← Book details Ciki Da Gaskiya Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 22 OF 83

Sashe 22

Ciki Da Gaskiya Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Su gwaska kam nacan suna nazarin yanda zasu Shiga gidan, d'aya daga cikinsu yana gwada wani d'an k'arfe a k'ofar falonsu kozai bud'e, cikin ikon ALLAH kuwa k'arfen yabud'e k'ofar falon su Aysha.
Dad'ine yacikashi, ya dunk'ule hannu yana fad'in yeees!.
Jin haka Wanda ke a kusadashi yamatso yana tambayarsa tabud'e?, yace Masa eh tabud'e.
Zagayawa yayi domin sanar dasu gwaska, shikuma d'ayan yashiga cikin falon.

Hankalin Aysha yayi masifar tashi, Dan batasan dami mutanene sukazoba, amma amamakinta saitaga ya khaleel ta Kansa kawai yakeyi bawai damuwa da mutanenba, Dan haryanzu yana manne da jikinta, data yunk'ura danta tashi zaice please karki barni, sanyi nakeji, Abu goma da ashirin inji Aysha.
Motsi sukafaraji alamun ana ta6a k'ofar d'akin, amma anjita GAM a kulle, sunata k'ok'arin sakab. k'arfennan dansu bud'e amma sun kasa, saboda key d'in yana ajiki ya khaleel bai zareba.
A tsorace Aysha tace, "ya khaleel zasu shigofa, Dan ALLAH katashi, wlhy k'ila kashemu zasuyi".
Tabashi tausayi, amma bashida k'arfin tunkarar kowa awannan yanayin dayake ciki, shikad'ai yasan halin dayake ciki, baita6a tsintar kansa acikin wannan halin ciwonba tunda yay wayo, yasandai yana ciwo, tunda yasha kwanciyama a asibiti, amma baita6a jin mai azaba irin wannanba, gabad'aya ga6o6in jikinsa kwankwatsa sukeyi, ga bala'in sanyin dayakeji.
Ahankali yace, "ki kwantar da hankalinki gasu Adams nan zuwa, bazasu iya bud'e k'ofarnanba saboda akwai key aciki, kibar kuka".
''Ya khaleel idan suka 6allafa?".
Shiru yayi yakasa bata amsa, ana cikin haka sukajiyo alamar ana dukan Abu, ya khaleel ya sauke ajiyar zuciya, Dan yasan su Adams sun iso, magana suke jiyowa sama-sama.
Su Adams ne suke dakama su gwaska tsawa, bayan sun tattaresu waje d'aya, katafila ne zaimusu gaddama Samuel ya dakesa, shine su Aysha sukajiyo.
Su Samuel suka tasa k'eyar su gwaska zuwa waje, mamaki yakama Adams ina ogan nasu yashiga haka? Har wawayennan suka shigarmasa gida?, gashi yaji maganarsa kamar a mawuyacin hali d'azun daya kirasa, tomeke faruwane?. wayarsa yad'auka yakirashi.
Ya khaleel yad'auka murya a dakushe yace, " Adams kunzone?".
"Ye sir, harma mun kamasu, amma kana inane?".
Da k'yar yace, " inan ad'aki kwance banida lfy, kuje dasu kawai, saida safe idan naga yanda natashi zan shigo".
"Oga kodai akira doctor k muje asibiti?, nake ganin baikamata kazauna cikin ciwoba".
" karka damu kuje, da safe zan kira Dr Abraham".
Badan Adams yasoba yace, "to shikenan Oga, ALLAH yak'ara afuwa".
"Ameen". ya khaleel ya amsa yana yanke wayar.

_______________________________
Haka suka kwana suduka babu mai isashshiyar lfy, duk agalabaice suka wayi gari, da k'yar ya khaleel ya iya raba jikinsa dana Aysha dake barci a wahalce itama, yana layi ahanya ya Isa toilet d'in, cikin dauriya yahad'a ruwa maid'an zafi yayi wanka tareda wankan tsarki, wani ruwan yakuma had'awa sannan yafito, yad'anji k'arfi ajikinsa, amma haryanzu zazza6in yana nan, kuma yanajin sanyi sosai, jallabiya yasaka da rigar sanyi mai kauri, ya dogara yay sallar Asubahi a d'akin, Dan bazai iya fita konan da tsakar gidaba.
Bakin gadon ya zauna yana cije la66a, idonsa nakan k'yak'yawan face d'in Aysha dake barci, dagani batajin dad'in barcin, yasan dukda wahalarnan dayake aciki tafisa, Dan bak'aramin wahalar da ita yayiba, kasa control d'in kansa yayima shi gabad'aya wlhy.
Ya lumshe idanunsa dake jajur sannan yabud'e akan Aysha, hannu yakai ya yaye bargon, Aysha tabud'e ido, kallo d'aya tamasa tamaida ta rufe saboda kunya.
Huci ya furzo a bakinsa, yad'an huro hancinsa alamun baya jin dad'in jikinsa, yace, "zaki iya tashine A'eesha?".
Shiru Aysha tayi masa, amma tad'aga kanta.
"Daure to kitashi kiyi wanka, kar lokacin sallah yashige", dagaji kasan a wahalce yake maganar.
Cikin zubda kwallah tace, " to kabani hijjab d'in nasaka".
Hijjab d'in yatashi da k'yar ya d'akko akan sofa, yamik'a mata, tana a kwancen tasaka, ta yink'ura zata tashi, amma azabar zafin dataji yasakata fad'in ya sallamm!!.
Tausayi tabashi, dukda jikinsa babu k'arfi haka yad'auketa cak yanufi bayin da ita, Aysha kasa bud'e ido tayi ta kallesa, ya direta, karki cutar da kanki, kishiga ruwan zafi sosai, zakiji sauk'in zafin kafin doctor yazo.
Kanta ta iya gyad'a masa kawai, amma takasa amasawa da baki.
Fitowa yayi, yacire bargon saman gadon, sannan ya cire bedsheets d'in gaba d'aya, ya nannad'eshi waje d'aya ya ajiye, wani bedsheets d'in yad'ako ya shimfid'a, batareda tsayawa wani gyarawaba ya haye yakwanta, ya k'udundune cikin bargo.
Aysha kam tanacan tashiga ruwan zafi, jin zafi yaratsata tamik'e zaram, kuma d'ibar ruwan sanyi tayi ta surka ruwan, zafin ya salamce, ahaka tashiga, shima batawani dad'eba tafita tayi wankan tsarki.
Fitowa tayi tana tafiya kamar wata y'ar kac.....🤭.
Saboda bata gasa jikin da k'yauba.
Ganinsa kwance yasakata ficewa daga d'akin, tanufi d'akinta, a can ta sauya kaya sannan tayi sallah a daddafe takoma kan gado ta kwanta.

Ya khaleel yanajin fitar Aysha, tun yana sauraren dawowarta harya fidda rai, yanda tafito daga bayin dawuri ya tabbatar masa batawani tsaya Gasa jikinta da k'yauba, yasan zata sha wahalane, saboda jikinta zai k'ara tsami, amma bashida wani k'arfin taimakonta.
Waya ya d'auka yakira doctor Abraham, dukda likitansune ta fannin aiki ya yarda dashi, duk wata Matsala ta ciwo Indai zata taso masa shi yake nema.
Babu dad'ewa kuwa saiga Dr Abraham d'in, ashema Adams ya Sanar masa yazo tunda Asubahi, Dan haka ya khaleel yay mamakin zuwan nasa da wuri.
Kwatancen d'akin yamasa yashigo, ya khaleel Na kwance suka gaisa, yace, "ashema kana kusa Na kiraka?".
" yes sir!, dama Adams ya sanarmin tun d'azun, nad'an dakatane gari Yakuma haske nazo, INA kan hanyar zuwama kakirani".
Ya khaleel ya jinjina kai yana lumshe idanu.
Bai 6oyema Dr Abraham ba, yasanar masa abinda yakawo ciwon.
Sorry sir, inaga ka Tara sha'awane shiyyasa, kadad'e kana buk'atar mace amma Baka d'auki wani matakiba akai, shiyyasa yau daka fidda (S) Ya haddasa maka da zazza6i da jin sanyi, sometimes irin hakan yana faruwa, idan mutum yakai age d'in buk'atar mace amma baiyi hakanba, sai (s) yarink'a taruwa amararsa, yakan haddasa masa yawan mantuwa, 6acin rai, ciwonkai, so duk randa yasamu damar fitarwar saikaga kuma ciwo mai tsanani ya sameshi, kamardai yanda katsinci kanka aciki, please Oga akiyaye gaskiya, Dan hakan had'arine ga lafiyar Dan adam".
Jin Nina kai ya khaleel yayi yana fad'in "OK doctor insha ALLAH".
Allura yamasa, sannan yabashi magunguna.
Ya khaleel yace, "itama yakamata kad'an bata magani, dannanga kamar zazza6inne ajikinta".
"OK sir! Amma ita NATA ba damuwa baneba sosai, gajiyace darashin sabo, tasha wannan maganin insha ALLAH zatajita normal".
"Amma yakamata kusha koda tea ne yanzu kafin kusha maganin, musamman kai da akama allura, Dan tanada k'arfi".
"Babu damuwa doctor, ngd sosai".
Sallama Dr Abraham yayi masa yatafi.

Tunani yafarayi akan waya kamata yakira danya taimaka masa akan Aysha, yakamata yasamu mai tsayawa akanta danta Gasa jikinta, Inda Anty zuwairah mutuniyar kirkice ai saiya kirasa, tunda dai y'ar uwarsace, kuma yayarsa, yaja guntun tsaki, garama yakira anty shukrah ko Amatullah.
Amatullah k'anwarsace, bara kawai yakira Anty shukurah d'in, tunda yaga ita halinta ya banbanta da su Anty zuwairah.
Harya fara nemanta saikuma yadakata, wani tunanine yazo masa, kodai yakira Ammah, Dan ita kakarsuce, akwai d'an k'arancin jin nauyinta tartare dasu, yanda zai iya fad'a mata damuwarsa itada Anty Mamie ko momy bazai iya fad'awaba.
Gaskiya kuma yanajin kunyar Anty Mamie matuk'a, Anty shukurah d'inma saiyaji kamar da kunya, garadai Ammah, dukda itama yanajin kunyar tata Amman dad'an sauk'i akan sauran.
Wayar Ammah yakira, bugu d'aya kuwa ta d'auka.
"Iro! Injidai lfy?".
Bayason iro d'inan, amma babu yanda zaiyi da Ammah, murya a tausashe yace please Ammah kid'anzo mana".
''Kaini kamin magana da yaren dazan gane, miye wani falis koma uwarmi kace?".
Dukda halin dayake ciki saida ya murmusa, aransa yace, " Ammah jaraba kenan, afili kuma yace, "to yi hak'uri, kizo bamuda lfy muduka".
Subahanalilahi, to ganin zuwa, aidama inada shirin lek'oku yau, amma dakam sai anjima, to amma ganina yanzu.
To saikinzo.

___________________________
Hhhhhh🤣, momy dai har Around 7am bata farkaba, tanata kwasar barci, babu Wanda yatada ita, su azatonsuma tatshi tayi sallar Asubahi takoma barcinne, basusan hajia momy ko motsima batayiba😆.
(Aikin amma yayi k'yau😂👍🏻).

__________________________
Har barci yafara figar ya khaleel yajiyo Ammah Na kwad'a sallama daga falo, bai iya amsa mataba, Dan bashida k'arfin hakan.
Jiyota yayi tana fad'in "yoni halima ina kuke y'ay'annan?, yad'an murmusa yana gyara kwanciyarsa, can saiya jiyo ta turo k'ofar d'akinsa, talek'o kanta, saida ta hangoshi sannan ta ida shigowa, "o, kajimin d'an nema, iro dama kanajina inata kwad'a sallama amma kamin banza?".
Yi hak'uri Ammah, banida k'arfin amsa mikine".
''Wayyo, to sannu, ina ita Aysha d'in?, tun d'azun tafita, inaga tana d'akinta kwance".
''To ALLAH ya sauwak'a", tad'auki maganin tana dubawa, kaikace tasan mi'aka rubuta, cikin tsokana ya khaleel yace, " Ammah kina karantawane?".
Ta ta6e baki, "yoni iro minasani a wannan shirmen?, to wayazo yabaku magani kuma? Kotun jiyane ciwon?".
" A'a Ammah, yanzu doctor yatafi, yamin allura, yacene nasha tea da Sauri saboda allurar tanada k'arfi, ita kuma tasha wannan maganin".
''To bara na had'a maka shayin, amma ni halima nata6a ganin ciwo da salo, kakama mata kakama miji, iro wai miyema yasamekune haka?".
Yawu ya khaleel yahad'iye da k'yar, yad'an sosai saman girarsa yana fad'in "um, um, Ammah kedai dakin bani tea d'in k'awai, kingafa rawar sanyi nakeyi, ga zazza6i mai zafi ajikina.
Tofa, ninaga wannan aiki, wai kishiya tara rana d'aya, tafice tana tsogumi akan momy, kai laure ko y'ar banzar yarinya, dasotayi tasaka yara cikin tsaka mai wuya, kullum tahana yaro samun ladan aure, aikinga danayi maganin tsagerancinta yanema ma kansa mafita, shima da munafiki yana min mazurai bayason auren, to yanzu ubanwa ya aikeshi gunta hardasu ciwo, mtsoww yaran zamani aii akwai iyayi da firfirta, yo inba firfirtaba miye nakirana wai basuda lfy?.
Koda dayake daya fad'ama tsagerar uwarsa d'incan aii gwamma nid'in, Dan nasandai Bilkisu bazai iyaba, bare waccan shema'un da bata shiga sabgar kowa (umme amarya🤣).
Tana had'a shayi akicin d'insu take wannan tsogunguman nata, (nace kai Ammah ikon ALLAH😀).

__________
Chapter 22 · 0% Book details