← Book details Ciki Da Gaskiya Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 19 OF 83

Sashe 19

Ciki Da Gaskiya Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

.......Anty zuwairah ce tafara ganinsa tace, "yauwa khaleel aigara dakazo, yau saina zane mara kunyar matarka a gidannan, ita hartayi balagar aikama da momy zagi?".
Shiru yayi yana binsu da kallo d'aya bayan d'aya, Anty zuwairah tace, "wai bakajin minace? naji kayi shiru".
"Naji". 'Yafad'a yana cigaba da tafiya hanyar d'akinsa'.
Sudai su mufeeda baki yamutu, sunyi tsit.
K'ofar d'akin nasa yamurd'a zai shiga yajita 6am. Mufeeda tace, " ya khaleel tana cikifa ta kulle kanta saboda tasan batada gaskiya".
K'ala baiceba, sai harara daya bankama mufeedar, tayi k'asa da kanta tana k'unk'uni.
Yafara kiran " Aee'sha! Zoki bud'e k'ofar nan".
Dukda tagane muryarsace saida tace, "wanene?".
"k'aniyarkice, kibud'emin k'ofa nace!!". 'Yay maganar a tsawace'.
Batareda tabud'e k'ofarba ta jingina ajiki ta fashe da kuka, ''ALLAH ya khaleel nabud'e dukana zasuyi, nikuma tsoro nakeji, kace sutafi sannan saina bud'e".
Huci yafurzar daga bakinsa. yace, "Aee'sha karki bari raina ya6aci, kibud'emin k'ofa, babu wanda zaimiki wani Abu acikinsu ina nan".
" har Anty zuwairah? ". 'Aysha tayi maganar tana kuka'.
Cikin tsawa yace, "k! Wlhy zan sa6a miki idan baki bud'emin nan da 3minutes ba!!".
Su Anty zuwairah kam duk dad'i yakamasu, sunsan saiya yima Aysha dukan mutuwa. k'ilama ya saketa saboda zagin momy datayi, kai da sunji dad'i kuwa.😂
Aysha kam saida taga minti ukun daya bata sunkusa cika sannan tabud'e k'ofar.
Yana niyyar Shiga su Anty zuwairah suka tashi suma, hannu yad'aga musu alamar su dakata, sannan yashige, yamaida k'ofar yarufe harda Murza key.
Aysha tak'ara k'arfin kukanta, tana ja da baya dafad'in wlhy ya khaleel ni ban zagesuba, sunema suketa zagin Abbana, ALLAH Anty mufeeda Ce tahad'a".
Ko kallon Inda take baiyiba, ya ajiye jakkar laptop d'insa da hula akan gado, fuskarnan a murtike, babu alamun wasa, yafara cire ma6allan rigar Uniform d'insa, saida ya 6alle tas sannan yafara k'ok'arin zare belt d'insa.
Aysha tanacan jikin Bango tana kuka, duk zatonta dukanta zaiyi da belt d'in.
Ganin yacire komai, dagashi sai vest da boxer ta rintse idanunta, ya zauna akan sofa yana kwance igiyar takalminsa, sannan yazare har sock's d'in, yana mik'ewa Aysha tak'ara k'ank'ame jikinta, azatonta kanta yayo, saitaga yashige toilet.
Ajiyar zuciya tasauke da baza idanu kozataga key d'in, bataso yafito ya sameta a d'akin, kuma tana tsoron fita sabodasu Anty zuwairah.
Suna falo kuwa sai cika da batsewa sukeyi, suna jiran jin hukuncin da ya khaleel d'in zai yankema Aysha, amma sai sukajiyo tsit, sunsan wani lokacin idan yanacin uban mutum baya barinsa yayi kuka, shiyyasa sukad'an k'ara jira.
Inda yabarta anan yafito ya sameta, sanye yake da lemon green d'in rigar wanka, hannunsa rik'eda k'aramin towul yana goge Kansa zuwa fuska, da'alama wanka yayo.
Aysha tana ganin Yakama igiyar rigar zai kwance tazame k'asa, tareda cusa kanta tsakanin cinyoyinta tana rera kuka a hankali.
Kallo d'aya yamata ya d'auke kansa, cigaba yayi da shafa mai, yasaka k'ananun kaya marsa nauyi dabazasu takura masaba, yad'an yafesa turare.
Inda Aysha take zaune yanufa, yad'auketa cak, aikam tafasa masa k'ara, tsawa yadaka mata, tayi saurin to she bakinta da hannu.
Su Anty zuwairah dake falo suka fashe da dariya, harda tafawa, su duk zatonsu ya khaleel Na punishing d'in Ayshane.
Ya d'orata visa gadonsa, ya haye shima tareda rungume kayarsa, ya lumshe manyan idanunsa dake cikeda barci, mutsu-mutsu Ayshan tafara, yabud'e ido dak'yar Dan barci harya fara figarsa, "k wlhy inbaki nutsuminba zan dakaki ad'akinnan, sannan Na turaki waje su Anty zuwairan suyi duk yanda sukaso dake, stupid girl kawai".
Tsit Aysha tayi, takoma ta lafe a k'irjinsa, Yakuma rungumeta da k'yau, yamaida idanunsa ya lumshe, cikin lokaci k'ank'ani barci ya d'aukesa.
Aysha tabud'e idanunta dasukasha kuka, duksun mata nauyi, fuskarsa take k'arema kallo, yanda yake barci cikin nutsuwa, numfashinsa nafita ahankali, fuskarsa tayi fayau ko'a fili bata zama haka Dan tamkar yana murmushi, wani dad'i ya mamaye zuciyar Aysha, wai itace kwance visa k'irjin ya khaleel yau? abinda ko'a mafarkinta bata ta6a zaton faruwarsaba, "ya ALLAH Na gode maka da wannan k'yauta, shima ALLAH kasaka MASA sona, fiyeda yanda nake sonsa".
Haka taita tunane-tunane itama har barci 6arawo ya saceta.
Afalo kuwa bayansu Anty zuwairah sunji ihun Aysha da tsawar da ya khaleel yaymata sai Anty zuwairah tace sutashi suje, tasan khaleel zai tunkud'o k'eyar Aysha har gaban momy, bayan yagama kir6arta, da wannan shawarar suka koma cikin gida, tareda kaima momy dadd'an labari, wai khaleel nacan na zane Aysha, harda kulle k'ofa.
Momy taji dad'i sosai, har zuciyarta tad'an huce, amma dolene tad'auki matakin gaggawa, inba hakaba Aysha zata musu 6arin makauniya agidannan.
Anty shukura kam hankalinta yatashi, batareda sanin kowaba tanufo gidansu Aysha, tsit taji falon, harta juya amma hankalinta yakasa kwanciya, komawa tayi tacan bayan d'akunansu, talek'a window d'in ya khaleel, kwance ta hangosu manne da juna suna barcinsu hankali akwance, murmushi tayi dafad'in Alhmdllh.
Cikin nishad'i takoma tacigaba da harkar gabanta, tana mai k'arajin k'aunar khaleel d'in aranta, da halayensa masu matuk'ar birgeta.

___________________,,,
Kiran sallar la'asarne ya farkar da khaleel, ya bud'e idonsa akan Aysha dake kwance bisa jikinsa, dagani kasan tanajin dad'in barci, aransan yace, "masha ALLAH, balaifi yarinyarnan k'yak'yk'yawace, komai nata yana tsaka tsaki wajen k'yawun, babu abinda yafi d'aukar hankalinsa sai kwantacce gashin gaban goshinta, Wanda yakusa had'ewa da gira, ga zara-zaran gashin idanu, zaka iya d'aukama ta k'arane amma natane, samun kansa yayi da Sosa saman idonta da d'anyatsansa, yanayi yana murmushi".
Acikin barci Aysha taji kamar ana mata tafiyar tsutsa akan idanu, tabud'e idonta ahankali, yayinda ya khaleel yajanye hannunsa yana wani k'ara had'e fuska, shi a dole kar a kawo masa raini.
Tsaf Aysha tagane shine ke ta6a mata saman ido, dariya abin yabata, amma batayiba ta gimtse, tana kallonsa yasauka daga gadon yashige toilet, itama sauka tayi tana mamakin barcin dasukayi.
Tana nan zaune yafito da alama alwala yayo, yanata shan k'amshinsa yace, ''kitashi lokacin sallah yayi".
Kanta tad'aga masa batareda ta tankaba, itafa yana bata dariya, duk dan kar arainasa yake wannan cika da batsewar.

____________________________

"Aminiya kece agidan namu?".
"Wlhy kuwa nice aminiya, canayi bara nazo namiki barka da tashin bak'i ko".
Baki hajia babba ta ta6e, "kinada abin haushi wataran hajia khaltum, ni namaji dad'in zuwanki, koda bakizoba nidama zanzo".
"Tofa miya farune".
" aminiya yarinyarnan zata zamemana matsalafa, nifa bazan 6oye mikiba inacikin matuk'ar tashin hankali tunda su kubra suka sanar mana yarinyarnance".
"Bake kad'aiba wlhy Aminiya, ingaya miki nakasa zaune nakasa tsaye, akwana biyunnan tufk'awa da warwara kawai nakeyi, dama jira nakeyi bak'i sugama tafiya Nazo muyi magana, matsala biyuce ta tasomu gaba, d'anki da matarsa, Dan kinsanfa duk wani asusun banki na Oga barau yadaina aiki, gashi hukumar shigi da fici sunyi seizing d'in passport nasa, yau yau d'innan aka kama Lazarus".
"Kai haba! Aminiya munshiga uku, waye yakamashi?".
"d'anki Ibraheem".

"Ibraheem fa!?, yaushe yafitama daga gidan? Shida yake hutu".
"Aikamdai yau d'innan da safe, dan gwaska ya tabbatarmin dayaga Ibrahim da idonsa, kinsan kuma yasanshi dai".
Zuface tafara ketoma hajia babba, tace, "shikenan munshiga tara".
"Nifa mamaki kike bani, miyasa kike tsoronsane? ina ganin akwai mafuta".
"Hummm kaltum haryanzu bakisan wanene Ibrahim ba nakula, amma miye mafitar?".
"Kawo kunnenki".
Hajia khaltum tafad'a ma hajia babba abinda nima banjiba.

Tad'anji sauk'in damuwarta, harta zayyanema hajia khaltum abinda Aysha tamusu yau.
"Ammafa yabirgeni daya zaneta, kuma tabbas ayau d'inan zamu kawo k'arshen iskancinta, Dan sha yanzu magani yanzu yafi dad'i, dama binda tayima su kubrah ya 6atamin rai, nakula itafa jin kanta takeyi on top saboda ta auri Ibrahim, shiyyasama takemana barazana, tana wasa damune, duka-duka shekarunta nawa?".
"Ca zakiyi shekarun uwarta nawama bare ita".
"Wlhy kuwa. Kedai yau ki birkice musu kawai, Dan bazasu ta6a kasancewa a inuwa d'ayaba, nasan duk Girman kan namiji saukeshi yakeyi akan mace, duk wannan mazuran dakikaga yanayi tsaf zai iya kwanciya da ita, tom inhar kikayi k'ok'ari yauma yakwana awajenki zamuci nasarar aikinmu, Dan adaran yau su gwaska zasu gama aikinsu akanta".
"Shikuma sai Aleeya tashigo rayuwarsa, Dan yakamata ki tada maganar bikinsa da ita da gaggawa".
"Kinsani farinciki aminiya, amma da zuciyata tamin k'unci, yanzu kam nasamu nutsuwa, shiyyasa banida kamarki duk duniyarnan, ngd ngd".
"Kibarmin godiya, munrigada munzama d'aya aii, kedai kawai kiyi k'ok'ari yauma, Dan wannan ciwon nakine kawai zai hanashi kwana agidansa".
"Gaskiyane, nima aii nasan taurin kansa, Ibrahim murd'ad'd'en mutumne, juyasa saimai basira, tun yana k'araminsa mutumne mai masifar taurinkai, balle yanzu da aikinnan nasa ke k'ara masa masifa da bushewar zuciya".
"Aii bak'aramin kuskure kikayiba dakika amince masa shiga aikinnan".
"Inbanda abinki wayasan mi gobe zata haifar, kumafa alhajine ya d'aure masa gindi".
Hummm like Father like son.
"Aigashinan yazame mana masifa kuwa, amma zamu nuna masa mun rigasa zuwa duniya aii''.
Haka sukaita tattauna batun, da yanda zasu 6ullo masa.

_____________________________
Aysha na zaune gefen ya khaleel dakecin abinci, itama ya tsareta saitaci, turawa kawai takeyi, Dan ko kad'an batason cin Abu mai nauyi tunda tadawo daga turai d'innan.
Tsaf shima ya fahimceta, Dan haka yad'aura d'ammarar dawo da ita kan turbar al'adarta, tanaci tana tunzura baki gaba.
Yi yayi tamkar baisan da zamanta awajenba, cin abincisa yakeyi yana kallon labarai a aljazeerah.
Kamar zatayi kuka, sai Harar gefen ido take masa, wadda tasan inhar yagani sai kashinta ya bushe.
Ahakadai suka gama, ammafa saida ya tsare Aysha taci sosai, da kuka kuwa tacid'in, tana bashi mamaki yanda kuka baya mata wahala ko kad'an.
Suna kammalawa ta tartare wajen, shikuma Yakoma saman kujera ya zauna, k'afafinsa nakan k'aramin table na glass, ya canja tashar zuwa sunnah TV, wa'azin sheaik Kabeer gwambe aka saka, kuma akan aure ake wa'azin.
Aysha tafito data kichin, ya khaleel yana burgeta, zata iya cewa bata ta6a ganinsa yana kallon wak'ok'i ko wani film d'in dabai daceba, kai ko wak'a bata tunanin yanajima, dukda kasancewarsa matashi, koda yaushe saidai kaga yana kallon labari ko wa'azi, Indai kaga yazauna kallon film to tabbas zai k'arune dawani Abu aciki.

Shiru babu mai cema wani uffan, amma suna sauraren wa'azin, saidai kunya takama Aysha sosai, daurewa kawai takeyi.
Wa'azin kam sosai yay tasiri ga ya khaleel, harma yake sak'ama ransa wani Abu daban....

__________________________
Chapter 19 · 0% Book details