← Book details Ciki Da Gaskiya Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 14 OF 83

Sashe 14

Ciki Da Gaskiya Part 2 Complete Hausa Novel · about 6 min read

Anty Ama tabud'ema Aysha motar dake gabansu, zuciyar Aysha sai harbawa takeyi, ahaka tarumtse idanu tashiga tana karanta addu'a aranta.
Kamshin turarensane yadaki hancinta, ta sauke numfashi da k'yar tareda had'iyar yawu.
Lafewa tayi ajikin murfin motar bayan Anty Ama tarufesu.
Ema...dake gaba zaya tuk'asu yace, "antynmu barka da dare".
Yanda hausar tasa take gura-gura yaso bama Aysha dariya, amma saita dake tad'an murmusa tareda amsawa, takula ya khaleel ya yarda ta tuk'in EMA gaskiya, indai bashi zai tuk'a kansaba to zakaga Emanuel ne driver d'insa.
Ta gefen ido tasaci kallon boss d'in, Wanda yayi tsit tamkar babushi a motar ma, sanye yake da popul d'in shadda irin ruwan kayan jikinta, d'inkin babbar Riga, sai farar hula akansa, yanata zabga k'amshi. Muryarta can k'asan mak'oshi tace, "ina yini?".
Idanunsa dake a lumshe yabud'e ahankali, ya saukesu akanta, kwalliyar Tamata k'yau yafad'a aransa.
Jin bai amsa mataba yasaka Aysha d'ago idanunta masu yalwar gashi ta sauke akansa, azatonta baijitabama.
Da sauri ta janye idanunta saboda kallon ido cikin ido dasukaima juna, wani kwarjini Na musamman yak'ara mata, kanta tamaida taduk'ar tana kallon zanen material d'in jikinta.
Babu wanda yasake cewa komai har suka Isa wajen dinner d'in.
Abokan ango suka fito domin yimusu rakkiya, sunfara tafiya Taheer ya gwargwad'a masa wani Abu a kunne.
Saida ya hararesa sannan.
Taheer yamatsa baya yana dariya.
Batareda Aysha tayi zatoba taji yarik'o hannunta ya rumtse anashi, atare sukaji shock, ya khaleel ya sauke sassanyar ajiyar zuciya, yayinda Aysha taji wata kasala tadaban, wadda ta k'ara haddasama tafiyarta sanyi ainun.
Wajen atsare kuma cikeda jama'a, suna shigowa aka saki tafi, su Ammah ana gaba-gaba itada inna da baba jummai Maman hajia babba, Ammah sai baza hakwara takeyi Dan dad'i😁.
Saida Aysha ta zauna sannan shima yazauna kusada ita, Dan kujera d'aya aka ajiye musu, amma basu matsuba saboda tanada d'an fad'i.
Anfara gudanar da abinda yatara mutane batareda bata lokaciba, ayshadai tayi tsit tamkar ruwa ya cinyeta, tamkar ance tad'ago idonta yasauka akan Anty kubrah da glory, bak'aramin tashin hankali Aysha tashigaba, takai dubanta kan Anty meerah wadda tahango itama hankalin nata atashe yake.
Innalillahi kawai Aysha take ambata azuciyarta, tsabar rikicewar datayi batasan ta d'ora hannunta kanna ya khaleel ba, jin tana Neman jimasa ciwo a bayan hannu yasashi juya hannunta yasak'ala nasa aciki, yatsunsu suka sark'e cikin najuna, tamatse kammm kuwa batareda tasan mitake aikatawaba, kallonsa yamaida direction d'in datake kallo saiyaga momynsace awajen da wasu mata biyu da kubra, yamaido kallonsa ga Aysha da idanunta ke zubar da siraran hawaye.
Matso da bakinsa yayi saitin kunnanta, batareda tayi zaton maganar tashiba taji saukarta cikin kunnenta.
Bashiri tadawo cikin hankalinta, tafara k'ok'arin zame hannunta, bai hanataba yasaki hannun nata, tareda mik'a mata hanky d'insa alamar tagoge hawayenta.
K'ar6a tayi, tanamai satar kallonsa, Yakuma maimaita tambayar tasa.
Suwanene su?.
Gaban Aysha Yakuma tsananta bugawa, muryarta Na rawa tace, "suwaye?".
Kafeta yayi da idanunsa, tayi saurin janye nata.
Yace, " ya ina tambayarki? Kuma kina tanbayata?, banason shirme suwanene sud'in?, miyasaki kuka akansu kuma?.
"Basu nakema kukakaba, nibanma sansuba, natuna Abbah ne kawai".
Bai gamsu da zancentaba, amma ya shareta baisake cewa komaiba.
Haka biki yacigaba da gudana, duk motsin Anty Kubrah da Anty glory akan idon ya khaleel da Aysha yake faruwa, kowa kuma da abinda yake kitsama zuciyarsa akansu.
Meerah kam tuni tabar wajen dinner d'in, saboda bata buk'atar su Anty glo su ganta.
Aysha da ya khaleel suka mik'e a k'ark'ashin jagorancin mc sukabi dukkan manyan iyayennan suna godiya agaresu, (Dan kowa zuwa gobe idan ALLAH ya kaimu zai kama gabansa).
Lokacin dasuka Isa wajensu Ammah sai Ammah tajawo Aysha ta d'ora akan cinyarta, tana kukan farincikin ganin wannan rana ta auren a khaleel.
Shikam yazauna kusada ita yana share mata hawayen da hannunsa yana murmushi, nanfa camera tafara aikinta, masu d'auka a waya nayi masu camera d'in da aka d'akko nayi.
Konifa abin ya birgeni.
Momy kam dasukaje gabanta saita dafa kan ya khaleel kawai, taki kallon ko Aysha.
Ganin haka ya khaleel yakamo hannunta itada Ayshar yahad'e waje d'aya yarumtse, cikin sanyin murya yace, "ga momyna farincikina, ga matana amanata, namik'a muku amanar kaina, banida abokai mafi kusanci dani samadaku Momy & Aee'sha!".
Hakan ya Sosa ran Momy, wai miyasa zai had'a matsayinta dana Aysha?, tazare hannunta batareda ta tankaba.
Aysha kam taji dad'i harcikin ranta, sai damuwarta tad'an ragu, ganin kodai Yaya, ya khaleel d'in yadamu da ita.
Idanun Anty glo nakan Aysha, sotake tatuna Inda tasan mai irin yanayinnan amma takasa tunawa.
Kubrah kam wani d'acine aranta da kishi, tadad'e tana nunama ya khaleel d'in k'auna amma yana shareta, sai yanzu Dan abin kunya zai kwaso y'ar cikinsa amatsayin matarsa, ita kanta hasashen inda tasan matar tasa takeyi amma takasa tunanowa.
Dasukaje wajen Anty Mamie kam tamkar ta cinyesu, itama rungume ayshar tayi tana kukan dabatasan dalilinsaba, tashafa kan ya khaleel tana saka musu albarka, da fatan nasara a Auren nasu.
Komai ya gudana cikin nutsuwa da tsafta, zuwa 10:30mp aka tashi.
Yanzukam Aysha batareda ya khaleel suka tafiba, mota d'aya suka tafi da Ammah.
Shikuma yatsaya sallama da abokan arzik'i wad'anda zasuyi asibancin tafiya gida.

Koda suka dawo gidan babu 6ata lokaci aka shirya Aysha akamata rakkiya 6angarenta.
Tana kuka darok'on ifteehal takwana dan ALLAH nan suka barota suna dariyar shak'iyanci.😂
Bayan tafiyarsu saita kifa kanta akan filo tana kuka mai tsuma zuciya da tausayin kanta, kowane irin zama kuma zasuyi da mijin nata? Ya rayuwa zata kasance da surukarta? Makiyarta, wadda taso ruguza rayuwarta tun tana y'ar k'arama, ga k'annen miji da yayyensa marasa mutunci

Acan kuma hankalin hajia babba tashe, Dan Anty glo da kubrah sungano ayshace amaryar bayan dogon nazari, dasake ganinta dasukayi lokacin da'aka dawo dinner ta wanke kwalliyar fuskarta, aka rakota wajen hajia babba amatsayin surukarta.
Hankalin hajia babba amatuk'ar tashe yake, su Kansu su Anty glo hankalinsu atashe yake, haryanzu suna zaton Aysha da meerah suna cikin islands UK Ashe bahaka baneba, ya akayi suka dawo gida Nigeria? Lallai kam lik'o Na Neman 6alle musu kuwa.
Hajia babba sai safa da marwa takeyi, gawata uwar zufa dake keto mata, shin ya'akayima takasa gane Aysha?, bazai yiwu d'anta yazauna da KARUWA ba.

Aysha ba karuwa baceba☹😏.

Ya khaleel dabaisan hidimar da akeyiba yashigo gidan kusan 12pm, tawaccan k'ofar yabi 6angarensu kenan, gaba d'aya jikinsa a sanyaye yake, waishine da mata yau, yanzu bashida hujjar k'in zuwa gareta sai ALLAH ya rubuta masa zunubi, tundaga lokacin da'aka d'aura auren dukkan hak'k'inta yadawo kansa, guda d'aya yatake sai ALLAH ya kamashi da laifi.
Shikad'ai ya iso gidan, babu rakkiyar kowanne aboki.
Da addu'a yatura k'ofar falon yashiga.............✍🏿

Yasin yatsuna zafi, zand'an huta gaskiya😿🤕🤧.

😍😍😍😍😍😍😍😍😍😍😍😘😘😘😘😘😘😘*_Typing📲_*

🤰🏻
*_CIKI DA GASKIYA........_*
_{🔪wuk'a bata hudashi🗡}_

*_Bilyn Abdull ce🤙🏻_*

*_HASKE WRITERS ASSOCIATION_*
_~Home of experts and perfect writers~_

*_Sadaukarwa_*
_My sweet dady_
~(ALLAH ya gafarta maka)~
🤲🏻😭

*_part 2_*
(littafi na biyu📕)

1⃣1⃣

A tsakkiyar falon yatsaya, yanamai binsa da kallo daki-daki, komai ya birgesa da k'ayatar dashi, gawani sassanyan k'amshi Na tashi, Wanda akasan duk gidan amarya dashi, yadire ledojin hannunsa Wanda shima baisan miye acikinsuba, Dan youseef ne yabashi.
Rasa d'akin dazai dosa yayi, baisan ainahin d'akin da matar tasa takeba, yay shiru yana nazarin d'akuna ukku dake cikin corridor d'in, zuciyarsace tafi karkata dana k'arshe, cigaba yayi datakawa ahankali, kaikace yana tsoron Isa ga d'akinne. Harya k'arasa jikin k'ofar.
Zuciyarsa tashiga harbawa da sauri-da sauri, shikam ba jarumi baneba awannan ga6ar, zai iya rantsuwa baita6a kasancewa dawata mace daba muharramar saba Na tsawon minti talatin, dagashi sai ita, saidai abokan aiki, suma basukad'aiba gaskiya, dolene kasamu akwai wani taredasu.
Cikin rinmtse ido yamurd'a handle d'in k'ofar yashiga, bashida za6in daya wuce hakan, musamman idan yatuna da lectures d'in malamai data gudana a wajen waleemar auren nasa.
Sallama yayi amma babu amsa.
Chapter 14 · 0% Book details