Sashe 19
Wasu Mazan Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Harararta ya yi, sai kuma ya shigo da motar.
"Sannu da zuwa." Ta ce masa bayan ta buɗe masa motar.
"Nasreen, ba na hana ki shiga maƙota kuma suna na hana su shigowa ba, don kin san bana son gulma da munafunci?.
"Ka yi hakuri Maman Muwaddat ce."
"Ita ɗin fa tun da ba ciki ɗaya kuka fito ba." Ya ƙarashe maganar tare da fita. Gaban motar ta shiga, ta kwashi kayan da ya shigo da ita.
Gabanta ne ya faɗi ganin sabbabin kaya masu tsananin kyau a bayan motarsa. Hannu ta ɗauko tana kallon kayan, duk da cewar ta san yana kashe wa kansa kuɗi, amma ɗinkin da ta ga ya yi sabbabi, sai da suka sanya kanta ya juya, saboda kayan sun yi kala bakwai.
Jikinta babu ƙarfi ta shigo da su. Yana zaune a falo ta shigo da kayan. Ɗakinta ta kai ta dawo ta wuce da cefanen da ya yi musu.
Ƙaramin tsuka ya ja ya shiga cikin ɗakin. Bayan ta kammmala girkin ta ɗauka ta kai masa. Tana ƙoƙarin shiga cikin ɗauki da ta ji muryarsa yana waya. Da sauri ta fasa murɗa ƙofar ta laɓe don ta tabbatar da zargin ta.
Dariya mai sauti ta ji ya yi, sannan ya faɗi wata magana wacce sai da ta ji kishinsa, saboda batsa da ta ji yana yi a cikin wayar. Kalamansa na ƙarshe, ya sanya ta ji kamar za ta faɗi ta kuma fara tabbatar da zargin ta.
"Sai ta shigo gidansa ya kwanta da ita zai tabbatar da ya auri mace? Faruk aure zai ƙara ba tare da ya sanar mini ba?" Ta yi wa kanta tambayar cikin tashin hankali, yayin da idanunta suka ciko.
"Innalillahi na shiga uku!" Ta ce bayan ta ije tiren abincin kanta na juyawa. Da ƙyar ta samu ta daidaita kanta ta shiga ciki, tunawa da ta yi dama ya sha faɗan, sai ya ƙara aure kuma ga shi har sun ɗauki shekaru bai ƙara auren ba. Ta gaya wa zuciyarta hakan ne don kawai ta yaudareta ta samu kwanciyar hankali, amma cikin zuciyarta tana ƙarfafa mata aure zai ƙara.
Yana wayar ta yi sallama ta shigo. Bai fasa wayar ba, sai ƙasa da murya da ya yi. Ganin haka ta ije masa abincin ta fice cikin tsananin damuwa.
Satan kallonsa ta yi da zata fita. Tana matuƙar son mijinta domin ta ko' ina Faruk ya kai namijin da mace za ta damu da shi. Halinsa ne kawai bai yi ba, na rashin ɗaukar mace da daraja. Ko da yake ba za ta ce baya ɗaukar mace da daraja ba, ita ce kawai ba ya daraja ta, duba ga yadda yake waya da 'yan mata yana kashe murya.Ɗaki ta koma ta zauna sai kawai ta tsinci fashewa da kuka.
Makaranta innsha Allahu yau zan yi posting safe da yamma a cigaba da surbubuɗo comments ❤️❤️❤️❤️💃💃💃💃
WASU MAZAN" Labari ne a kan rayuwar Nasreen wacce ta haɗu da jarrabawar rayuwa. Nasreen tasha jarrabawa a rayuwar aurenta da Faruk. Wanda faruwar haka yana da nasaba da rashin bango mai kyau abin jingina da ba ta samu ba, wato mahaifinta da ya kasa cike gurbin da ya kamata ya cike. Rayuwar aurenta madubi ne ga wasu matan da suke shan wahala ko rashin sama lafiya da mazajensu. Duk da ƙoƙarin su na son su zauna a ɗakinsu don gudun ZAWARCI da kuma fargabar rayuwar 'ya'yansu yadda za su kasance in ba su, da kuma fargabar mijin da za su aura bayan aurensu ya mutu. Wannan dalilin ya sanya ta jure zaman gidan aurenta don ta samu ta rayu da 'ya'yanta. Sai dai ƙaddara ba ta wuce mutum dole afkuwarsa tabbataciyace tun da Ubangiji ya tsara tun a Lauful Mahfuz. Duk yadda ta so ta kaucewa ƙaddara faruwar hakan ya ci tura. Ta shiga cikin tsananin rayuwa da fidda tsammani. Ta haɗu da wacce ta kira hasken da ya haska fitilar rayuwarta, amma sai dai a garin ta kawo hasken, ta sanya rayuwarta cikin tsarƙaƙiyar da ya zama tsarƙen da ya jefa rayuwar ta cikin tsarƙaƙiyar soyayyar mai kama da ƙiyayya. Sai dai Ubangiji ya faɗa a cikin littafinsa mai tsarki cewar,"Duk tsakani, akwai sauƙin." Haka ta kasance a lokacin da ta fidda tsammani a cikin rayuwarta, sai Allah ya kawo haske mai walƙiya da ya canza tubalin ƙaddararta da ga duhu zuwa haske. Ta kuma sha ruwan zuman da take tunanin ba za ta taɓa shan sa ba, bayan ta kwankwaɗi na maɗaci, wanda ya gauraye dukkan rayuwarta har ta fidda tsammanin shan zuma. A cikin littafin akwai wata irin soyayya mai tsuma zuciya. Masoyana karku sake a baku labarin littafin "WASU MAZAN" Domin na wasa ƙwaƙwalwa ta na zauna na tsara shi ta yadda zai sa ya ku tausayi da nishadi har ma ya zama darasi. Ku kasance masu bibiyar littafin domin jin yadda tubalin ginin rayuwarta zai kasance. Kun san dai alkalamin Jamila lawal Zango ba ya rubuta shirme.
FOR WHATSAPP: 07072971093
CALL: 008144072423
Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/KusyXgwh9wEAHDTn6dzD43
*WASU MAZAN*
NA
*JAMILA LAWAL ZANGO*
*FIRST CLASS WRITERS*
MARUBUCIYAR
Sakacina ko halin maza
Kura da fatar akuya
Ranar wanka...
And now
Wasu mazan
08144072423
PAGE 12
BISMILLAHIR RAHMANINR RAHIM
Sosai ta yi kuka tana baƙincikin rayuwar da suke yi da Faruk. Tunani take yi wane irin zama za su yi, da matar da zai auro don ta san ya riga ya gama zubar mata da ƙima a gurinta.
Bayan fitarsa ta aiki Raihan ta kira Maman Muwaddat. Ba ta jima ba suka dawo da Raihan. A yadda ta ganta a firgice, ta ɗauka ya gaya mata. Kallonta ta yi cikin tausaya.
"Ina jinki kin ce za mu yi wata magana, kuma na lura ke kanki ba kyau son faɗin maganar." Tausayi ta bata sosai tana mamakin mugun halin Faruk. Haba ai zalunci ne ace zaka yi wa mace kishiya ka ƙi sanar da ita.
"Nasreen, hakuri zan ba ki a rayuwarki. Na san cewa kina cikin wani hali na zaman ki da mijinki, amma yanzu dole ƙi ƙara saboda..."
"Saboda zai ƙara aure ko?" Ta furta tambayar hawaye yana shatata a fuskarta.
Dafata ta yi ganin yadda ta rikice."Ya gaya miki ne?"
"A'a bai gaya mini ba, ji na yi yana waya cewar yanzu zai san ya auri mace. Maman Muwaddat mai na yi wa Faruk, wanda ya zaɓi ya shigo cikin rayuwata ya cutar da ni? Don zai yi aure sai ya sanar da amaryarsa ba ni da ƙima a idanunsa. Da wane ido yake so ta kalle ni. Hakan da yake yi ya ba ta ƙofar da zata ɗauke ni mara daraja a idanunsa. In har ba zai yi mini kayan faɗar kishiya ba, na cancanta ya sanar da ni ko da ace ba zai rarrashe ni ba." Kuka take yi sosai tana ji tamkar zuciyarta za ta fito.
"Ki yi hakuri Nasreen, haka WASU MAZAN suke yi. Ba ke kaɗai aka yi wa hakan ba, domin mata da yawa mazajensu na ƙara aure ba tare da sun gaya musu ba, kuma in suka yi haƙuri sai kiga komai ya wuce. Ki ɗauki kishiyar da zuciya ɗaya kuma ki riƙe Allah."
Sosai take yin kuka tana jin bai yi mata adalci ba. Hawaye ta share tana kallonta."Na gode da sanar mini da kika yi, kuma na gode da shawarki. In sha Allahu zan haƙura na barwa Allah komai."
"Yauwa dama na san za ki jure ki ci gaba da hakuri Allah yana tare dake." Ta ce mata cikin tausayawa. Ta daɗe a gidan tana ba ta baki har sai da ta ɗan ji dama, sannan ta yi mata sama ta tafi.
Tana fita ta ƙara sakin kuka ta shige cikin ɗakinta. Ƙoƙari kawai ta yi ta daure ta nuna mata ta haƙura, amma Allah kaɗai ya san zafin da take ciki. Tayi kuka sosai har sai da ta ji hawayen sun daina zuba, sannan ta haƙura ta ɗauki maganin damuwar ta ta fara karantawa.
Sai da ta ji ɗan dama ta shiga kicin ta ɗora abinci. Tana tsaye a kicin ɗin tun da ta ɗora ruwa ta kasa yin komai. Zuciyarta take tafasa da wani irin abu na kishin mai kama da ƙwallo ya taso mata kuma ya ƙi wucewa. Ita kanta ba ta san tana mugun sonsa ba sai yanzu. Tana tsaye har ruwan ya tafasa.
"Umma ruwan yana tausa." Ta ji muryar Raihan da take tsaye tana rike da hannunta. A maimakon ta wanke shinkafar ta zuba, sai kawai ta ɗauki ruwan zafin ta zuba a cikin ɗanyar shinkafar, ta sanya hannu don ta wanke. Tsananin zafin da ta ji ya farga da ita abin da ta yi. Da sauri ta cire hannunta tare da sanya ƙara tana salati. Hannu ta da ya tashi ya yi ja take dubawa hawaye yana zuba a ƙuncinta.
"Umma, kin ƙone ne?" Raihan ta ce mata tana kallon hannunta.
Tsintar kanta ta yi da rungumeta tana kuka sosai da kuma ƙarfi. Tuna shinkafar za ta iya lalacewa ya sa ya ta yi saurin sakinta ta mayar da shinkafar da ruwan kan wuta. Bisa abin da ya faru kan dole ta tafasa sannan ta zubar da ruwan ta girka abinci. Hawaye kawai take sharewa. Cikin dare da ta kwanta ta kasa bacci. Har ya dawo idanunta biyu.
Saboda haushinsa da take ji bayan ta buɗe masa get. Wucewa ɗakinta ta yi, ba tare da ta kalle shi ba, saboda mugun haushinsa take ji. Raka ta da idanu ya yi ganin yadda take. "Ko an gaya mata ne?" Ya yi wa kansa tambayar cikin rashin damuwa. Tsaki ya yi tare da ɗaga kafaɗunsa alamun bai shafe shi ba.
Shiga cikin ɗakinsa ya yi, bayan ya yi wanka ta fito da naman da siyo, ya ci ya ƙoshi ya kira da lemunsa ya kwanta. Rintse idanunsa ya yi yana ta ayyana surar Rashida da fanshe kuɗinsa da zai yi.
"Sannu da zuwa." Ta ce masa bayan ta buɗe masa motar.
"Nasreen, ba na hana ki shiga maƙota kuma suna na hana su shigowa ba, don kin san bana son gulma da munafunci?.
"Ka yi hakuri Maman Muwaddat ce."
"Ita ɗin fa tun da ba ciki ɗaya kuka fito ba." Ya ƙarashe maganar tare da fita. Gaban motar ta shiga, ta kwashi kayan da ya shigo da ita.
Gabanta ne ya faɗi ganin sabbabin kaya masu tsananin kyau a bayan motarsa. Hannu ta ɗauko tana kallon kayan, duk da cewar ta san yana kashe wa kansa kuɗi, amma ɗinkin da ta ga ya yi sabbabi, sai da suka sanya kanta ya juya, saboda kayan sun yi kala bakwai.
Jikinta babu ƙarfi ta shigo da su. Yana zaune a falo ta shigo da kayan. Ɗakinta ta kai ta dawo ta wuce da cefanen da ya yi musu.
Ƙaramin tsuka ya ja ya shiga cikin ɗakin. Bayan ta kammmala girkin ta ɗauka ta kai masa. Tana ƙoƙarin shiga cikin ɗauki da ta ji muryarsa yana waya. Da sauri ta fasa murɗa ƙofar ta laɓe don ta tabbatar da zargin ta.
Dariya mai sauti ta ji ya yi, sannan ya faɗi wata magana wacce sai da ta ji kishinsa, saboda batsa da ta ji yana yi a cikin wayar. Kalamansa na ƙarshe, ya sanya ta ji kamar za ta faɗi ta kuma fara tabbatar da zargin ta.
"Sai ta shigo gidansa ya kwanta da ita zai tabbatar da ya auri mace? Faruk aure zai ƙara ba tare da ya sanar mini ba?" Ta yi wa kanta tambayar cikin tashin hankali, yayin da idanunta suka ciko.
"Innalillahi na shiga uku!" Ta ce bayan ta ije tiren abincin kanta na juyawa. Da ƙyar ta samu ta daidaita kanta ta shiga ciki, tunawa da ta yi dama ya sha faɗan, sai ya ƙara aure kuma ga shi har sun ɗauki shekaru bai ƙara auren ba. Ta gaya wa zuciyarta hakan ne don kawai ta yaudareta ta samu kwanciyar hankali, amma cikin zuciyarta tana ƙarfafa mata aure zai ƙara.
Yana wayar ta yi sallama ta shigo. Bai fasa wayar ba, sai ƙasa da murya da ya yi. Ganin haka ta ije masa abincin ta fice cikin tsananin damuwa.
Satan kallonsa ta yi da zata fita. Tana matuƙar son mijinta domin ta ko' ina Faruk ya kai namijin da mace za ta damu da shi. Halinsa ne kawai bai yi ba, na rashin ɗaukar mace da daraja. Ko da yake ba za ta ce baya ɗaukar mace da daraja ba, ita ce kawai ba ya daraja ta, duba ga yadda yake waya da 'yan mata yana kashe murya.Ɗaki ta koma ta zauna sai kawai ta tsinci fashewa da kuka.
Makaranta innsha Allahu yau zan yi posting safe da yamma a cigaba da surbubuɗo comments ❤️❤️❤️❤️💃💃💃💃
WASU MAZAN" Labari ne a kan rayuwar Nasreen wacce ta haɗu da jarrabawar rayuwa. Nasreen tasha jarrabawa a rayuwar aurenta da Faruk. Wanda faruwar haka yana da nasaba da rashin bango mai kyau abin jingina da ba ta samu ba, wato mahaifinta da ya kasa cike gurbin da ya kamata ya cike. Rayuwar aurenta madubi ne ga wasu matan da suke shan wahala ko rashin sama lafiya da mazajensu. Duk da ƙoƙarin su na son su zauna a ɗakinsu don gudun ZAWARCI da kuma fargabar rayuwar 'ya'yansu yadda za su kasance in ba su, da kuma fargabar mijin da za su aura bayan aurensu ya mutu. Wannan dalilin ya sanya ta jure zaman gidan aurenta don ta samu ta rayu da 'ya'yanta. Sai dai ƙaddara ba ta wuce mutum dole afkuwarsa tabbataciyace tun da Ubangiji ya tsara tun a Lauful Mahfuz. Duk yadda ta so ta kaucewa ƙaddara faruwar hakan ya ci tura. Ta shiga cikin tsananin rayuwa da fidda tsammani. Ta haɗu da wacce ta kira hasken da ya haska fitilar rayuwarta, amma sai dai a garin ta kawo hasken, ta sanya rayuwarta cikin tsarƙaƙiyar da ya zama tsarƙen da ya jefa rayuwar ta cikin tsarƙaƙiyar soyayyar mai kama da ƙiyayya. Sai dai Ubangiji ya faɗa a cikin littafinsa mai tsarki cewar,"Duk tsakani, akwai sauƙin." Haka ta kasance a lokacin da ta fidda tsammani a cikin rayuwarta, sai Allah ya kawo haske mai walƙiya da ya canza tubalin ƙaddararta da ga duhu zuwa haske. Ta kuma sha ruwan zuman da take tunanin ba za ta taɓa shan sa ba, bayan ta kwankwaɗi na maɗaci, wanda ya gauraye dukkan rayuwarta har ta fidda tsammanin shan zuma. A cikin littafin akwai wata irin soyayya mai tsuma zuciya. Masoyana karku sake a baku labarin littafin "WASU MAZAN" Domin na wasa ƙwaƙwalwa ta na zauna na tsara shi ta yadda zai sa ya ku tausayi da nishadi har ma ya zama darasi. Ku kasance masu bibiyar littafin domin jin yadda tubalin ginin rayuwarta zai kasance. Kun san dai alkalamin Jamila lawal Zango ba ya rubuta shirme.
FOR WHATSAPP: 07072971093
CALL: 008144072423
Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/KusyXgwh9wEAHDTn6dzD43
*WASU MAZAN*
NA
*JAMILA LAWAL ZANGO*
*FIRST CLASS WRITERS*
MARUBUCIYAR
Sakacina ko halin maza
Kura da fatar akuya
Ranar wanka...
And now
Wasu mazan
08144072423
PAGE 12
BISMILLAHIR RAHMANINR RAHIM
Sosai ta yi kuka tana baƙincikin rayuwar da suke yi da Faruk. Tunani take yi wane irin zama za su yi, da matar da zai auro don ta san ya riga ya gama zubar mata da ƙima a gurinta.
Bayan fitarsa ta aiki Raihan ta kira Maman Muwaddat. Ba ta jima ba suka dawo da Raihan. A yadda ta ganta a firgice, ta ɗauka ya gaya mata. Kallonta ta yi cikin tausaya.
"Ina jinki kin ce za mu yi wata magana, kuma na lura ke kanki ba kyau son faɗin maganar." Tausayi ta bata sosai tana mamakin mugun halin Faruk. Haba ai zalunci ne ace zaka yi wa mace kishiya ka ƙi sanar da ita.
"Nasreen, hakuri zan ba ki a rayuwarki. Na san cewa kina cikin wani hali na zaman ki da mijinki, amma yanzu dole ƙi ƙara saboda..."
"Saboda zai ƙara aure ko?" Ta furta tambayar hawaye yana shatata a fuskarta.
Dafata ta yi ganin yadda ta rikice."Ya gaya miki ne?"
"A'a bai gaya mini ba, ji na yi yana waya cewar yanzu zai san ya auri mace. Maman Muwaddat mai na yi wa Faruk, wanda ya zaɓi ya shigo cikin rayuwata ya cutar da ni? Don zai yi aure sai ya sanar da amaryarsa ba ni da ƙima a idanunsa. Da wane ido yake so ta kalle ni. Hakan da yake yi ya ba ta ƙofar da zata ɗauke ni mara daraja a idanunsa. In har ba zai yi mini kayan faɗar kishiya ba, na cancanta ya sanar da ni ko da ace ba zai rarrashe ni ba." Kuka take yi sosai tana ji tamkar zuciyarta za ta fito.
"Ki yi hakuri Nasreen, haka WASU MAZAN suke yi. Ba ke kaɗai aka yi wa hakan ba, domin mata da yawa mazajensu na ƙara aure ba tare da sun gaya musu ba, kuma in suka yi haƙuri sai kiga komai ya wuce. Ki ɗauki kishiyar da zuciya ɗaya kuma ki riƙe Allah."
Sosai take yin kuka tana jin bai yi mata adalci ba. Hawaye ta share tana kallonta."Na gode da sanar mini da kika yi, kuma na gode da shawarki. In sha Allahu zan haƙura na barwa Allah komai."
"Yauwa dama na san za ki jure ki ci gaba da hakuri Allah yana tare dake." Ta ce mata cikin tausayawa. Ta daɗe a gidan tana ba ta baki har sai da ta ɗan ji dama, sannan ta yi mata sama ta tafi.
Tana fita ta ƙara sakin kuka ta shige cikin ɗakinta. Ƙoƙari kawai ta yi ta daure ta nuna mata ta haƙura, amma Allah kaɗai ya san zafin da take ciki. Tayi kuka sosai har sai da ta ji hawayen sun daina zuba, sannan ta haƙura ta ɗauki maganin damuwar ta ta fara karantawa.
Sai da ta ji ɗan dama ta shiga kicin ta ɗora abinci. Tana tsaye a kicin ɗin tun da ta ɗora ruwa ta kasa yin komai. Zuciyarta take tafasa da wani irin abu na kishin mai kama da ƙwallo ya taso mata kuma ya ƙi wucewa. Ita kanta ba ta san tana mugun sonsa ba sai yanzu. Tana tsaye har ruwan ya tafasa.
"Umma ruwan yana tausa." Ta ji muryar Raihan da take tsaye tana rike da hannunta. A maimakon ta wanke shinkafar ta zuba, sai kawai ta ɗauki ruwan zafin ta zuba a cikin ɗanyar shinkafar, ta sanya hannu don ta wanke. Tsananin zafin da ta ji ya farga da ita abin da ta yi. Da sauri ta cire hannunta tare da sanya ƙara tana salati. Hannu ta da ya tashi ya yi ja take dubawa hawaye yana zuba a ƙuncinta.
"Umma, kin ƙone ne?" Raihan ta ce mata tana kallon hannunta.
Tsintar kanta ta yi da rungumeta tana kuka sosai da kuma ƙarfi. Tuna shinkafar za ta iya lalacewa ya sa ya ta yi saurin sakinta ta mayar da shinkafar da ruwan kan wuta. Bisa abin da ya faru kan dole ta tafasa sannan ta zubar da ruwan ta girka abinci. Hawaye kawai take sharewa. Cikin dare da ta kwanta ta kasa bacci. Har ya dawo idanunta biyu.
Saboda haushinsa da take ji bayan ta buɗe masa get. Wucewa ɗakinta ta yi, ba tare da ta kalle shi ba, saboda mugun haushinsa take ji. Raka ta da idanu ya yi ganin yadda take. "Ko an gaya mata ne?" Ya yi wa kansa tambayar cikin rashin damuwa. Tsaki ya yi tare da ɗaga kafaɗunsa alamun bai shafe shi ba.
Shiga cikin ɗakinsa ya yi, bayan ya yi wanka ta fito da naman da siyo, ya ci ya ƙoshi ya kira da lemunsa ya kwanta. Rintse idanunsa ya yi yana ta ayyana surar Rashida da fanshe kuɗinsa da zai yi.