Sashe 3
Wasu Mazan Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Fitowa fili za ki yi kice ni ɗan wuta ne, domin na lura abin da kike son ki faɗi kenan. Banza shashasha, kin san yadda na yi karatu? An gaya miki ni wawa ne, da zan saki kuɗina da na samu a wahalar ki wulaƙantar? To wallahi ki cire wannan bazan tunanin na ki, saboda na san darajar kuɗi. A lokacin da na yi rayuwar wahala babu uban da ya taimaka mini, sai yanzu za ki rinƙa tsara mini yadda zan yi rayuwa. In kin raina abin da na ke miki ki nemo in kin ɗauka neman kuɗin a banza ne."
"Wannan dalilin ya sanya nake son na kammala digirina, na samu aiki ko da koyarwa ce a private."
"A tunani ki kuma sai na bar ki ko?"
"Haba Abban Raihan sam ba ka yi wa rayuwata adalci ba, matukar ba ka bar ba, ai ba za ka hana ni nema ba. Kana ganin iyayena basu da shi mahaifiyata tana fama da jinya."
"Ni na ɗora mata? Tun da bani bane sai ki shafa mini lafiya. Ko da yake cigaba da karatun ma yana ƙila wa ƙala, tun da ɗan iya da ya sa ya ki shi ma ya kasa biya."
Gabanta ne ya faɗi tuna haka wanda hakan hawaye ya wanke mata fuska.
"Allah zai taimaka mini ba zai barni ba, tun da ya ga ina son karatun."
"Aci gaba in iska na hura wuta." Ya ce sai kuma ya kalleta ya ce,"Nasreen, za ki bani hakkinsa ko na je titi na nema? Tun da ga mata nan masu kyau waɗanda suka fiki."
"Ka je ba zan bayar ba wannan kai da Allah."
"Ke kuma wutarki daban ce, don in har Ina sama kina can ƙasa-ƙasa. Kina sane da Allah da Mala'iku suna tsine miki. Ki rinƙa buɗe murya kina karatun qur'ani ke a dole malama. Ƙiri-kiri ko bancin kirki ba kya bari na yi, amma in har na kawo buƙata ta sai ki koma kamar ba musulma ba."
Kallonsa ta yi cikin tsananin mamaki jina bin da yake faɗi."Dama ai ba ka nuna ilmin ka sai anan gurin, ni kuma ka ji na rantse in har ba za ka rinƙa yin soyayya ba, wallahi ba zan lamunta ba."
"Kin amince na kunna miki mu kalla sannan mu yi soyayyar? Domin ni sha'awarki kwata-kwata ba na ji."
"Allah ya kyauta! Ubangiji ya tsare ni da kallon surar wasu kai ma ina maka addu'ar ka daina domin babu kyau.
"Ashe jiki zai yi tsami." Ya ce tare da sanya hannunsa ya haɗata da jikinsa da ƙarfi.
Hannu ta sanya ta ture shi ta sanya kuka.
"Nasreen zan ci ubanki wallahi zan miki dukan tsiya a dakin nan!"
"Don Allah Abba, karka dake ta." Ya ji muryar Hairan tana faɗin haka.
Tsaki ya ja yana kallonta cikin takaici.
"Kina ganin abin da kike mini ko? Ba gaya miki za ki rinƙa kwana a ɗakina, amma wallahi ba da yarannan ba. In kin amince ki tashi mu je."
"Ni kuma ba zan bar yarana ba ƙanana saboda kai. Yarannan fa 'ya'yanka ne ba agola na taho da su ba."
"Ina ruwana ko daga jiki a suka fito. Ni wallahi yarannan suna ɗaya daga cikin abin da yasa na ƙara tsanarki. Duka shekararmu huɗu da aure, amma kin tara mini 'ya'ya biyu. Kin ji na rantse miki wallahi na ganki da ciki sai dai ki haifa a gidanku, tun da kin ƙi yin tsarin iyali."
"Ni ba zan kashe kaina ba, ai akwai na maza ka je ka yi mana. Sai ni? Da ba ni da gata, kuma 'ya'ya rahama ne wani na nema da kuɗin da bai samu ba."
"Ki je ki basu duk na yafe musu, ba ni buƙata saboda ina cikin tashen ƙuruciyata, ba za ki tara mini 'ya'ya ba ki tsigar da ni."
"Ka ji tsoron Allah kai ka ganni kana so ba tushe aka yi maka ni ba."
"Na yi dana sani saboda ba ki dace da ni ba. Sam da na san haka kike da ƙafiya da taurin kai babu abin da zai sanya na siyo ciwon kai na kawo gidana, kuma wallahi in har ba ki canza ba, kina gab da shiga cikin layin zawarawa don ba zan ɗauki iskanci ba."
Gabanta ne jin abin da ya ce, sai ta yi shiru can kuma cikin muryar kuka ta ce,"Allah shi ne gatana."
"Ni kuma ki ce sheɗan ne gatana in kin so." Ya ce tare da ɗaukar ta can ya yi ɗakinsa.
Tana kuka tana dukan ƙirjin shi, amma bai kula ba sai da ya biya buƙatar ta kamar yadda ya saba, sannan ya koma ya kwanta yana sauke numfashi.
"Allah ya saka mini ni da 'ya'yana."
"Ki fito kai tsaye ki zage ni." Ya ce tare da rufe idanunsa sai bacci.
Ita kuwa ta kasa yin bacci tana jin yadda Musaddik ya ke kuka yana faɗin,"Umma, fo." Wanda hankalinta ya ƙara tashi amma babu yadda za ta yi.Hankalinta ya kwanta jin Hairan ta sanya shi a fon.Miƙewa ta yi ta, shiga bayi ta yi wanka tare da ɗauro alwala ta daura tawul ɗin da ta fito.
Ganin ya yi bacci yana jan rago ya sanya ta lallaɓa ta ɗaya kansa ta ɗauki key ɗin ɗakin.Buɗewa ta yi ta fice tana takaicin rayuwarsa, don ta san da kyar ya yi wankan sai gobe in zai fita aiki ya yi.
Daki ta koma ta gyara musu kwanciya, ta mike tare da sanya rigar sallarsa ta shinfiɗa dadduma.
Sallah ta fara yi. Raka'a biyu ta yi bayan ta isar sai ta mayar da kanta ta rinƙa fadin,"La'ilaha illa anya subuhanaka.inni kuntu minaz zzalimin." Har sau arba'in da ɗaya, sannan ta yi wa Allah kirari tana kuka, da ya shirya mata mijinta ya zaunar da su lafiya.
Haƙiƙa Ummar Faruk miji ne na nuna wa tsara. Yana da kyau daidai shi. Dogo ne amma ba shi da haske sosai. Sannan yana da jiki na maza hali ne kawai ba shi da shi. Sai shegen son 'yan mata duk da cewar yana da maƙo, amma yana sakin ma 'yan matansa.
Ba ta tashi daga daddumar ba, sai da ta aka kira sallar asuba, sannan ta miƙe ta yi Raka'atul fijr ta sallame tare da yin sallar asuba.
"Umma na tashi." Hairan ta ce tana miƙa da salati.
"Good girl, then go and brush your teeth."
"Ok, Umma." Ta ce tare da wucewa cikin bayin.
Bayan ta yi brush ta yi alwala, sannan ta fito ta shinfiɗa karamar daddumarta ta yi sallah.
"Ummu, good morning?"
"Morning baby how are you?" Ta ce mata tare da rungume ta.
"Am fine Umma."
"Good, mu koma bacci kafin gari ya waye ina da lecture zuwa ten, kuma test za mu yi, ina shirya na kaiku school sai na dawo na gyara gidan na tafi ko?"
"To umma, I wish you all the best."
"Thanks babyna. Allah ya yi wa rayuwarmu albarka." Ta ce tana shafa ka kansu tare da tofa musu addu'a.
Yaran sune duniyarta, a dalilin su take rayuwa a gidan ubansa, domin ta san matuƙar ta rabu da mahaifinsu rayuwarsu da na ta sun shiga garari. Wannan dalilin ya sanya ta ke jure duk ɗaci da uƙubar zaman gidan ubansa don ta tallafi rayuwarsu. Tana ƙoƙarin ba su tarbiyya ta gari, a yadda take son su yi karatun boko ko Hausa ba ta cika yi musu ba. Sannan tana kula da karatun Muhammadiya ta su. Da kyar da taimakon Allah ta sanya mahaifiyar Faruk, ta tilasta shi ya sa ya su a makarantar boko mai tsada da islamiya da hadda. Ga shi yarinyar kwanyarta na ja, don tana da wayo wani lokacin maganar da take yi ya girmi shekarunta. Kuma duka shekararta uku.
"Umma, zan je na gaida Abba." Ta ji yarinyar tana faɗi tare da ƙoƙarin sauka daga gadon.
"Karki damu ya yi sallah, ya kwanta kin san in ya yi sallah sai tara yake tashi." Ta yi mata ƙaryata hakan tare da mayar da ita ta kwanta.
"Mu yi bacci in muka tashi sai ki gaishe shi."
"Ok,".Ta ce tare da kwanciya.
Ƙarfe baccin awa ɗaya ta yi, ta tashi dama akwai wuta ta sanya ruwa a kettle. Ɗaukar ruwan ta yi ta yi musu wanka sannan ta shirya su.
Ragowar abincin ta ɗumama ta saka mata a kula sannan ta zuba mata ta ci.
"Umma, don Allah ki daina sa mini ɗumame lalacewa ya ke yi kafin na ci. Kuma 'yan ajinmu bobo da biskit suke zuwa da shi."
"Ba na gaya miki ki daina sa ido kan abin da suka zo da shi ba?"
"Sorry Umma."
"Good girl. Na ce miki ina gama makaranta na samu aiki zan rinƙa siya miki duk abin da kike so."
"To, Umma Allah ya taimaka ya sa ki gana kuma ki samu aikin."
"Amin." Ta ce tana kallonta tana murmushi.
"Bari na rinƙa sa miki abincin a roba kar ya lalace, sannan kuma mu je shagon Dauda na siya miki biskit guda ɗaya."
Ɗaya mata kanta ta yi sannan ta ci gaba da cin abincin.
Kallonta take yi cikin tausaya wa, ganin mahaifinta na da halin da zai siya nata duk abin da take so, amma tsabar maƙonsa da son abin duniya, tare da rashin girmama yaran ya sanya shi ƙin siya mata.
Kasancewar babu wani tafiya tsakanin gidansu, da makarantar ba ta jima ba suka isa.
Miƙa mata biskit ta yi tare da kama hannunta." Ga shi ko kawo jakarki na sanya miki. Ki ci kin ji sam kar ki roki kowa, in kuma kika yi haka aljanuna za su faɗa mini."
"To ba zan riƙa ba ai na daina tun da kika ce babu kyau."
"Yauwa, Allah ya yi miki albarka ya ba ki ilmi mai amfani." Ta karashe maganar tana ɗaga mata hannu ganin ta shige cikin makarantar.
Bayan ta dawo a gauguace ta gyara gidan ta shiga wanka. Ba ta jima ba ta fito ta sanya doguwar rigarta tare da rolling ɗin ɗankwalin abayar ta dauki jakarta da littafanta.
"Wannan dalilin ya sanya nake son na kammala digirina, na samu aiki ko da koyarwa ce a private."
"A tunani ki kuma sai na bar ki ko?"
"Haba Abban Raihan sam ba ka yi wa rayuwata adalci ba, matukar ba ka bar ba, ai ba za ka hana ni nema ba. Kana ganin iyayena basu da shi mahaifiyata tana fama da jinya."
"Ni na ɗora mata? Tun da bani bane sai ki shafa mini lafiya. Ko da yake cigaba da karatun ma yana ƙila wa ƙala, tun da ɗan iya da ya sa ya ki shi ma ya kasa biya."
Gabanta ne ya faɗi tuna haka wanda hakan hawaye ya wanke mata fuska.
"Allah zai taimaka mini ba zai barni ba, tun da ya ga ina son karatun."
"Aci gaba in iska na hura wuta." Ya ce sai kuma ya kalleta ya ce,"Nasreen, za ki bani hakkinsa ko na je titi na nema? Tun da ga mata nan masu kyau waɗanda suka fiki."
"Ka je ba zan bayar ba wannan kai da Allah."
"Ke kuma wutarki daban ce, don in har Ina sama kina can ƙasa-ƙasa. Kina sane da Allah da Mala'iku suna tsine miki. Ki rinƙa buɗe murya kina karatun qur'ani ke a dole malama. Ƙiri-kiri ko bancin kirki ba kya bari na yi, amma in har na kawo buƙata ta sai ki koma kamar ba musulma ba."
Kallonsa ta yi cikin tsananin mamaki jina bin da yake faɗi."Dama ai ba ka nuna ilmin ka sai anan gurin, ni kuma ka ji na rantse in har ba za ka rinƙa yin soyayya ba, wallahi ba zan lamunta ba."
"Kin amince na kunna miki mu kalla sannan mu yi soyayyar? Domin ni sha'awarki kwata-kwata ba na ji."
"Allah ya kyauta! Ubangiji ya tsare ni da kallon surar wasu kai ma ina maka addu'ar ka daina domin babu kyau.
"Ashe jiki zai yi tsami." Ya ce tare da sanya hannunsa ya haɗata da jikinsa da ƙarfi.
Hannu ta sanya ta ture shi ta sanya kuka.
"Nasreen zan ci ubanki wallahi zan miki dukan tsiya a dakin nan!"
"Don Allah Abba, karka dake ta." Ya ji muryar Hairan tana faɗin haka.
Tsaki ya ja yana kallonta cikin takaici.
"Kina ganin abin da kike mini ko? Ba gaya miki za ki rinƙa kwana a ɗakina, amma wallahi ba da yarannan ba. In kin amince ki tashi mu je."
"Ni kuma ba zan bar yarana ba ƙanana saboda kai. Yarannan fa 'ya'yanka ne ba agola na taho da su ba."
"Ina ruwana ko daga jiki a suka fito. Ni wallahi yarannan suna ɗaya daga cikin abin da yasa na ƙara tsanarki. Duka shekararmu huɗu da aure, amma kin tara mini 'ya'ya biyu. Kin ji na rantse miki wallahi na ganki da ciki sai dai ki haifa a gidanku, tun da kin ƙi yin tsarin iyali."
"Ni ba zan kashe kaina ba, ai akwai na maza ka je ka yi mana. Sai ni? Da ba ni da gata, kuma 'ya'ya rahama ne wani na nema da kuɗin da bai samu ba."
"Ki je ki basu duk na yafe musu, ba ni buƙata saboda ina cikin tashen ƙuruciyata, ba za ki tara mini 'ya'ya ba ki tsigar da ni."
"Ka ji tsoron Allah kai ka ganni kana so ba tushe aka yi maka ni ba."
"Na yi dana sani saboda ba ki dace da ni ba. Sam da na san haka kike da ƙafiya da taurin kai babu abin da zai sanya na siyo ciwon kai na kawo gidana, kuma wallahi in har ba ki canza ba, kina gab da shiga cikin layin zawarawa don ba zan ɗauki iskanci ba."
Gabanta ne jin abin da ya ce, sai ta yi shiru can kuma cikin muryar kuka ta ce,"Allah shi ne gatana."
"Ni kuma ki ce sheɗan ne gatana in kin so." Ya ce tare da ɗaukar ta can ya yi ɗakinsa.
Tana kuka tana dukan ƙirjin shi, amma bai kula ba sai da ya biya buƙatar ta kamar yadda ya saba, sannan ya koma ya kwanta yana sauke numfashi.
"Allah ya saka mini ni da 'ya'yana."
"Ki fito kai tsaye ki zage ni." Ya ce tare da rufe idanunsa sai bacci.
Ita kuwa ta kasa yin bacci tana jin yadda Musaddik ya ke kuka yana faɗin,"Umma, fo." Wanda hankalinta ya ƙara tashi amma babu yadda za ta yi.Hankalinta ya kwanta jin Hairan ta sanya shi a fon.Miƙewa ta yi ta, shiga bayi ta yi wanka tare da ɗauro alwala ta daura tawul ɗin da ta fito.
Ganin ya yi bacci yana jan rago ya sanya ta lallaɓa ta ɗaya kansa ta ɗauki key ɗin ɗakin.Buɗewa ta yi ta fice tana takaicin rayuwarsa, don ta san da kyar ya yi wankan sai gobe in zai fita aiki ya yi.
Daki ta koma ta gyara musu kwanciya, ta mike tare da sanya rigar sallarsa ta shinfiɗa dadduma.
Sallah ta fara yi. Raka'a biyu ta yi bayan ta isar sai ta mayar da kanta ta rinƙa fadin,"La'ilaha illa anya subuhanaka.inni kuntu minaz zzalimin." Har sau arba'in da ɗaya, sannan ta yi wa Allah kirari tana kuka, da ya shirya mata mijinta ya zaunar da su lafiya.
Haƙiƙa Ummar Faruk miji ne na nuna wa tsara. Yana da kyau daidai shi. Dogo ne amma ba shi da haske sosai. Sannan yana da jiki na maza hali ne kawai ba shi da shi. Sai shegen son 'yan mata duk da cewar yana da maƙo, amma yana sakin ma 'yan matansa.
Ba ta tashi daga daddumar ba, sai da ta aka kira sallar asuba, sannan ta miƙe ta yi Raka'atul fijr ta sallame tare da yin sallar asuba.
"Umma na tashi." Hairan ta ce tana miƙa da salati.
"Good girl, then go and brush your teeth."
"Ok, Umma." Ta ce tare da wucewa cikin bayin.
Bayan ta yi brush ta yi alwala, sannan ta fito ta shinfiɗa karamar daddumarta ta yi sallah.
"Ummu, good morning?"
"Morning baby how are you?" Ta ce mata tare da rungume ta.
"Am fine Umma."
"Good, mu koma bacci kafin gari ya waye ina da lecture zuwa ten, kuma test za mu yi, ina shirya na kaiku school sai na dawo na gyara gidan na tafi ko?"
"To umma, I wish you all the best."
"Thanks babyna. Allah ya yi wa rayuwarmu albarka." Ta ce tana shafa ka kansu tare da tofa musu addu'a.
Yaran sune duniyarta, a dalilin su take rayuwa a gidan ubansa, domin ta san matuƙar ta rabu da mahaifinsu rayuwarsu da na ta sun shiga garari. Wannan dalilin ya sanya ta ke jure duk ɗaci da uƙubar zaman gidan ubansa don ta tallafi rayuwarsu. Tana ƙoƙarin ba su tarbiyya ta gari, a yadda take son su yi karatun boko ko Hausa ba ta cika yi musu ba. Sannan tana kula da karatun Muhammadiya ta su. Da kyar da taimakon Allah ta sanya mahaifiyar Faruk, ta tilasta shi ya sa ya su a makarantar boko mai tsada da islamiya da hadda. Ga shi yarinyar kwanyarta na ja, don tana da wayo wani lokacin maganar da take yi ya girmi shekarunta. Kuma duka shekararta uku.
"Umma, zan je na gaida Abba." Ta ji yarinyar tana faɗi tare da ƙoƙarin sauka daga gadon.
"Karki damu ya yi sallah, ya kwanta kin san in ya yi sallah sai tara yake tashi." Ta yi mata ƙaryata hakan tare da mayar da ita ta kwanta.
"Mu yi bacci in muka tashi sai ki gaishe shi."
"Ok,".Ta ce tare da kwanciya.
Ƙarfe baccin awa ɗaya ta yi, ta tashi dama akwai wuta ta sanya ruwa a kettle. Ɗaukar ruwan ta yi ta yi musu wanka sannan ta shirya su.
Ragowar abincin ta ɗumama ta saka mata a kula sannan ta zuba mata ta ci.
"Umma, don Allah ki daina sa mini ɗumame lalacewa ya ke yi kafin na ci. Kuma 'yan ajinmu bobo da biskit suke zuwa da shi."
"Ba na gaya miki ki daina sa ido kan abin da suka zo da shi ba?"
"Sorry Umma."
"Good girl. Na ce miki ina gama makaranta na samu aiki zan rinƙa siya miki duk abin da kike so."
"To, Umma Allah ya taimaka ya sa ki gana kuma ki samu aikin."
"Amin." Ta ce tana kallonta tana murmushi.
"Bari na rinƙa sa miki abincin a roba kar ya lalace, sannan kuma mu je shagon Dauda na siya miki biskit guda ɗaya."
Ɗaya mata kanta ta yi sannan ta ci gaba da cin abincin.
Kallonta take yi cikin tausaya wa, ganin mahaifinta na da halin da zai siya nata duk abin da take so, amma tsabar maƙonsa da son abin duniya, tare da rashin girmama yaran ya sanya shi ƙin siya mata.
Kasancewar babu wani tafiya tsakanin gidansu, da makarantar ba ta jima ba suka isa.
Miƙa mata biskit ta yi tare da kama hannunta." Ga shi ko kawo jakarki na sanya miki. Ki ci kin ji sam kar ki roki kowa, in kuma kika yi haka aljanuna za su faɗa mini."
"To ba zan riƙa ba ai na daina tun da kika ce babu kyau."
"Yauwa, Allah ya yi miki albarka ya ba ki ilmi mai amfani." Ta karashe maganar tana ɗaga mata hannu ganin ta shige cikin makarantar.
Bayan ta dawo a gauguace ta gyara gidan ta shiga wanka. Ba ta jima ba ta fito ta sanya doguwar rigarta tare da rolling ɗin ɗankwalin abayar ta dauki jakarta da littafanta.