← Book details Amfanin Soyayya Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 39 OF 46

Sashe 39

Amfanin Soyayya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"dalla dakata malam kaji a baki na nace maka ina son tane har kaje kake gaya mata ai ita tasan bana sonta ko zuwan da kaga nayi da gigicewan da nayi dan saboda Kai ne bana son ka hada baki da kazamin bakin ta guntun cancer dako kyan gani babu ba hakori har 2 amma badan nadamu da ita ba."

Mujashid yace "to nagode dan reni hankari."

Hassana ce takira Ummi tace "Ummi kar ki nemi Ruwaida fa wai hayaniyane bata so kanta yana mata ciwo tana gidana ita tasa aka kirani ashe amma nasa an mata komai matar da ta mata aikin har tafi wanda tayi na gida iyawa sai anjima zan kawota."

"to yanzu Hassan tana gidan naki tunda baki kirani ba sai daren nan ga Mijin tama yana tambayanta yanzu yafita a nan."

"afuwa Ummin mu ita tace idan akasan inda taken yanzu su Farida zasu zo su dameta."

"to shikenan sai kunzo."

*Borno*

Ayya kam sai hamdala dan kowai yayi mata daida a rayuwanta sosai dangin mijinta suke sonta da tattalinta hatta kishiyar ta kwantar da kai tayi suna zaune lafiya dama Maryam kishiyar ta bata da matsala

Balle shi oga da ko ita Ayya bazata ce ga adadin sonda Grema yake mata ba

Kwace take akan cinyar sa rokon sa take akan yabarta ta tafi adamawa saboda shiye shiyen bikin Hamrah

"to wai yanzun me zaki jeyine? bikin da sai on 29
saura fa 2weeks ."

marairaicewa tayi tace "to ai muna wasu shirye shiye ne akwai abin da zan tafi mata dashi da kuma Hajja Batul zata mata gyaran jiki na sati biyu amma ni ko kwana dayane kabari naje nayi ga Barrat ta dameni zan wuce kaduna na kaita wajen Abdallah sai kuma inson samu ne nawuce Kano naga my Ruwa."

"caf kaji duk wannan yawon sai kace shanshani."
Shafo cikinta yayi yace "ban sani ba ko inada ajiya anan a wahalan minda baby kide aika Hajja Batul din namiki alkawarin zakije auren Hamrah sai kuhadu akanon Barrat kuma zan sa akaita wajen Abdallah dan Abban Ruwaida yakirani jiya ma wai dan Allah akawowa Abdallah Barrat."

*Kano*

washe gari Ruwaida tasha kuka dan sai asannan akace mata Abban ta har yanzu bai shuce ba akan abinda ta masa ba

cikin kuka tace
"Ummi dan Allah kar ku kai ni dakin aure mahaifina yana fushi dani."

Ummi wayan ta tadauko takira Abban yana dauka ta gaya masa komai tare da bashi hakuri

"shikenan Hjy Ruwaiya amma badan gidan aure zata ba da bazan sauko dawuri ba Amma bata wayan."

Ummi ta meka mata

Kuka Ruwaida ta fashe dashi
"Abba kayafe min Wllh tun alokacin dama bada niyar gaske na........

"stop AISHA na yafe miki nakuma samiki albarka kuma cikin satinnan za muzo nida Hajja da malama dan malama ta matsa tana son ganin ki."

"Abba malama kuma?

"Eh."
Yace

Haushi ne yasa Ruwaida cewa "to Abba nagode."
takashe wayan ta mekawa Ummi wayanta

Nasiha sosai su Ummi su kayiwa Ruwaida

Abida takama hanuta suka rakata adaidai get Ruwaida ta tsaya t
cek abin ya bawa sau Abida mamaki amma sai suka ji kamar addua take

Ruwaida sai da tayi dogon addua ta amfaci sunan Allah ta daga kafar dama ta shiga bakin ta dauke da addua har zuwa bedroom dinsu kokarin zaunar da ita Abida tayi amma taki zama

"Aunty abeed zan dan shiga bathroom."

Dariya su Kharajina suka ai dole cikin ki ya kad'a wannan k'iran na yamall

Aunty Hassan tace "bama son rashin kunya fa Nafi ku fice mana."

Farida tace caf "ai muna nan sai munga kokof."

Abida tace "a kofe kude inde yamall ne

Ruwaida alwala tayi tafito tace "aunty abeed ina sallahn da daddy yabani dama yana hannu Ashur kanin Farida har Qur ani da shijab ta karba ta tada ikkama tayi rakk'a 2 tare dogon addua har su abida suka gaji sukace mude zamu tafi kar wannan mugun ya taddamu dan dare yayi

Nafi tace "wai ita y'ar iska dan mubar mata gidan tane tawani share mutane ta dauki karatun munafurci to Wllh gobe da safe anan zanyi break."

Haka suka karaci mata tsiya su

Suna fita Ruwaida ta fara jin wani mugun ciwon mara wanda na period ne dan tana shan wahala gashi dama doctor ya hanata shan kowane magani acewar sa zai iya mata wani illan tunda shekarun ta yakai na aure tayi shine samun saukin ta saide tayi ta han ruwa mezafi dan samun sauki da wuri

fitowa tayi general Parlour na kasa dan ko zata samu ruwa dan kitchen din saman taga fanfon yaki kuma bawani alaman ruwa aduk fridge din

Tana fitowa ta zube a kan kujera tana dafe da maranta

Mall badan yanda Ummi tasa ido akan saba ba abin da zaisa yatare part din nan batare da Haliman saba

tana kwacen yazo ya wuce ta yashiga

Bayan yafito a toilet ne yagama shirin komai nasa yaja wayan sa zai tura wani sako ta email duk akan ashirin auren sane

Message yake ta shiko masa ta whatsapp sai da yagama abinda yakeyi

yashiga WhatsApp din bakon number yagani
Shiga yayi yaci garo da abinda ya firgitashi

Kamar haka harda video

_Mall me Sa a ko nace me sakaci ka ari mace me kyu bayan hausawa sunce mace me fasale ko tai aure bata dan gana ba kai ko ita ta dangana mu Mosoyan ta basu dangana_

Sai ya danna video din
Kansa ne yafara zuyawa amma yana cigaba da kallon yanda Ruwaida da Affan suke romance na mugun watsewa kuma a zir din su suke adaidai sanda Ruwaida ta kamo gaban Affan zata sa abaki

wani irin k'ara Mall yasa tare da mekewa kawai tsintan kansa yayi a parlour inda Ruwaidan take kwance bai karasa ba ya jefa mata wayan sai da yadaki goshinta ita ma k'aran tasa dan ko bata duba ba tasan ya fasa mata goshi

"kidauki wayan kigayawa kwarton ki ni Ismail Wllh na wuce kuntun su dan haka yadena bawa kansa wahala wajen turomin k'azanta cikin waya idan ganinki yake so yayi yane ma muku inda zaku na haduwa bani da damuwa."

yana gama fadan haka ya haye sama

zubewa yayi a gado yana wani irin numfashi abin tausayi

Ahankali cikin ma wuyacin hali ya furta
```Ummi idan kin rasani dalilin Ruwaida ne ai kinga irinta ga abinda yasa na hakura da ita ya Allah ka d'auke rayuwan baiwar ka AISHA dan zuciyar bawanka Ismail ta samu sauki ko kadauke nawa na huta```

Ruwaida saida taji rad'adin goshin yadan lafa ta dauki wayan da har lokacin videon ne yakeyi

"walahaula walakuwata illahbillah!."

Affan dama duk zamanda muke da kai daukana kake kana adanawa nashiga ukku ni AISHA zinah nadena ka baka dena bina ba duk da haka ba zinah nayi gaba daya ba
Asttafullah kuka take sosai tunanin bari takira mommy sa ta gaya mata abinda Affan yayi baikyu ta ba tayi dan tana da number ta Akanta

Sallama mommy tayi tace
"dawa nake tare."

cikin rawan murya Ruwaida tace "mommy nice."

"Ruwaida yawwa ai dama nemanki muke ido rufe saboda munfara aikin mu amma sai da hadin kanki zamu samu nasara da gaggawa yanzu haka ga son nan munturawa Ismail sak'o muna jiran Ripley ne ke kuma akin da zan baki sai mun hadu gaba da gaba dan haka ki san yanda zakiyi ki samu ki fito cikin kwanakin nan biyu
kuma dan Allah kar ki yarda ko hannunki Ismail ya taba dan ga son nan tunda yamma yakasa cin komai wai idan Ismail ya kusanceki bazai iya rabuwa dake ba
gashi ma Affan dinki dan lallasheshi......

"Hello my love. "

"Affan kana tunani abinda kamin shine soyayya yanzu kam banyi nadaman rasa kaba sai ma godewa Allah dan ku ba alkairi bane agareni."

"what Affan ne fa my love menayi miki."

"ashe Affan duk zaman mu dakai muna furtata kake kana daukana a video dan wata ran katuzarta rayuwa ta ko kamar yanda kayi yau."

Affan yace
"ada banyi da niyan wani abu ba kawai idan ina wajen aiki nayi missing naki idan na kunna nagani sai nasamu nusuwa yanzu haka na kunna ina kallo ina kuka mommy da tagani tace ai wannan ma makamine na turawa Mall kinji yanda akayi."

"Affan Wllh sonda mommy take maka zai kaiku ga halaka kuna rayuwa sai kace na ya hudawa nik...

Kar ban wayan mommy tayi tace "Ruwaida idan na fashimce ki kamar bazaki bamu hadin kaiba ko to Wllh idan kina shirin haka ma kiyi.......

"dakata mommy dama da hadin bakin ki Affan yamin haka na cire Affan a sawun masoyana masoyi bazai min abin da yamin ba dake da danki kufita min cikin rayuwa."

Tana gama fadan haka ta kashe wayan

Tashiga video din tayi detele din komai

Tsaban bacin rai ciwon ma rasashi tayi ajiye masa wayan tayi ta haye sama dan yanzu ita ma kunyan Mall takeji zata guji duk hanyan da zai hadasu

Bayan sati 2

Ruwaida da Mall tunda abin yafaru ba suga juna ba gashi har gobe dauren auren sa da Halima Sahal da Hamrah

abangaren Affan shida mommyn sa sai abinda yakaru suna shiri sosai dan ma sun rasa number Mall dan wanda suka turo na farko bai sake kallon inda wayan yake ba

Ruwaida tana babban gidan ana ta harka kannen ta sunzo ga Barrat har da Hajja

Khalifa ne yashigo
Ruwaida tace "ya khall yaushe kazo."?

"Lill momy ai tunsan da kika k'ule a gidan ki kika manta mu."

Dariya Ruwaida tayi tace "sorry yakhall Wllh ba waya a hannuna kuma lefin su Nafi ne ai kullum muna tare."

ganin wawulon Ruwaida yasa Khalifa ya dafa kansa alamun yayi mantuwa
yace "kahs kinga ko nakusa na manta doctor kin fa yamin waya yace zuwa yanzu za a iya miki aikin hakorin dan haka asa ranan komawa asa miki."

"yawwa yakall kamar kasan Wllh amatse nake ko bakina bana son budewa gaba daya."

Dariya Abubakar k'anin Sahal yayi
yace "kaci uwar gida wato kina tsoron amaryar mu tazo tana renaki da wawulon baki ko."

hararan sa Farida tayi tace "ai Wllh yabull ko duk hakorin ta rasa Wllh wuce nan wannan me bakin fuskan tarena ta."

Abubakar yace "ban da ky'ashi ai naganta a colander tas take."
Chapter 39 · 0% Book details