momy yafara rawa, tadafe k'irji tana layi zata fad'i, mufeeda Ce tayi azamar tarota suka fad'a saman kujera, tana kwala kiran Momy! Momy!!....
Ina Momy ta suma aii.
Ihuntane ya farkar da Anty shukurah, tafito falon cikin yanayin barci.
Idanu tazaro, tak'araso dasauri inda suke, "k mufeeda lfy? Miya faru da momyn?".
"Wlhy Anty shukurah fad'uwa tayi, dankawai taga zan fita siyen credit, tazata wani gurin zanje..
Wani kallon Anty shukurah Tamata, ahakan zakije siyen credit mufeedah? Da wannan shigar mufeedah? Kekuma wannan rayuwar kika za6ama kanki?".
"Wlhy Anty shukurah gaskiya nafad'a miki, kiyarda dani"...
"Banida wannan lokacin, kinga tashi ki tado su husnah mu kamata akaita d'aki, mu biyu bazamu iyaba''.
"Anty shukurah ko ya khaleel za'a kirane?".
"A'a bazamu tadoshiba yana cikin iyalinsa, mudai kaita d'akinta".
Mufeedah tasaka hijjab d'inta ta tado su hasnah.
Da k'yar suka d'auki Momy suka kai d'akinta, Anty shukurah ta shafa mata ruwa takawo numfashi, saidai da k'yar numfashin ke fita, sai huttai takeyi, fanka suka kunne, aka kashe ac d'in, duk suka zagayeta suna mata addu'a.
Anty shukurah dai Tahana atado ya khaleel dukda Kiran sunansa da Momy keyi ahankali.

__________________________
Cikin barci Aysha taji ana shafata, abirkice tafarka, tazabura zata tashi ya maidata, cikin kunnenta yace, "k nutsu mana nine".
Jikinta Na rawa tace, "amma ya akayi kashigo bayan Na kulle k'ofar?".
Murmushi yayi, yakuma rungumeta da k'yau, cikin kunnenta yace, " haba 'yammata, zakici kazane a banza baki biyaba?".
"Aii wlhy banciba, kaine kasakani dole naci aii, kuma ALLAH shine shaidata, cikin kuka tayi maganar".
Yanda take magana tana kuka saita bashi dariya, cikin salonsa na jarumta yadara yana mata abinda ke k'ara firgitata.
Tarik'e hannunsa tana fad'in, " naji kabari da safe zan biyaka kazarka danaci".
"Tab kinma rainani kenan, banason wata kaza, sunnah zanyi yarinya".
Yink'urin tashi tayi yamaidata da sauri yakuma matseta.

🚶🏻‍♀Sum-sum nafito dannagafa ya khaleel da gaske yakeyi, yauma kazarsa Aysha
zata biyashi.😆.lol.

*_washe gari_*

Daga masallaci ya khaleel yawuce cikin gidan, Dan tunda asuba Anty shukurah takirasa tasanar dashi momy babu lafiya, idan yayi sallah yazo suje asibiti.
Ana idar da sallar kuwa suka iso shida baffah da sauran samarin gidan.
Ba'awani 6ata lokaciba aka d'auki momy zuwa asibiti.
Suna Isa aka kar6eta da gaggawa zuwa Emergency, duk suna k'ofar d'akin da aka kwantar da ita, kowa kagani hankalinsa ba'a kwanceba, mazan kad'aine sukazo, koda Anty shukurah ba'azo asibitinba.

*************

Da k'yar Aysha tatashi tai sallah, tun dare ya khaleel ya taimaka mata ta gasa jikinta da kansa, Dan wlhy yauma tasha bak'ar wahala, azuciyarta tana mamakin masucewa aure da dad'i, ina wani dad'i anan ana azabtar damutum😢😜.
Tana idar da sallah takulle d'akinta takoma ta kwanta, batawani dad'eba barci ya d'auketa, Dan barcin bai ishetaba.
Sai around 9am tafarka, cikin hanzari ta dirgo daga gadon saboda ganin time.
Agurguje tashiga toilet tayi wanka, bata tsaya wata kwalliyaba, dama can Aysha kwalliyar tsiyarnan badamunta tayiba, doguwar riga 'Yar kanti roba-roba orange tasaka, tamata k'yau sosau, Dan duk wani Shep nata saida rigar ta fiddo, gashi kuma ta fidda ainahin colour d'inta, tasaka hula black sannan tafito falon.
Amamakinta babu kowa, d'akin ya khaleel tanufa, azatonta bai tashiba shima, saitaga wayam, tamatsa jikin toilet shiru, ''kodai yafitane inata barci?, maiybi kam yafita, ko yaje cikin gida gaidasu baffah".
Hakan Aysha ta ayyana aranta tacigaba da ikin gyaran gidan.
Tsaf ta gyara ko ina kamar yanda ta saba, saiga maleeka takawo musu breakfast, alokacinne Aysha taji momy ce babu lafiya, tanuna jimaminta agaban maleekah, gudun karta zargi wani abu.
Amma azuciya catake ALLAH yak'ara ma momy zafin dayafi wannanma🤭.
Maleekah na tafiya tazauna tayi break d'inta hankali kwance, kamarma babu wani abinda ke faruwa agidan.

Ho sholyn sadaukinta, kina aljannah ina binki da addu'ar fatan alkairi nida fans🤣👍🏻.

Har wajen 12 su baffah duk suna asibiti, amma jikin momy da sauk'i, barcima takeyi an saka mata k'arin ruwa.
Baffah yace, "duk suje gida su karya, idan sukaje saisu Shukurah su taho shima yaje gida ya shirya".
Suduka suka amsa da to.
Ya khaleel yace, " baffah kabisu kuje, idan su Anty shukurah sukazo nisana tafi".
"A'a mu'azzam kuje kawai, karka damu".
Badan yasoba ya amsa dato.
Chapter 29 · 0% Book details