Sashe 38
Wasu Mazan Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ganin haka ya juya ciki a lokacin da ya isa cikin ɗakin Mama. Tana zaune a falo tana kuka. Mama ke gefenta tana ba ta baki. Tsaki ya yi sannan ya sannan ya kalle su," Ke Nasreen mijin ki na waje ya zo biko, kuma wallahi kika yi masa rashin mutunci sai kin sani."
"Baba, don Allah ka sanya Faruk ya sake ni wallahi na tsani zama da shi." Ta ƙarashe maganar cikin kuka.
"Hmmmmh!Kina dai ganin turjiyar da Ahmad ya nuna kan zai raba aurenki, amma daga karshe kin ga an neme shi an rasa. Ko wannan bai isa ya nuna miki aurenki da Faruk, mutu ka raba ba?"
"Shikenan, cikin ƙunci zan ƙarashe rayuwata? Ban sha ta daɗi ba, a lokcin da na ke ni kaɗai a gurinsu, ballantana yanzu da yake da wata matar?"
"Sai ki je ki yi hakuri, kuma Nasreen in an bi ta ɓarawo, abu ta ma bi sahu, don shegen kafiya ce da ke, wataƙila ɗiban albarka kike masa."
Takaici ya sanya ba ta amsa masa ba, sai kuka tana share hawaye."Ki je yana jiran ki, kuma wallahi kika yi masa rashin kunya, kin san shi ma ba kanwar lasa bane." Ya ƙarashe maganar tare da juyawa ya fice.
Kallon Mama ta yi sai ta fashe da kuka, tare da faɗawa jikinta."Mama, ki yi mini addu'a, kar na koma gidansa na kwaso zunubi duk bana jin akwai sausauci a tsakanina da shi. A dalilin a biya shi kudinsa, Ya Ahmad ya ƙarfafa tafiyar nan, duk lokacin da na tuna ji nake kamar na shaƙe sa ya mutu."
Kuka take yi sosai tana tausayinta."Ki yi hakuri ki ci gaba da addu'a, kin ga yanzu ina kafe dole ya sake ki, ba mu da kuɗin da za mu yi masa hulɗi. Allah yana tare da ke, tun da ya halicce. Ko ci gaba da kai masa kuka, watarana zai ji kukan ki, domin baya zalinci kuma ba ya barin ayi."
"To,"Ta ce ba don ta haƙura ba, sai dai ba yadda za ta yi. Ta san cewa tun da Ahmad ya ɓata, ba ta da sauran gata, sai dai zuciyarta na ƙarfafa mata ita ce kawai gatanta a duniya. Ita za ta tashi ta ƙwaci 'yancinta, tun da Baba bai damu da rayuwar ta ba.
Wanke fuskarta ta yi sannan ta sanya hijabi ta fita. A lokacin har ya tada mota zai bar gurin. Ganinta bai sanya ya fasa ba, har sai da ya fara tafiya. Ko mai ya tuna oho ya ja ya tsaya.
Ganin shiru bai tafi ba sai ta ƙarasa gurin motar. Tamkar wani baƙo a gurinta ta tsaya ba tare da ta ƙarasa ba. Zuciyarta bugu take mata tare da wani irin tsanarsa. da haushinsa suka haɗu suka sanya zuciyarta tafasa. Don kawai ta san Faruk ba zai taɓa sace Ahmad ɗin ya ci gaba da zama da ita ba, saboda ta san ba ya sonta, kawai yana zama da ita ne don ya wulakanta rayuwarta, amma za ta iya zargin shi ya sace shi.
"Ke an gaya miki zan cigaba da jure wulaƙancin ki ne?" Ya furta daidai lokacin da ya buɗe ƙofar yana mata kallo tamkar ya ga kashi. Ganin ta yi shiru ba ta ce komai ba, sai kallonsa take yadda ya ƙara kyau har tumbi ya ɗan yi.
Tsaki ya saka yana kallonta."Dubi yadda kika lalace kika koma wata tsohuwa dake. Ɗan watannin da kika yi, ya sa ya kika koma haka? Wannan in da za ki yi shekara sai an tausaya miki, kuma a haka kike mini wulaƙanci har kike wani banza gardi can da aurenki ya ba ki jininsa? Kin san ba ki da gatan da ya wuce zaman gidana. Ita wacce take zuga ki tana ina? Ta bar ƙasar bayan ta lalata miki rayuwar auren ki." Ya numfasa yana watsa mata mugun kallo ko za ta ce wani abu.
Raihan ce ta fito daga cikin gidan da sauri ta ƙara so."Abba," Ta ce tare da kama hannunsa.
Da sauri ya fisge yana kallonta kamar zai yi amai."Kina gani ko Nasreen, kina ganin irin rayuwar talauci da ƙaskancin da kika zaɓi yarana su kasance. Dubi jikin Raihan kamar wacce ta shekara ba ta yi wanka ba? A haka kike son ki wulaƙanta rayuwarsu. Su taso cikin talauci da dauɗa kamar yadda kai taso."
Hawaye share suke ƙoƙarin zubo mata jin tozarcin da yake mata yana ɗaya murya. Juyawa ta yi za ta shige ciki ba tare da ya ce komai ba. Da sauri ya fito ya sha gabanta."Zaman wahala da kika yi a gidanku, har yanzu ba ki zama mai biyayya ba, saboda iskanci ina magana za ki wuce."
"Ba ni da abin da zan ce maka Faruk, duk abin da kake yi mini Ubangiji yana kallonka kuma ya san halin da na ke ciki. Kana amfani da rashin iyayena kana wulaƙanta rayuwata, saboda ƙofar da mahaifina ya ba ka. Na san cewa watarana za ka yi dana sani mara amfani, domin aikin alkhairi kawai mutum zai aikata ba tare da ya yi nadama ba, amma watarana za ka yi nadama a lokacin da ruwa ya ƙare wa ɗankada, kuma tusa ta ƙarewa bodari.
Wata mahaukaciyar dariya ya saki tare da buga bayan motar sa."Matuƙar kika ce haka kin yaudari kanki. Abu biyu zai sanya ki gane ba zan taɓa nadama, yadda ɓacewar Ahmad ta zo miki bazata, wadanda suke miki ingiza mai kantu suka gudu."
"Akwai wanda ba ya bacci kuma ba ya barin mai zalinci, da Ni kaina Faruk. In har sun kauce a rayuwata. Ubangiji yana nan domin shi ya yi wa masu hakuri da cewa su ci gaba da hakuri, sannan ya yi musu busharar samun sauƙi a rayuwa. Akwai wanda zai iya sanya maka soyayya ta a lokacin da na yi maka nisa, a lokacin da wutsiyar raƙumi ta yi nesa da ƙasa. Allah zai iya jarrabar ka da mutuwar sona.."
"Ƙarya kike yi matuƙar ina da kuɗi zan iya auren matan da suka fi ki kyau da ƙuruciya, kamar yadda na auri Rashida wacce take bin duk abin da na ke so, kuma take cike mini gurbin da duk macen ƙwarai ta kama ta."
"Kuɗi ba sa maganin komai Faruk, yadda kake wulaƙanta rayuwata ina kaiwa Allah kukana. Ina ji a jikina za ka yi nadama mara amfani. Watarana zai zo ka durƙusa a gaban kana roƙona a lokacin da ba zan saurari kukanka ba"
"Na lura ɓacewar Ahmad ya zautar da ƙwaƙwalwarki. Ya kamata kafin na mayar da ke gidana, aje a duba ki kar ki zo ki cutar da matata." .
Jin abin da ya ce hawayen suka wanke mata fuska."Ni kuma zan tuna maka da wannan ranar karka manta da kalaman da ka gaya mini, saboda zan tuna maka da su, watakila a nan ko a wani guri."
"Ba za ki tuna mini ba, don na yi wa kaina alƙawarin wulaƙanta rayuwarki, sai na canza miki kamanni ta yarda babu wanda zai iya kallonki da sunan yana sonki. Sai na mayar da rayuwarmu abar tausayi na ɓata ki a idanun kowa, sannan zan yarda ƙwallon mangaro na huta da ƙuta.
Murmushi mai ciwo ta yi tana faɗin,"Wannan shi ne soyayyar da kake mini kafin ka aure ni? Dama soyayya yana zama ƙiyyaya Faruk?Mai na yi maka ka zaɓi ka wulaƙanta rayuwata?" Ta yi masa tambayar tare da durƙushewa a gurin.
"Wannan shi ne sakamakon macen da ba za ta bi umurnin mijinta ba, har za ta iya yarda a sanya mata jinin wani ƙarto, bayan ta gana cin ama...."
"Faruk, kar ka zarge ni da mutumin da na yi maka rantsuwar ɗan musulmi ban taɓa ganinsa ba sai a ranar. Kar ka zarge ni da mutumin da halin yanzu ba shi da maƙiya kamata. Ya yi mini rana na saka masa da dare, ta hanyar yin sanadin matarsa, wacce yake so fiye da komai. Mutumin da na sanya ƙasarsa ta yi masa baƙi har ya yi hijira duk adalilina da na zamo masa butulu, ya yi ninyar mini alkhairi sai na saka masa da sharri na zaman masa tauraruwa mai wutsiya. Kar ka zamo WASU MAZAN da babu yarda da amana a tsakaninsu da matansu. Kar ka zamo WASU MAZAN da suke wulaƙanta iyalansu..
Hannun ya sanya ya ture ta yana faɗin,"Ba zan yi sausauci a gareki ba, sannan ina gargaɗinki da ki zama mai ladabi da biyayya ga matata, in kuka ba haka ba, sai ki fara irga kanki a cikin zawarawa, don ina sonta ba zan lamunci ki wulaƙanta mini ita ba.
"Akwai Allah yana kallon ka shi zai kawo mini mafita. Zan koma gidanka saboda tursasa ni da Baba ya yi, amma ka sani wallahi ba zan ɗauki wulakanci da gurinka ba, da matarka saboda a yanzu na shirya don na ƙwaci 'yancina. Ina da daraja da ƙima 'ya mace na ke sam ba zan wulaƙanta kaina. A yanzu zan tsaya da kaina na ƙwatar wa kaina 'yanci
"Ashe kuwa kin dawo ne don na ƙarasa yanke igiyar dake tsakaninmu, saboda kin san a lokacin da kike ke kaɗai ban ɗauki raini ba, ballantana yanzu da nake da wacce take share mini hawaye. Wallahi kin mini rashin kunya sakin ki xan yi ki je can gidanku ki yi zawarci."
"Murmushi mai ciwo ta yi tana girgiza kanta ta ce,"Ashirye na ke Faruk! A yanzu a shirye na ke na yi rayuwata ni kaɗai matuƙar zan samu farin ciki. A yanzu na ƙuna bana jiran wake. Tursasar mahaifina kawai zan sanya na koma gidanka. Zawarci kaina farau? Mata nawa suke zawarcin kuma suke samu ingantacciyar rayuwa, sannan suka samu ci gaba? Sannan suke cikin farin ciki ba na tsoron zawarci in har Allah ya ƙaddara mini. In don talaucin iyayenta ne a ciki ka ganni. Yanzu da na koma gida mutuwa na yi? Da zaman aure irin na gidan ka Gara na mutu babu aure."
Wani kallon wulaƙanci ya yi mata yana dariyar rainin wayo." Nasreen marabinki da gawa rai ne kawai, amma dubi yadda kika koma tamkar mai ƙanjamau?"
"Baba, don Allah ka sanya Faruk ya sake ni wallahi na tsani zama da shi." Ta ƙarashe maganar cikin kuka.
"Hmmmmh!Kina dai ganin turjiyar da Ahmad ya nuna kan zai raba aurenki, amma daga karshe kin ga an neme shi an rasa. Ko wannan bai isa ya nuna miki aurenki da Faruk, mutu ka raba ba?"
"Shikenan, cikin ƙunci zan ƙarashe rayuwata? Ban sha ta daɗi ba, a lokcin da na ke ni kaɗai a gurinsu, ballantana yanzu da yake da wata matar?"
"Sai ki je ki yi hakuri, kuma Nasreen in an bi ta ɓarawo, abu ta ma bi sahu, don shegen kafiya ce da ke, wataƙila ɗiban albarka kike masa."
Takaici ya sanya ba ta amsa masa ba, sai kuka tana share hawaye."Ki je yana jiran ki, kuma wallahi kika yi masa rashin kunya, kin san shi ma ba kanwar lasa bane." Ya ƙarashe maganar tare da juyawa ya fice.
Kallon Mama ta yi sai ta fashe da kuka, tare da faɗawa jikinta."Mama, ki yi mini addu'a, kar na koma gidansa na kwaso zunubi duk bana jin akwai sausauci a tsakanina da shi. A dalilin a biya shi kudinsa, Ya Ahmad ya ƙarfafa tafiyar nan, duk lokacin da na tuna ji nake kamar na shaƙe sa ya mutu."
Kuka take yi sosai tana tausayinta."Ki yi hakuri ki ci gaba da addu'a, kin ga yanzu ina kafe dole ya sake ki, ba mu da kuɗin da za mu yi masa hulɗi. Allah yana tare da ke, tun da ya halicce. Ko ci gaba da kai masa kuka, watarana zai ji kukan ki, domin baya zalinci kuma ba ya barin ayi."
"To,"Ta ce ba don ta haƙura ba, sai dai ba yadda za ta yi. Ta san cewa tun da Ahmad ya ɓata, ba ta da sauran gata, sai dai zuciyarta na ƙarfafa mata ita ce kawai gatanta a duniya. Ita za ta tashi ta ƙwaci 'yancinta, tun da Baba bai damu da rayuwar ta ba.
Wanke fuskarta ta yi sannan ta sanya hijabi ta fita. A lokacin har ya tada mota zai bar gurin. Ganinta bai sanya ya fasa ba, har sai da ya fara tafiya. Ko mai ya tuna oho ya ja ya tsaya.
Ganin shiru bai tafi ba sai ta ƙarasa gurin motar. Tamkar wani baƙo a gurinta ta tsaya ba tare da ta ƙarasa ba. Zuciyarta bugu take mata tare da wani irin tsanarsa. da haushinsa suka haɗu suka sanya zuciyarta tafasa. Don kawai ta san Faruk ba zai taɓa sace Ahmad ɗin ya ci gaba da zama da ita ba, saboda ta san ba ya sonta, kawai yana zama da ita ne don ya wulakanta rayuwarta, amma za ta iya zargin shi ya sace shi.
"Ke an gaya miki zan cigaba da jure wulaƙancin ki ne?" Ya furta daidai lokacin da ya buɗe ƙofar yana mata kallo tamkar ya ga kashi. Ganin ta yi shiru ba ta ce komai ba, sai kallonsa take yadda ya ƙara kyau har tumbi ya ɗan yi.
Tsaki ya saka yana kallonta."Dubi yadda kika lalace kika koma wata tsohuwa dake. Ɗan watannin da kika yi, ya sa ya kika koma haka? Wannan in da za ki yi shekara sai an tausaya miki, kuma a haka kike mini wulaƙanci har kike wani banza gardi can da aurenki ya ba ki jininsa? Kin san ba ki da gatan da ya wuce zaman gidana. Ita wacce take zuga ki tana ina? Ta bar ƙasar bayan ta lalata miki rayuwar auren ki." Ya numfasa yana watsa mata mugun kallo ko za ta ce wani abu.
Raihan ce ta fito daga cikin gidan da sauri ta ƙara so."Abba," Ta ce tare da kama hannunsa.
Da sauri ya fisge yana kallonta kamar zai yi amai."Kina gani ko Nasreen, kina ganin irin rayuwar talauci da ƙaskancin da kika zaɓi yarana su kasance. Dubi jikin Raihan kamar wacce ta shekara ba ta yi wanka ba? A haka kike son ki wulaƙanta rayuwarsu. Su taso cikin talauci da dauɗa kamar yadda kai taso."
Hawaye share suke ƙoƙarin zubo mata jin tozarcin da yake mata yana ɗaya murya. Juyawa ta yi za ta shige ciki ba tare da ya ce komai ba. Da sauri ya fito ya sha gabanta."Zaman wahala da kika yi a gidanku, har yanzu ba ki zama mai biyayya ba, saboda iskanci ina magana za ki wuce."
"Ba ni da abin da zan ce maka Faruk, duk abin da kake yi mini Ubangiji yana kallonka kuma ya san halin da na ke ciki. Kana amfani da rashin iyayena kana wulaƙanta rayuwata, saboda ƙofar da mahaifina ya ba ka. Na san cewa watarana za ka yi dana sani mara amfani, domin aikin alkhairi kawai mutum zai aikata ba tare da ya yi nadama ba, amma watarana za ka yi nadama a lokacin da ruwa ya ƙare wa ɗankada, kuma tusa ta ƙarewa bodari.
Wata mahaukaciyar dariya ya saki tare da buga bayan motar sa."Matuƙar kika ce haka kin yaudari kanki. Abu biyu zai sanya ki gane ba zan taɓa nadama, yadda ɓacewar Ahmad ta zo miki bazata, wadanda suke miki ingiza mai kantu suka gudu."
"Akwai wanda ba ya bacci kuma ba ya barin mai zalinci, da Ni kaina Faruk. In har sun kauce a rayuwata. Ubangiji yana nan domin shi ya yi wa masu hakuri da cewa su ci gaba da hakuri, sannan ya yi musu busharar samun sauƙi a rayuwa. Akwai wanda zai iya sanya maka soyayya ta a lokacin da na yi maka nisa, a lokacin da wutsiyar raƙumi ta yi nesa da ƙasa. Allah zai iya jarrabar ka da mutuwar sona.."
"Ƙarya kike yi matuƙar ina da kuɗi zan iya auren matan da suka fi ki kyau da ƙuruciya, kamar yadda na auri Rashida wacce take bin duk abin da na ke so, kuma take cike mini gurbin da duk macen ƙwarai ta kama ta."
"Kuɗi ba sa maganin komai Faruk, yadda kake wulaƙanta rayuwata ina kaiwa Allah kukana. Ina ji a jikina za ka yi nadama mara amfani. Watarana zai zo ka durƙusa a gaban kana roƙona a lokacin da ba zan saurari kukanka ba"
"Na lura ɓacewar Ahmad ya zautar da ƙwaƙwalwarki. Ya kamata kafin na mayar da ke gidana, aje a duba ki kar ki zo ki cutar da matata." .
Jin abin da ya ce hawayen suka wanke mata fuska."Ni kuma zan tuna maka da wannan ranar karka manta da kalaman da ka gaya mini, saboda zan tuna maka da su, watakila a nan ko a wani guri."
"Ba za ki tuna mini ba, don na yi wa kaina alƙawarin wulaƙanta rayuwarki, sai na canza miki kamanni ta yarda babu wanda zai iya kallonki da sunan yana sonki. Sai na mayar da rayuwarmu abar tausayi na ɓata ki a idanun kowa, sannan zan yarda ƙwallon mangaro na huta da ƙuta.
Murmushi mai ciwo ta yi tana faɗin,"Wannan shi ne soyayyar da kake mini kafin ka aure ni? Dama soyayya yana zama ƙiyyaya Faruk?Mai na yi maka ka zaɓi ka wulaƙanta rayuwata?" Ta yi masa tambayar tare da durƙushewa a gurin.
"Wannan shi ne sakamakon macen da ba za ta bi umurnin mijinta ba, har za ta iya yarda a sanya mata jinin wani ƙarto, bayan ta gana cin ama...."
"Faruk, kar ka zarge ni da mutumin da na yi maka rantsuwar ɗan musulmi ban taɓa ganinsa ba sai a ranar. Kar ka zarge ni da mutumin da halin yanzu ba shi da maƙiya kamata. Ya yi mini rana na saka masa da dare, ta hanyar yin sanadin matarsa, wacce yake so fiye da komai. Mutumin da na sanya ƙasarsa ta yi masa baƙi har ya yi hijira duk adalilina da na zamo masa butulu, ya yi ninyar mini alkhairi sai na saka masa da sharri na zaman masa tauraruwa mai wutsiya. Kar ka zamo WASU MAZAN da babu yarda da amana a tsakaninsu da matansu. Kar ka zamo WASU MAZAN da suke wulaƙanta iyalansu..
Hannun ya sanya ya ture ta yana faɗin,"Ba zan yi sausauci a gareki ba, sannan ina gargaɗinki da ki zama mai ladabi da biyayya ga matata, in kuka ba haka ba, sai ki fara irga kanki a cikin zawarawa, don ina sonta ba zan lamunci ki wulaƙanta mini ita ba.
"Akwai Allah yana kallon ka shi zai kawo mini mafita. Zan koma gidanka saboda tursasa ni da Baba ya yi, amma ka sani wallahi ba zan ɗauki wulakanci da gurinka ba, da matarka saboda a yanzu na shirya don na ƙwaci 'yancina. Ina da daraja da ƙima 'ya mace na ke sam ba zan wulaƙanta kaina. A yanzu zan tsaya da kaina na ƙwatar wa kaina 'yanci
"Ashe kuwa kin dawo ne don na ƙarasa yanke igiyar dake tsakaninmu, saboda kin san a lokacin da kike ke kaɗai ban ɗauki raini ba, ballantana yanzu da nake da wacce take share mini hawaye. Wallahi kin mini rashin kunya sakin ki xan yi ki je can gidanku ki yi zawarci."
"Murmushi mai ciwo ta yi tana girgiza kanta ta ce,"Ashirye na ke Faruk! A yanzu a shirye na ke na yi rayuwata ni kaɗai matuƙar zan samu farin ciki. A yanzu na ƙuna bana jiran wake. Tursasar mahaifina kawai zan sanya na koma gidanka. Zawarci kaina farau? Mata nawa suke zawarcin kuma suke samu ingantacciyar rayuwa, sannan suka samu ci gaba? Sannan suke cikin farin ciki ba na tsoron zawarci in har Allah ya ƙaddara mini. In don talaucin iyayenta ne a ciki ka ganni. Yanzu da na koma gida mutuwa na yi? Da zaman aure irin na gidan ka Gara na mutu babu aure."
Wani kallon wulaƙanci ya yi mata yana dariyar rainin wayo." Nasreen marabinki da gawa rai ne kawai, amma dubi yadda kika koma tamkar mai ƙanjamau?"