Sashe 48
Musayar Zuciya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
A true life story
*K.A.S Precious Hajja ce*
*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*
(Home of expert & perfect writer's)
*DEDICTEED TO:* Sanah Isma'il Matazu.
*VOTE me on wattpad @Hajjac*
*Shafin yau naki ne m sweet heart SOFIYYA GALADANCI, I love you Allah ya nuna mana ranar Auranki da rai da lafiya nasan ke ko...?
kawai dai Allah ya k'ara miki baseera dear Bari nayi tsit*
Page *38*
Alama yayi mata da hannu ta saki labulen da aka nannad'e aka d'ora akan k'ofar d'akin. Murmushi tayi tare da zaro idanuwa tana girgiza kai alamar a'a, ganin haka yasa shi matsawa yana kallon k'ofar ganin babu me kallonsa yayi saurin sauke labulen INdo tace.
"Kai.. Kai... Kai! ba ruwa na nidai Inna ce fa ta d'aga shi wai sabida akwai zafi."
Hannu yasa ya janyo ta kusa dashi yana kallon fuskarta, ya kaleta ya kalli Ayman a hankali ya kai bakinsa saman goshinta ya sumbace ta INdo tasa hannu ta bayansa ta rungume shi itama sannan ta kallesa tace.
"Ka zauna ka tsaya."
Hannunsa cikin nata suka zauna yana kuma rik'e da Ayman.
Kwantar da Ayman yayi a gefe kasan cewar yana cikin towel sannan ya juya yana kallon INdo wanda ke kallon k'irjinsa dan wani iri taji da yadda yake mata wani irin kallo.
"Sannu da zuwa, ya gurin su Mama?"
"Kin yi kyau cutie na, kinyi kamar ba me jego ba dan babu wani alamun da zai nuna hakan meye sirrin?"
"Inna ce."
Ta bashi amsa tana wasa da yatsun hannunsa yayi murmushi tare da matso da ita kusa dashi yana mak'alota jikinsa.
"Ko kawai ma idan zan wuce mu tafi tare tunda kun gama wanka ai kin fara sallah ma ko cutie?"
INdo ta zaro idanuwa tana kallansa yayi murmushi yana d'aga mata girarsa kafin yaji tace.
"Ta6... In bikafa kace? So kakeyi insha zagi kenan a cikin garin nan, kasan mu bazan koma gidan ka ba dole sai an yi garar barka sannan za'a maida ni."
Kallonta yayi cikin rashin fahimtar maganarta ta sannan ta d'an zame ta janyo kayan abincin ta tsiyaya mai lemo ya kar6a har yana cewa.
"Cutie ban gane abinda kike nufi bane wace irin garar suna? Kuma wazai kai? Wa za'a bawa.?!"
"Kayan abinci ne ake kawowa gidan su me jego,su anan sun maida hakan kamar ibada dan haka idan miji be yi ba sai abin ya zama gori har jikokin mutum."
"Ikon Allah, Allah guda d'aya amma garuruwa daban-daban ni ban ta6a ji ba koda wasa wallahi. Toh idan kuma mijin bashida halin yi fa sai ayi ya ya cutie?"
INdo tana gyara k'afar Ayman ba tare da ta kallesa ba tace.
"Idan miji beyi miki ba shikenan sai a rabu dashi baza a mayar da ita ba. Idan aka ga ya takura da zaryar zuwa gidan su kuma sai ad'auke ta a kaita inda bazai sake ganinta ba har sai ya kawo kayan."
Sosai mamaki ya cika masa zuciya, lallai akwai d'inbin gyara a cikin kauyan nan amma banda haka ya za'ayi a hana miji matarsa akan abinda ba alkurani bane ya wajabta shi ba. Lallai yadda ya k'agu ta koma su tafi kwara state tare dole yaje a harhad'o a kawo,yarinyar tayi tsada da yawa daga wannan sai ace maka wannan.
"In zuba maka yanzu ko sai kayi sallan azahar naga an kusa kirawo wa."
"Bari sai nayi sallah cutie, dawo nan in dinga jin duminki a jikina."
Matsawa tayi ya rungumeta, yana yawo a jikinta da hannunsa ita kuma ta lumshe ido tana sauraransa. Sallamar su Uwani suka jiyo Sadeeq yayi saurin zame hannunsa daga jikinta yana yatsina fuska yace..
"Su waye?"
"Inajin su Maryam ne naji muryar su da Uwani da Sahura."
"Kai nashiga uku ni Sadeeq, wai hardasu nake aure ne da kullum na shigo garin nan sai sunzo sun samin ido? Ko 'yan uwanku ne cutie?"
"A'ah k'awaye nane amma kuma su haka suke duk inda sukaji labarin wani abun tofa sai ka gansu sabida dama ba wani tambayar miji fita suke yi ba."
"Ai munafukai ne wallahi."
Ya fad'a a kufule kafin ya matsa sun shigo cikin d'akin bakunansu a washe.
Zama suka yi daga bakin k'ofar amma hakan be hana warin ranar jikinsu da kaurin icen girki shiga cikin hancin Sadeeq ba ya tuna da tuni itama INdon haka take amma Allah ya d'aukaka ta.
Da kyar ya amsa musu a ciki-ciki sabida yadda suke kallansu suna rik'e ha6a sabida sunga sun manne jikin juna.
"Cutie zanyi alwala."
"Okey toh bari akawo ruwa k'ofar gida, ko zaka yi anan ciki."
"A'ah Inna na nan da dai bata nan sai nayi."
Tashi yayi suka d'an ra6e ya wuce sannan INdo ta fito suma suka bita a baya, tunda tazo gida suke bibiyarta ganinta suke tamkar Matar wani shugaban me rik'e da wani muk'amin.
Ruwa ta zuba tasa mayafi takai mai wajan mota sannan ta koma ciki.
Hira suka farayi dasu har aka idar da sallah Sadeeq ya dawo daga massalaci dan har tsayawa yayi suka d'anyi hira da principal d'in tsefawa makarantar su INdo daya bari.
Nafeesah ce ta kuma fita ta shigo dashi sannan INdo ta bishi su kuma su Uwani suka ci gaba da hira da Inna duk da bata cika sanya musu baki ba.
"Cutie Ina baby na kika kaishi?"
"Inna ta goyashi ko na kar6osa?!"
"Ah no kyalesa kar ace nayi rashin kunya."
Waina ta zuba masa da miya sannan ta matsa kusa dashi, had'e hannuwa yayi a k'ijinsa tare da bud'e baki alamar ta bashi da kanta.
Murmushi tayi tana girgiza kai ta fara bashi kunnuwansa har motsawa suke yi sabida yadda miyar tayi mai dad'i idan ta bashi sau d'aya itama sai ya tura mata wanda ta kuma d
ebowa yasa mata a baki haka suka dinga yi har suka kusa cinyewa yace ya k'oshi.
"Cutie gaskiya ranar Sunday zaki koma zanyi duk iya yadda zanyi na tabbatar da an kawo kayan nan, sannan direct za'a wuce dake can gidan marigayi acan zaki ci gaba da zama an raba gado Abba yace idan kin koma zaizo yayi miki bayani kinji.?!"
Kifta idanuwa ta shiga yi alamar hawaye take son karsu fito ya janyo ta tare da kamo fuskarta yana san saka kwayar idanunsa cikin nata.
"Karki zubar min da hawaye kinga nima ina tattala nawa, keda ma ba'ayi miki da yawa ba tunda an baki me kamadashi iri d'aya sak sannan kina cikin zuciya ta kamar rai. Ni kuwa tare muka taso mu kwana tare muyi fad'a mu shirya ba tare da kowa ya sani ba, shine ni nine shi amma yau babu shi."
"Ka d'auka kaima a ranka nice shi tunda dama silarsa ce ta sa muka zama abu d'aya dakai, na zame maka shi kaima karka sake yin kuka mun riga munyi *MUSAYAR ZUCIYA* ni da kai fatana a yanzu shine na zama tauraruwa kamar yadda yake so yaga na zama kayi min addu'a malama Hannatu tace addu'ar miji akan matarsa tana saurin kar6owa."
Bakinsa da yake ta motsi tun d'azu shi ya zura cikin nata cikin wani mugun tausayinta da wata azababbar kaunarta da soyayyarta da ta taso mai. Kissing d'in ta yake cikin wani irin salo wanda yasa INdo ta kasa gane kansa, ya shagala kawai suka ji muryar malam Hamza a tsakar gida amma Sadeeq ji yayi tamkar a tsakiyar d'akin yayi sabida tsabar tsoro.
"Na tafi cutie kar nayi abun kunya a gidannan a d'akin baba dan naga kema ba hanani zaki ba."
Dariya INdo take yi sosai wanda tasa Sadeeq kallonta yana hararata dan har rik'e ciki takeyi ya matsa can bakin k'ofa-k'ofa tare da maida hularsa yana jiran shigowar malam Hamza d'akin dan yaji Inna tana cewa suna ciki.
"Matsoraci kawai Abu Ayman, uhm...uhm..uhm.."
INdo ta fad'a cikin dariya ya juya yana mata gwalo shima. muryar malam Hamzan yaji a bakin k'ofar Sadeeq yayi saurin d'aga labulen ita kuma INdo ta fara matsar da kayan da suka ci abinci kamar masu gaskiya.
"Baba sannu da shigowa, gashi duk mun tsare maka d'akin."
Sadeeq ya fad'a yana gyara zama tare da turo hula gaba yana kuma mai da ita baya alamar kunya ya keji.
Malam Hamza yayi dariya tare da k'arasawa cikin d'akin ya zauna a bakin gadon sa yana cewa ba komai Gaidashi Sadeeq yayi cike da girmamawa har suka d'an fara hira ita kuma INdo ta kwashe kayan ta fita dasu can su Uwani aka ci ragowar ana jinjinawa INdo ganin duk da kud'inta tayi wannan shagalin.
Malam Hamza da Sadeeq sun jima suna hira kafin malam Hamza ya fita INdo ta shiga tare da d'ora mai ayman akan k'afarsa kasan cewar ta kar6o masa shi dan tasan yana son ganinsa.
"Cutie ni kikawa dariyar mugunta ko? Hmmm zan rama ai zaki zo inda nake."
"Toh ai kaine da abin dariya wallahi."
"Za dai mu had'e you will see."
Kallon ayman yayi tare da cewa.
"Cutie wannan da wa yake kama sam na kasa ganewa?!"
"Ban sani ba nima kasan ance ba'a gane kamanin jarirai harsai sun fara girma."
"Ki dinga karanta mai ayatul kursiyu kina tofa mai a mad'igarsa ai kin iya ta ko?"
Tana kallonsa yatsan hannunta k'arami a cikin bakinta tace.
"Eh na iya mana."
"Matso nan toh kiyi min inji ko dai-dai ne."
Cikin jin wani iri dan kar ta kakare ta matsa jikinsa ya rik'ota, a hankali ta fara karanto mai inda yaji zata 6ata wani gurin sai ya gyara mata harta gama sannan yace.
"Yauwa ki dinga yi mai Allah ya kare mana shi daga sharrin shaid'anu."
"Amin abu Ayman."
"Zan wuce sai kinzo cutie ki yo shiri sosai dan wannan karan hmmmm."
Dariya ta kuma yi sannan ya zaro kud'i 10k ya bata ko zata yi wani abun idan zata dawo sannan ya mik'e itama ta tashi suka rungumi juna kamar basa son rabuwa cikin yanayi na ba haka aka so ba Sadeeq ya bata Ayman sannan ya fita suka yi sallama da Inna su Uwani sai subirbid'a mai addu'ar sauka lafiya suke yi dan har lokacin suna gidan.
A zaure Sadeeq yaga malam Hamza kan wata guntuwar tabarma yana gyaran redio suka yi sallama bayan ya ajiye mai 5k yana ta godiya.
Yana shiga mota INdo tazo nan ma suka yi sallama ji yake tamkar ya tafi da ita amma ba yadda zai yi dole ta fita yaja motar ya tafi cike da kewarta ji yake ma tamkar basu had'u ba kamar yanzu ne ma yake kan hanyar zuwa ya gansu....
*HAJJA CE*
[7/31, 5:13 PM] Aisha Galadima: *
MUSAYAR ZUCIYA...
*K.A.S Precious Hajja ce*
*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*
(Home of expert & perfect writer's)
*DEDICTEED TO:* Sanah Isma'il Matazu.
*VOTE me on wattpad @Hajjac*
*Shafin yau naki ne m sweet heart SOFIYYA GALADANCI, I love you Allah ya nuna mana ranar Auranki da rai da lafiya nasan ke ko...?
kawai dai Allah ya k'ara miki baseera dear Bari nayi tsit*
Page *38*
Alama yayi mata da hannu ta saki labulen da aka nannad'e aka d'ora akan k'ofar d'akin. Murmushi tayi tare da zaro idanuwa tana girgiza kai alamar a'a, ganin haka yasa shi matsawa yana kallon k'ofar ganin babu me kallonsa yayi saurin sauke labulen INdo tace.
"Kai.. Kai... Kai! ba ruwa na nidai Inna ce fa ta d'aga shi wai sabida akwai zafi."
Hannu yasa ya janyo ta kusa dashi yana kallon fuskarta, ya kaleta ya kalli Ayman a hankali ya kai bakinsa saman goshinta ya sumbace ta INdo tasa hannu ta bayansa ta rungume shi itama sannan ta kallesa tace.
"Ka zauna ka tsaya."
Hannunsa cikin nata suka zauna yana kuma rik'e da Ayman.
Kwantar da Ayman yayi a gefe kasan cewar yana cikin towel sannan ya juya yana kallon INdo wanda ke kallon k'irjinsa dan wani iri taji da yadda yake mata wani irin kallo.
"Sannu da zuwa, ya gurin su Mama?"
"Kin yi kyau cutie na, kinyi kamar ba me jego ba dan babu wani alamun da zai nuna hakan meye sirrin?"
"Inna ce."
Ta bashi amsa tana wasa da yatsun hannunsa yayi murmushi tare da matso da ita kusa dashi yana mak'alota jikinsa.
"Ko kawai ma idan zan wuce mu tafi tare tunda kun gama wanka ai kin fara sallah ma ko cutie?"
INdo ta zaro idanuwa tana kallansa yayi murmushi yana d'aga mata girarsa kafin yaji tace.
"Ta6... In bikafa kace? So kakeyi insha zagi kenan a cikin garin nan, kasan mu bazan koma gidan ka ba dole sai an yi garar barka sannan za'a maida ni."
Kallonta yayi cikin rashin fahimtar maganarta ta sannan ta d'an zame ta janyo kayan abincin ta tsiyaya mai lemo ya kar6a har yana cewa.
"Cutie ban gane abinda kike nufi bane wace irin garar suna? Kuma wazai kai? Wa za'a bawa.?!"
"Kayan abinci ne ake kawowa gidan su me jego,su anan sun maida hakan kamar ibada dan haka idan miji be yi ba sai abin ya zama gori har jikokin mutum."
"Ikon Allah, Allah guda d'aya amma garuruwa daban-daban ni ban ta6a ji ba koda wasa wallahi. Toh idan kuma mijin bashida halin yi fa sai ayi ya ya cutie?"
INdo tana gyara k'afar Ayman ba tare da ta kallesa ba tace.
"Idan miji beyi miki ba shikenan sai a rabu dashi baza a mayar da ita ba. Idan aka ga ya takura da zaryar zuwa gidan su kuma sai ad'auke ta a kaita inda bazai sake ganinta ba har sai ya kawo kayan."
Sosai mamaki ya cika masa zuciya, lallai akwai d'inbin gyara a cikin kauyan nan amma banda haka ya za'ayi a hana miji matarsa akan abinda ba alkurani bane ya wajabta shi ba. Lallai yadda ya k'agu ta koma su tafi kwara state tare dole yaje a harhad'o a kawo,yarinyar tayi tsada da yawa daga wannan sai ace maka wannan.
"In zuba maka yanzu ko sai kayi sallan azahar naga an kusa kirawo wa."
"Bari sai nayi sallah cutie, dawo nan in dinga jin duminki a jikina."
Matsawa tayi ya rungumeta, yana yawo a jikinta da hannunsa ita kuma ta lumshe ido tana sauraransa. Sallamar su Uwani suka jiyo Sadeeq yayi saurin zame hannunsa daga jikinta yana yatsina fuska yace..
"Su waye?"
"Inajin su Maryam ne naji muryar su da Uwani da Sahura."
"Kai nashiga uku ni Sadeeq, wai hardasu nake aure ne da kullum na shigo garin nan sai sunzo sun samin ido? Ko 'yan uwanku ne cutie?"
"A'ah k'awaye nane amma kuma su haka suke duk inda sukaji labarin wani abun tofa sai ka gansu sabida dama ba wani tambayar miji fita suke yi ba."
"Ai munafukai ne wallahi."
Ya fad'a a kufule kafin ya matsa sun shigo cikin d'akin bakunansu a washe.
Zama suka yi daga bakin k'ofar amma hakan be hana warin ranar jikinsu da kaurin icen girki shiga cikin hancin Sadeeq ba ya tuna da tuni itama INdon haka take amma Allah ya d'aukaka ta.
Da kyar ya amsa musu a ciki-ciki sabida yadda suke kallansu suna rik'e ha6a sabida sunga sun manne jikin juna.
"Cutie zanyi alwala."
"Okey toh bari akawo ruwa k'ofar gida, ko zaka yi anan ciki."
"A'ah Inna na nan da dai bata nan sai nayi."
Tashi yayi suka d'an ra6e ya wuce sannan INdo ta fito suma suka bita a baya, tunda tazo gida suke bibiyarta ganinta suke tamkar Matar wani shugaban me rik'e da wani muk'amin.
Ruwa ta zuba tasa mayafi takai mai wajan mota sannan ta koma ciki.
Hira suka farayi dasu har aka idar da sallah Sadeeq ya dawo daga massalaci dan har tsayawa yayi suka d'anyi hira da principal d'in tsefawa makarantar su INdo daya bari.
Nafeesah ce ta kuma fita ta shigo dashi sannan INdo ta bishi su kuma su Uwani suka ci gaba da hira da Inna duk da bata cika sanya musu baki ba.
"Cutie Ina baby na kika kaishi?"
"Inna ta goyashi ko na kar6osa?!"
"Ah no kyalesa kar ace nayi rashin kunya."
Waina ta zuba masa da miya sannan ta matsa kusa dashi, had'e hannuwa yayi a k'ijinsa tare da bud'e baki alamar ta bashi da kanta.
Murmushi tayi tana girgiza kai ta fara bashi kunnuwansa har motsawa suke yi sabida yadda miyar tayi mai dad'i idan ta bashi sau d'aya itama sai ya tura mata wanda ta kuma d
ebowa yasa mata a baki haka suka dinga yi har suka kusa cinyewa yace ya k'oshi.
"Cutie gaskiya ranar Sunday zaki koma zanyi duk iya yadda zanyi na tabbatar da an kawo kayan nan, sannan direct za'a wuce dake can gidan marigayi acan zaki ci gaba da zama an raba gado Abba yace idan kin koma zaizo yayi miki bayani kinji.?!"
Kifta idanuwa ta shiga yi alamar hawaye take son karsu fito ya janyo ta tare da kamo fuskarta yana san saka kwayar idanunsa cikin nata.
"Karki zubar min da hawaye kinga nima ina tattala nawa, keda ma ba'ayi miki da yawa ba tunda an baki me kamadashi iri d'aya sak sannan kina cikin zuciya ta kamar rai. Ni kuwa tare muka taso mu kwana tare muyi fad'a mu shirya ba tare da kowa ya sani ba, shine ni nine shi amma yau babu shi."
"Ka d'auka kaima a ranka nice shi tunda dama silarsa ce ta sa muka zama abu d'aya dakai, na zame maka shi kaima karka sake yin kuka mun riga munyi *MUSAYAR ZUCIYA* ni da kai fatana a yanzu shine na zama tauraruwa kamar yadda yake so yaga na zama kayi min addu'a malama Hannatu tace addu'ar miji akan matarsa tana saurin kar6owa."
Bakinsa da yake ta motsi tun d'azu shi ya zura cikin nata cikin wani mugun tausayinta da wata azababbar kaunarta da soyayyarta da ta taso mai. Kissing d'in ta yake cikin wani irin salo wanda yasa INdo ta kasa gane kansa, ya shagala kawai suka ji muryar malam Hamza a tsakar gida amma Sadeeq ji yayi tamkar a tsakiyar d'akin yayi sabida tsabar tsoro.
"Na tafi cutie kar nayi abun kunya a gidannan a d'akin baba dan naga kema ba hanani zaki ba."
Dariya INdo take yi sosai wanda tasa Sadeeq kallonta yana hararata dan har rik'e ciki takeyi ya matsa can bakin k'ofa-k'ofa tare da maida hularsa yana jiran shigowar malam Hamza d'akin dan yaji Inna tana cewa suna ciki.
"Matsoraci kawai Abu Ayman, uhm...uhm..uhm.."
INdo ta fad'a cikin dariya ya juya yana mata gwalo shima. muryar malam Hamzan yaji a bakin k'ofar Sadeeq yayi saurin d'aga labulen ita kuma INdo ta fara matsar da kayan da suka ci abinci kamar masu gaskiya.
"Baba sannu da shigowa, gashi duk mun tsare maka d'akin."
Sadeeq ya fad'a yana gyara zama tare da turo hula gaba yana kuma mai da ita baya alamar kunya ya keji.
Malam Hamza yayi dariya tare da k'arasawa cikin d'akin ya zauna a bakin gadon sa yana cewa ba komai Gaidashi Sadeeq yayi cike da girmamawa har suka d'an fara hira ita kuma INdo ta kwashe kayan ta fita dasu can su Uwani aka ci ragowar ana jinjinawa INdo ganin duk da kud'inta tayi wannan shagalin.
Malam Hamza da Sadeeq sun jima suna hira kafin malam Hamza ya fita INdo ta shiga tare da d'ora mai ayman akan k'afarsa kasan cewar ta kar6o masa shi dan tasan yana son ganinsa.
"Cutie ni kikawa dariyar mugunta ko? Hmmm zan rama ai zaki zo inda nake."
"Toh ai kaine da abin dariya wallahi."
"Za dai mu had'e you will see."
Kallon ayman yayi tare da cewa.
"Cutie wannan da wa yake kama sam na kasa ganewa?!"
"Ban sani ba nima kasan ance ba'a gane kamanin jarirai harsai sun fara girma."
"Ki dinga karanta mai ayatul kursiyu kina tofa mai a mad'igarsa ai kin iya ta ko?"
Tana kallonsa yatsan hannunta k'arami a cikin bakinta tace.
"Eh na iya mana."
"Matso nan toh kiyi min inji ko dai-dai ne."
Cikin jin wani iri dan kar ta kakare ta matsa jikinsa ya rik'ota, a hankali ta fara karanto mai inda yaji zata 6ata wani gurin sai ya gyara mata harta gama sannan yace.
"Yauwa ki dinga yi mai Allah ya kare mana shi daga sharrin shaid'anu."
"Amin abu Ayman."
"Zan wuce sai kinzo cutie ki yo shiri sosai dan wannan karan hmmmm."
Dariya ta kuma yi sannan ya zaro kud'i 10k ya bata ko zata yi wani abun idan zata dawo sannan ya mik'e itama ta tashi suka rungumi juna kamar basa son rabuwa cikin yanayi na ba haka aka so ba Sadeeq ya bata Ayman sannan ya fita suka yi sallama da Inna su Uwani sai subirbid'a mai addu'ar sauka lafiya suke yi dan har lokacin suna gidan.
A zaure Sadeeq yaga malam Hamza kan wata guntuwar tabarma yana gyaran redio suka yi sallama bayan ya ajiye mai 5k yana ta godiya.
Yana shiga mota INdo tazo nan ma suka yi sallama ji yake tamkar ya tafi da ita amma ba yadda zai yi dole ta fita yaja motar ya tafi cike da kewarta ji yake ma tamkar basu had'u ba kamar yanzu ne ma yake kan hanyar zuwa ya gansu....
*HAJJA CE*
[7/31, 5:13 PM] Aisha Galadima: *
MUSAYAR ZUCIYA...