← Book details Ciki Da Gaskiya Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 16 OF 83

Sashe 16

Ciki Da Gaskiya Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

___________________________.
Ya khaleel yariga Aysha tashi, saboda kiran da Taheer yamasa akan bak'ifa zasu tafi, yakamata yazo akawosu su gaisa da amarya amusu rakkiya.
A hanzarce yay wankan ya shirya cikin farin boyal mai shara-shara, Dan har best d'insa ana gani, babudai hula amma yayi k'yau, turare yafesa kad'an sannan yafito yana saka ma6allin link d'in hannun rigarsa.
d'akin Aysha yashigo da sallama, tana tsaye jikin madubi fitowarta kenan daga wanka, daga ita sai guntun towel.
Batayi zatoba taji dallamarsa kuma harya shigo, cikin rikita tafara neman abinda zata rufe jikinta.
Shima kallo d'aya yamata yakauda kansa tareda juya bayansa.
Bayan kamar Monti biyu yajuyo Dan yanada tabbacin ta kimtsa, hijjab d'in datayi sallah tasaka, yakaimata har k'asa, taduk'ar da kanta k'asa saboda kunyar ganinta dayayi ahaka.
Shima kanshi yaji wani iri, Dan hakan baita6a faruwa dashiba, ganin mace ahaka, bashiga d'akin k'annensa yakeba, bakumashi dalokacin kallace-kallecen films d'in banza, shi indai film baishafi bincike-bincikeba baya kallonsa.
"Ehhm, bara naje zamuzo dabak'i, dan zasu wuce yau".
Aysha tace, ''to, tana d'an satar kallonsa, kwalliyar tasa tamata k'yau, saidai fuskarsa babu walwala, itakam batasan randa zata fara ganin dariyarsaba".
Juyawa yayi zaifita, tace, " ALLAH ya tsare".
Ya amsa da amin ciki-ciki.
Harya kama k'ofar zai fita tace, "umh....".
Saikuma tayi shiru.
Juyowa yayi yana kallonta, alamun yana saurarenta, ganin tayi shiru yace, " kinsanfa ana jiranane".
Cikin jinjina kai tana had'iye yawu tace, "dama zancene bazaka karyaba?". 'murya a sanyaye tayi maganar'.
"Saina dawo zan karya", 'yayi maganar yana fita'.

A gaggauce yashiga ya duba Momy, amamkinsa saiya isketa ragal, tanata dannama cikinta breakfast.
" A lallai Momy sauk'i yasamu? harkinsamu kina cin abinci?".
d'an murmushi tayi tana gyara zamanta, "da sauki kam Ibraheem, jiki Alhmdllh, amma inazakaje haka kaci gayu?".
" Zanje nazo da abokainane zakuyi sallama, duk yau zasu wuce".
"To masha ALLAH, ya Aysha?".
"Lfy lau take, bara naje Momy. koma wajen baffah bazan shigaba saina dawo".
Sallama yamata yafita ad'an hanzarce.
Itakuma tasaka dariya tana fad'in Ibraheem kenan, inhar ina raye bazaka ta6a had'a shinfid'a da y'ar isakar yarinyarnanba, lafiyata k'alau, nasan bazaka ta6a biyuwa ta sauk'iba shiyyasa na 6ullo maka tahaka, damacan natsani uwarta bare ita...............✍

Nace hummm, hajia babba sai ku zuba migani keda Aysha.🤝🏻😂

Wlhy banajin dad'i, ALLAH yasama Na iya typing gobe idan ALLAH ya kaimu😥, INA buk'atar addu'arku🙏🏻.

💋💋💋💋💋💋💋💋💋😍😍😍
[9/12, 6:48 PM] Aysha Galadima: *_Typing📲_*

🤰🏻
*_CIKI DA GASKIYA........_*
_{🔪wuk'a bata hudashi🗡}_

*_Bilyn Abdull ce🤙🏻_*

*_HASKE WRITERS ASSOCIATION_*
_~Home of experts and perfect writers~_

*_Sadaukarwa_*
_My sweet dady_
~(ALLAH ya gafarta maka)~
🤲🏻😭

*_part 2_*
(littafi na biyu📕)

1⃣2⃣

Yana fita Aysha tasauke ajiyar zuciya, hijjabin jikinta tacire tayi simple kwalliya, tasaka siket da riga Na atanfa, kayan sunmata k'yau sosai, amma ita kokad'an bawani tadamu da sawar baneba, saboda gargad'in da mama tamatane kawai take kiyayewa.
d'akinta tagyara tsaf, tasaka turare sannan tanufi falo shimadai gyaran kad'an tamasa tasaka turaren, tayi mamakin rashin ganin kayan abincin jiya, aranta tace, "k'ila ya khaleel ne yad'auke".
Harta nufi hanyar kicin taji ana Knock d'in k'ofa, tajuyo dabaya danufin dubawa ya khaleel yashigo da sallama, Aysha ta amsa kanta ak'asa.
d'an nesa da ita yatsaya, idonsa kyam akanta, saidai fuskar haryanzu babu walwala. yace, "tarenake da bak'i, kinzo kin tsayamin akai, kije kisaka hijjab zasu shigo".
Haushine ya kama Aysha, batasan ta murgud'a masa bakibama, tawuce tana k'unk'uni batareda yaji mitake cewaba, ransane yad'an sosu, amma saiya danne yayimusu iso zuwa ciki, Dama suna bakin k'ofane tsaye.
Masifa natacin Aysha a zuciya tana d'akko hijjab a wardrob tana tsogumin yanda halayen ya khaleel yake, shidai bazai ta6a kuyi magana mai dad'iba dashi, to yaushema yasakema mutane fuska, itafa gaskiya bazata iya wannan rayuwarba.....
Tajiyo bayan tad'akko hijjab d'in danufin rufe wardrobe d'in taji tabuge Abu, ad'an figice tawaigo dansan ganin minene?. Bak'aramar fad'uwa gabanta yayiba ganin ya khaleel tsaye abayanta, kokad'an bataji alamar shigowarsaba.
"Zan.....zan wu wuce".
Tayi maganar cikin in ina da rawar baki, jikinta sai tsuma yakeyi.
Bai motsaba, kuma bai tanka mataba, fuskarnan babu alamar sauk'i.
Hakan yak'ara saka Aysha cikin tsoro, tatura murfin wardrobe d'in tareda jingina ajiki, idanunta Na kallon k'asa tana k'arema yatsun k'afafunsa kallo. Yayinda shikuma itad'in yake k'arema kallo, baita6a damuwa da kallon ya Aysha takeba a can baya, amma ayanzu saiya samu kansa dabin halittar jikinta da kallo daki-daki.
Kad'an tad'ago ido ta kalleshi, ganin kallon k'urillar dayake matane tayi saurin saka hijjab d'inta.
Yalumshe manyan idanunsa yana kauda kansa, Aysha tara6a ta gefensa zata wuce cikin d'ari-d'ari.
Da sauri yaruk'o hannunta, cikin Aysha yabada k'ululu!..
"dawo magana zamuyi".
Jiki a sanyaye tadawo baya, kafin yace wani Abu wayarsa tafara ring.
Cirota yayi yaduba, taheer ne, batareda yad'agaba yasaki hannun Aysha yanufi k'ofa, saida yabud'e sannan yace, "kizo Ku gaisa, zasu tafine, sannan kitanaji bayanin dazaki Kare kanki akan murgud'amin Baki dakikayi". 'Baijira cewartaba yafice abinsa'.
Bak'aramin rud'u Aysha tashigaba, itama tasan hakan ba daidai baneba, amma wlhy rantane bayason dizgin dayake mata.
Jiki a sanyaye tabi bayansa, gudun karta k'ara wani laifin.
Sannu da zuwa tamusu tanufi kichin, sukuma suna tsokanar ya khaleel d'in, wai daga kira yayi bulum ad'aki, miyakeyi?.
Tsaki yayi yana hararsu, yaxauna a kujera yana ''fad'in duk abinda zuciyarku tabaku shi Ibraheem khaleel yakeyi".
Dariya sosai suka Sanya masa da shak'iyanci irinnan abokai. Ayaha tafito daga kichin d'aukeda babban tire dake cikeda drinks, ta ajiye a tsakkiyar falon takoma, babu dad'ewa tadawo da snacks, ta ajiye takoma tad'akko glass cups, duk suka mata sannu.
Cikin kunya take amsawa, anutse tagaishesu, duk sun yaba da ayshan, harsuna taya abokinsu burna azukatansu, sunta tsokanarta irinnan abokan miji, bata iya cewa komai saidai murmushi.
Ya khaleel kam saima karantse baya falon, waya yaketa dannawa batareda saka bakinsa a zancensuba.
Aysha tamik'e tabar musu falon dansu d'an ci abinda ta ajiye musu.
Shigarta d'akinta da y'an mintuna saiga anty glo...da kubrah, saida suka gaisa dasu ya khaleel afalo sannan suka shigo, bisa umarnin ya khaleel d'in.
Zumbur Aysha tamik'e daga bakin gadon, Dan batayi zaton ganinsuba.
Anty glo tashek'e da dariya tana "fad'in sholy amarsun ango, Ashe dama tsoron john Na k'aryane kikeyi, koda yake naga kinzama y'ammata, ina Antyan taki meerah?".
Amamakinsu sai sukaga Aysha tayi murmushi, takoma bakin gadon ta zauna tana musu wani kallon rainin hankali, "mtsowww! Wlhy ku kama kanku, kenaga kanki rawa yakeyi glory!, inaga dai k'awar taki bata sanar dake wanene mijin nawaba ko? Karfa wajen tone tonen kaza, tatono wuk'ar yanka kanta".
Kubra tabud'e baki zatayi magana kenan ya khaleel yaturo k'ofar ya shigo, kallo yabisu dashi su duka, glory da kubrah sund'anji shock da shigowar tasa, Aysha kam ko'a kwalar rigarta, Dan zuwa yanzu batak'i komai ya 6aciba.
Ko kallo su kubra basu isheshiba, yace, ''taso kuyi sallama zasu tafi".
Aysha tamik'e itama batareda ta kalli su kubra d'inba tanufi k'ofa.
Ganin haka suma dole sukabi bayanta, bak'aramin Sosa ransu lamarin yayiba, suna mamkin yaushe Ayshan tawaye har haka? Lallai hajia laura kallon baibai takema Aysha, kuma dolene sud'auki mataki akan Aysha da meerah, Dan zasu 6allo musu ruwane.

Bayan tafiyarsu glory da abokan ya khaleel, mutanen Kano sukazo mata sallama, kowa dai yak'ara mata nasiha, gayyar ciki da gaskiya fans ma sunzo sallama, cikin mutunci Aysha ta kar6esu, ko'ina sun zagaya a gidanna Aysha, sannan suka mata sallama suka tafi, harda 'yan kwallanta kuwa, acikin fans d'in ciki da gaskiya kuwa wasu basuso tafiyaba😂🤧😜.
Amma na tusa k'eyarsu gudun samun matsala,🤣, karsu ragema ya khaleel jin dad'i💺😏🤧kundai gane😉.

To Alhmdllh bak'i sunyi halin ruwa, gida yayi tsit, saisu Anty zuwairah da y'ay'ansu kawai.

______________________________
Har 4 ya khaleel bai shigoba, Aysha tad'an damu, ko breakfast baiyiba, Na ranama da Anty Mamie ta aiko itakad'ai taci.
Yanzu haka saboda bak'in daketa kara kaina shiyyasa yak'i shigowa.
Bayan tayi sallar la'asar takuma gyara ko ina da'aka 6ata, gidan yad'auki k'amshi, babu wuta gakuma babu Wanda yashigo, ta zauna shiru tana tunanin ina ya khaleel yashiga? Tundaga rakkiyar 6ak'ifa.
Jitayi ana Knocking d'in k'ofa, tamik'e a d'arare taje tabud'e, su Tasleem ne d'aukeda abinci, rungume juna sukayi Dan duk yau bata gansuba.
Suka shiga tsokanarta matar yaya matar Yaya.
Nandai suka zauna sunata hirarsu, ananma suke bata labarin soyayyar tasleem da maheer, maleeka da shakur, sosai Aysha tayi farinciki.
Suna cikin hirar ya khaleel yashigo.
Kowa yay tsit, suka shiga gaisheshi da sannu da zuwa.
Bayabo babu fallasa ya amsa tareda nufar d'akinsa.
Su Tasleem suka mik'e, rok'onsu Aysha tashigayi akan su zauna, basu sauraretaba suka gudu.
Tarasa miya dace tayi?, tana nan zaune inda suka barta ya khaleel yafito, ya sauya kayansa zuwa jallabiya blue black, ya zauna afalon bisa 2sita, tareda ajiye system d'insa dake hannunsa da wayoyi.
Mik'ewa Aysha tayi tashiga kichin, yabita da kallo a munafunce.
Bata dad'eba tafito d'aukeda k'aramin tire, tad'oro ruwa da cup, sai drink.
Harya kunna system d'insa yafara aiki, da'alama aikin mai muhimmancine, kuma yazo masa a gaggaucene, ruwa Aysha tafara zuba masa, ya kar6a hankalinsa nakan aikinsa, saida yasha ya ajiye cup d'in sannan yad'an d'ago ido yakalli Ayshan, kallon dabaifi second4 ba yamata yajanye idonsa, "wazai gyaramin d'aki?", 'Yay maganar murya adake'.
Kunyace takama Aysha, Dan yakamata ace tunda safe tashiga ta gyara, to amma tsoron dizginsa takeyi, murya a sanyaye tace, ''kayi hak'uri, wlhy bak'ine sukamin yawa, amma zan gyara yanzu, sannan ga abinci, naga ko break fast bakayiba kafita".
Baice da ita uffanba, saima k'ok'arin amsa call yakeyi, "hello Joseph!, yawwa nagani, amma yakamata kunema mana bayanai akan Ak'ilu Abbas d'innan, Dan banyarda dashiba, idan kanutsu akan zancensa akwai kalamai masu kama da rashin gaskiya, ina Hutu amma tilas gobe idan ALLAH ya kaimu nafito aiiki, Dan zankama Lazarus da kainane".
"OK babu damuwa, kausar da fharuk sumin binciken asusun bankinsa, inason bayanai kuma akan hajiar data tura massege wa Barau modibbo, awaccan ranar".
Chapter 16 · 0% Book details