Sashe 23
Musayar Zuciya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
A true life story
*K.A.S Precious Hajja ce*
*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*
(Home of expert & perfect writer's)
*VOTE me on wattpad @Hajjac*
*DEDICTEED TO:* Sanah Isma'il Matazu
*Gaskiya ban san me zan cewa masoya maso bibiyar labarin nan ba sai dai nace muku love you all.*
_Shafin naku ne My Shuwa Arab, Dota Fatima, Dota Marok'i, My Shama, My Olo, aunty Jidder_
Page *18*
*Bayan wasu shekaru.*
Gaba d'aya an kammala yin komai ansa rana da Fateemah ta kammala school za'ayi dan haka ginin su kawai suke yi. Gidane me kyawun gaske kowanne yake ginawa kowa kuma da yadda yake son abunsa. Gidan Abubakar yafi tsaruwa nesa ba kusa ba yafi na Sadeeq sosai kasan cewar shi yana son ya samu wani acan inda yake business dinsa idan sunje da matarsa babu wani fargaba dama yanada gidanshi dan haka biyu ya raba sa6anin Abubakar dashi a abujan ma yana da k'atan gida a quarters d'in asibitin da yake aiki.
*****
Fateema na shekarar k'arshe domin sauran 'yan watanni ta kammala, yayin da a 6angaran INdo itama sai hamdala domin zata iya rubuta wasu kalmomin harma ta rubuta wasik'a da Hausa koda ajimi kuma iya yawancin surorin alkur'ani me girma an samu cigaba sosai.
Kyawunta ya fito ta waye ta goge kai in baka cika ishasshe bama bata kulaka bare harkuyi hudd'a tare. Zaune malam Hamza da Inna suka suna tattaunawa akan yadda zasu yi da kayan d'akin INdo gashi INdo tace harda gararta zata tafi batason abin gori.
"Toh malam ya zamu yi, iya abinda Allah ya bamu shi zamu yi mata ai suma sunsan damu dasu ba d'aya bane sun fimu ta ko'ina."
"Hakane Maryamu yanzu dai dole naje na siyar da gonata dake can saye guda d'aya, sannan na siyar da shanuna guda biyu sai ayi mata amfani da kud'in nasan dai bazamu yi mata irin yadda take so ba saidai ai munyi k'ok'ari kuma mani wallahi dandai Dacta Habu zata aura hiyasa zanyi mata duk abinda nasan Zan iya sabida yaron nan d'an k'irki ne, duk sanda na kalli katangar nan naganta da suminti sai naji dad'i."
"Hakane kam malam toh sai a siyar d'in Allah ya bada lada."
Malam Hamza yace "Amin."
Kwana hudu dayin zance ya d'auki abokinsa malam kallah suka tafi Saye bayan rabansa da zuwa kusan shekaru goma sha biyar kenan. Sun gaisa da kowa saidai tsakaninsa da yakumbo tsahare babu ko kallon banza, bayan an gayawa sarkin shanu aka yi cinikin shanun malam Hamza wanda shine ya baiwa yakumbo talatu su yace idan sun haihu ya barmata saidai duk lokacin da yake da bukata toh zai dawo ya karbi guda biyu. Dubu talatin-talatin aka siye su nan aka bawa malam Hamza kud'insa dubu sittin, aka koma kan gona wani mutum ya siya dubu cas'sa'in malam Hamza ya kar6o kudin suka dawo gida da dubu d'ari da Hamsin cas.
Had'awa akayi da kud'in nagani inaso d'inta aka had'a suka zama d'ari biyu cif malam Hamza yace aje ayi cinikin gado madubi da wardrobe, nan aka nuna musu kud'ad'an ko wanne babu ma na k'asa da dubu d'ari a cikin irin wanda INdo ta nuna tana so.
Na dubu d'ari da hamsin suka za6ar mata wata yayar Inna ce da take aure a dawakin tofa sukaje suka tayo. Sai kud'in gudun mawar da aka dinga kawo musu dan su kauye basai ranar biki suke bada gudunmawa ba. Haka dame d'ari d'aribiyu dubu biyu gashinan dai aka dinga vawa inna da malam Hamza suka had'e ya basu dubu hamsin da biyar da naira ashirin. Suka had'e da ragowar hamsin dinnan aka had'a d'ari na kujeru gaskiya INdo taci Kud'i wai...!
Sai kuma masu kawo kayan amfani na kitchen me kofi , me tasa, me plate, gashi nan dai suma aka had'a Inna tasa aka siyar da gonarta itama sai aka sissiya abubuwan da babu a kitchen d'in.
****
Gidan su Fateema kuwa ko shirin basu farayi ba sabida su ba wani case karatunta kawai takeyi hankali kwance.
'Bangaren mazan kuwa, kayan lefe ake had'awa komai iri d'aya Mama tace azuba colors ne kawai suke ban-bantawa da kuma size domin INdo tafi Fateemah jiki ita kuma Fateemah tafi INdo haske da tsawo.
Akwatuna bakwai-bakwai akayi musu kowacce shak'are da kaya domin mazajen ba k'aramin k'ok'ari suka yi ba sun kashe Kud'i over.
Ranar da su Fateema sukayi graduation a ranar aka kai kaya murna biyu ta had'ar mata.
'Bangaran INdo ma ankai kayan tana gidan Rukayya kwance tana waya da Abubakar, cikin salon mak'e muryar data koyo wajan su Zainab da Hadiza tace mai.
"My key wai me kakeyi ne yanzu?!"
"Ina office a zaune tare da frame d'inki inata kallonki."
"Yeeee naji dad'i nima ka tambaye ni.."
"Habibty mekike yi yanzu..?"
Ya fad'a kamar yana cikin maye, dariya INdo tayi me sauti sannan tace.
"Ni tunaninka nakeyi dan Allah yauhe zaka dawo.?!"
Dariya yayi tare da cewa, "Sai ending d'in month d'innan, ya mekika tanadar min?!"
Tace "kana nufin ending k'arhen Month watan nan ko?!
"Eh haka nake nufi madam."
"Toh kenan kana nufin ankusa biki."
Yace "Eh amma ai Sadeeq yana nan ba kuma zai koma ba sai an gama biki kokina buk'atar wani abun nasa ya aiko miki dashi?!"
INdo ta kuma gyara kwanciya domin yarinyar ta iya kar6ar sakwan love tace.
"Eh akwai abinda nakeso."
"Toh madam menene shi..?!"
Tace cikin jan numfashi "Kai nake son gani."
Abubakar saida tsigar jikinsa ya tashi yarrrr ya d'ora k'afarsa kan table tare da jin gina da jikin kujerar dayake kai, hannu yasa a k'irjinsa yana d'an bubbugawa tsawon wani lokaci sannan yace mata.
"Sorry Habibty da ace da yadda zanyi danayi na taho, saidai na riga na k'ar6i aikin wani abokina inason idan na taho ya kar6i nawa sabida idan munyi aure bazan dawo da wuri ba sai na gama shan amarci na."
INdo ta guntse baki jin abinda ya fad'a sannan taji yace.
"Ko kina son da an d'aura aure na dawo."
Da sauri tace "A'a bana son ka koma."
"Toh ki tanadar min kanki a duk ranar da aka kawoki gidana."
Kit..yaji ta yanke wayar ya sauke yana kallon screen d'in yana murmushi bata san wannan zantuttukan baya manta ranar daya fara gaya mata irin maganganun tace mai ita ba 'yar iska bace. Ranar yaci dariya kamar cikin sa zaiyi ciwo, bebi kiran ba yaci gaba da aikinsa yana ta murmushi INdo na bashi laugh yasan idan sukayi aure zai dinga shan dariya.
INdo kuwa bata koma gida ba sai da tayi magariba sannan ta koma gida, wayyo Allah dataga irin akwatinan zamanin da Abubakar ya kawo mata bata san lokacin data fad'a jikin Inna ta rushe da kuka ba. Inna sai faman lallashi takeyi Sagiru da shehu suna kallon kayan kowa sai nuna abinda yake sukeyi da kyar tayi shiru aka cigaba da kallon kaya Inna ta nuna mata dubu hamsin tace,
"Gashi 'yarnan sunce kud'in d'inki ne."
K'ar6a INdo tayi tana godiya, tana gama kallon kayan suka rufe ta fita waje. Unguwar su kezy taje ta samesu zaune sai zuk'ar sugari sukeyi ta toshe hanci tana musu magana.
"Kai kezy aji tsoran Allah dai za'a mutu."
Tayi maganar tana sake toshe hanci, jazuli yace.
"Kefa 'yar rainin hankalice dan kinzama babbar yarinya shine zaki dinga yi mana kallon equal.."
"Kai masifaffe ni gurinku nazo, kunsan ankawo kayan aurena, toh sonake kuzo gida kuyi gadi Allah ma yace tashi intemake ka, idan ma kune 6arayin nidai kuzo gobe he'in baku dubu goma."
"Kai hajiya INdo kin zama hajjaju fa Allah."
Kezy ya fad'a tace "Eh koma dai meye nidai kuyi min."
"Karki damu zamuci uwar hegen dazaiyi gigin zuwa."
"Toh nagode."
Tafad'a ta wuce ta shiga gidan su Sahura, ta dad'e kafin ta koma gida. Haka akayi suka yi gadin gidan Allah kuma ya temakesu babu wanda yaje. Washe gari ta basu 10k suka tafi, ta ciro atamfa d'aya ta bawa Nafeesa tayi ta murna sannan ta ciro tirmi biyar ta bawa Inna tace tasa da biki. Inna tace a'a itama INdo ta dage tace tabar mata. Cikin shaddojinta kuma ta za6o wata ash tace abawa babanta, gaskiya INdo batada kyashi wajan bawa iyaye abunta amma fur taki bawa Sagiru yayi mitar yayi magiyar tace bazata bayar ba yana da kud'i. Aikuwa yaji haushi duk abinda tasashi bayayi mata shima.
Kowanne 6angare shiri akeyi ta kowanne side, 6angaran Fateema anje an fara jere haka itama INdo an fara, saidai tsarin gidan yasa bazasu iya cewa sai sun saka mata komai ba domin basu da halin yin hakan. Iya d'akinta kawai suka sawa kaya sai parlon farko dining area kuwa kokalansa basuyi ba gashi gida yayi masifar yin kyau domin yafi na Sadeeq had'uwa.
Ana sauran sati d'aya biki Abubakar ya dawo kano, gidan su harya fara cika da bak'in nesa sai tsiya suke mai da masu nuna cewar ya auro 'yar talakawa ga gida har gida amma babu kaya. Sharesu yayi yana yin wanka Sadeeq yazo suka fita. Gidan Sadeeq suka fara zuwa sai sambarka domin kayane nagani na fad'a aka zubawa Fateema, royal ne furniture d'in sannan babu inda va'a k'awata ba sannan suka wuce gidan Abubakar babu abinda yaji aransa na 6acin rai suna shiga cikin bedroom d'in INdo ya fad'a kan gado katifar ta lotsa da alama sakance kuma ba vita form bace ya ware hannuwa yana cewa Sadeeq.
"M twinnie remain 6days na kwana anan nida Humairah tah."
Sadeeq yayi murmushi tare da girgiza kai gaba d'aya INdo ta rikita mai d'an uwa, shi har yau ya kasa manta INdon da ta baya can domin duk sanda zai tuno ta a k'azamarta yake haskilota har tausayin Abubakar yake idan yaka yana wani abun dominta.
Cikin kwanaki uku Abubakar yasa aka sake zuba mai wasu k'awatattun furniture's a inda ba'a zuba ba aka sanya labulaye da site na dining area ba tare daya sanar da kowa ba sai Sadeeq domin cikin dare akaje akasa komai harda plasma TV. Koda dangin INdo suka dawo gidan ba k'aramin mamaki suka yiba.
Ana gobe kamu/yini da d'aurin aure....
*HAJJA CE*
[7/31, 5:13 PM] Aisha Galadima: *
MUSAYAR ZUCIYA...
*K.A.S Precious Hajja ce*
*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*
(Home of expert & perfect writer's)
*VOTE me on wattpad @Hajjac*
*DEDICTEED TO:* Sanah Isma'il Matazu
*Gaskiya ban san me zan cewa masoya maso bibiyar labarin nan ba sai dai nace muku love you all.*
_Shafin naku ne My Shuwa Arab, Dota Fatima, Dota Marok'i, My Shama, My Olo, aunty Jidder_
Page *18*
*Bayan wasu shekaru.*
Gaba d'aya an kammala yin komai ansa rana da Fateemah ta kammala school za'ayi dan haka ginin su kawai suke yi. Gidane me kyawun gaske kowanne yake ginawa kowa kuma da yadda yake son abunsa. Gidan Abubakar yafi tsaruwa nesa ba kusa ba yafi na Sadeeq sosai kasan cewar shi yana son ya samu wani acan inda yake business dinsa idan sunje da matarsa babu wani fargaba dama yanada gidanshi dan haka biyu ya raba sa6anin Abubakar dashi a abujan ma yana da k'atan gida a quarters d'in asibitin da yake aiki.
*****
Fateema na shekarar k'arshe domin sauran 'yan watanni ta kammala, yayin da a 6angaran INdo itama sai hamdala domin zata iya rubuta wasu kalmomin harma ta rubuta wasik'a da Hausa koda ajimi kuma iya yawancin surorin alkur'ani me girma an samu cigaba sosai.
Kyawunta ya fito ta waye ta goge kai in baka cika ishasshe bama bata kulaka bare harkuyi hudd'a tare. Zaune malam Hamza da Inna suka suna tattaunawa akan yadda zasu yi da kayan d'akin INdo gashi INdo tace harda gararta zata tafi batason abin gori.
"Toh malam ya zamu yi, iya abinda Allah ya bamu shi zamu yi mata ai suma sunsan damu dasu ba d'aya bane sun fimu ta ko'ina."
"Hakane Maryamu yanzu dai dole naje na siyar da gonata dake can saye guda d'aya, sannan na siyar da shanuna guda biyu sai ayi mata amfani da kud'in nasan dai bazamu yi mata irin yadda take so ba saidai ai munyi k'ok'ari kuma mani wallahi dandai Dacta Habu zata aura hiyasa zanyi mata duk abinda nasan Zan iya sabida yaron nan d'an k'irki ne, duk sanda na kalli katangar nan naganta da suminti sai naji dad'i."
"Hakane kam malam toh sai a siyar d'in Allah ya bada lada."
Malam Hamza yace "Amin."
Kwana hudu dayin zance ya d'auki abokinsa malam kallah suka tafi Saye bayan rabansa da zuwa kusan shekaru goma sha biyar kenan. Sun gaisa da kowa saidai tsakaninsa da yakumbo tsahare babu ko kallon banza, bayan an gayawa sarkin shanu aka yi cinikin shanun malam Hamza wanda shine ya baiwa yakumbo talatu su yace idan sun haihu ya barmata saidai duk lokacin da yake da bukata toh zai dawo ya karbi guda biyu. Dubu talatin-talatin aka siye su nan aka bawa malam Hamza kud'insa dubu sittin, aka koma kan gona wani mutum ya siya dubu cas'sa'in malam Hamza ya kar6o kudin suka dawo gida da dubu d'ari da Hamsin cas.
Had'awa akayi da kud'in nagani inaso d'inta aka had'a suka zama d'ari biyu cif malam Hamza yace aje ayi cinikin gado madubi da wardrobe, nan aka nuna musu kud'ad'an ko wanne babu ma na k'asa da dubu d'ari a cikin irin wanda INdo ta nuna tana so.
Na dubu d'ari da hamsin suka za6ar mata wata yayar Inna ce da take aure a dawakin tofa sukaje suka tayo. Sai kud'in gudun mawar da aka dinga kawo musu dan su kauye basai ranar biki suke bada gudunmawa ba. Haka dame d'ari d'aribiyu dubu biyu gashinan dai aka dinga vawa inna da malam Hamza suka had'e ya basu dubu hamsin da biyar da naira ashirin. Suka had'e da ragowar hamsin dinnan aka had'a d'ari na kujeru gaskiya INdo taci Kud'i wai...!
Sai kuma masu kawo kayan amfani na kitchen me kofi , me tasa, me plate, gashi nan dai suma aka had'a Inna tasa aka siyar da gonarta itama sai aka sissiya abubuwan da babu a kitchen d'in.
****
Gidan su Fateema kuwa ko shirin basu farayi ba sabida su ba wani case karatunta kawai takeyi hankali kwance.
'Bangaren mazan kuwa, kayan lefe ake had'awa komai iri d'aya Mama tace azuba colors ne kawai suke ban-bantawa da kuma size domin INdo tafi Fateemah jiki ita kuma Fateemah tafi INdo haske da tsawo.
Akwatuna bakwai-bakwai akayi musu kowacce shak'are da kaya domin mazajen ba k'aramin k'ok'ari suka yi ba sun kashe Kud'i over.
Ranar da su Fateema sukayi graduation a ranar aka kai kaya murna biyu ta had'ar mata.
'Bangaran INdo ma ankai kayan tana gidan Rukayya kwance tana waya da Abubakar, cikin salon mak'e muryar data koyo wajan su Zainab da Hadiza tace mai.
"My key wai me kakeyi ne yanzu?!"
"Ina office a zaune tare da frame d'inki inata kallonki."
"Yeeee naji dad'i nima ka tambaye ni.."
"Habibty mekike yi yanzu..?"
Ya fad'a kamar yana cikin maye, dariya INdo tayi me sauti sannan tace.
"Ni tunaninka nakeyi dan Allah yauhe zaka dawo.?!"
Dariya yayi tare da cewa, "Sai ending d'in month d'innan, ya mekika tanadar min?!"
Tace "kana nufin ending k'arhen Month watan nan ko?!
"Eh haka nake nufi madam."
"Toh kenan kana nufin ankusa biki."
Yace "Eh amma ai Sadeeq yana nan ba kuma zai koma ba sai an gama biki kokina buk'atar wani abun nasa ya aiko miki dashi?!"
INdo ta kuma gyara kwanciya domin yarinyar ta iya kar6ar sakwan love tace.
"Eh akwai abinda nakeso."
"Toh madam menene shi..?!"
Tace cikin jan numfashi "Kai nake son gani."
Abubakar saida tsigar jikinsa ya tashi yarrrr ya d'ora k'afarsa kan table tare da jin gina da jikin kujerar dayake kai, hannu yasa a k'irjinsa yana d'an bubbugawa tsawon wani lokaci sannan yace mata.
"Sorry Habibty da ace da yadda zanyi danayi na taho, saidai na riga na k'ar6i aikin wani abokina inason idan na taho ya kar6i nawa sabida idan munyi aure bazan dawo da wuri ba sai na gama shan amarci na."
INdo ta guntse baki jin abinda ya fad'a sannan taji yace.
"Ko kina son da an d'aura aure na dawo."
Da sauri tace "A'a bana son ka koma."
"Toh ki tanadar min kanki a duk ranar da aka kawoki gidana."
Kit..yaji ta yanke wayar ya sauke yana kallon screen d'in yana murmushi bata san wannan zantuttukan baya manta ranar daya fara gaya mata irin maganganun tace mai ita ba 'yar iska bace. Ranar yaci dariya kamar cikin sa zaiyi ciwo, bebi kiran ba yaci gaba da aikinsa yana ta murmushi INdo na bashi laugh yasan idan sukayi aure zai dinga shan dariya.
INdo kuwa bata koma gida ba sai da tayi magariba sannan ta koma gida, wayyo Allah dataga irin akwatinan zamanin da Abubakar ya kawo mata bata san lokacin data fad'a jikin Inna ta rushe da kuka ba. Inna sai faman lallashi takeyi Sagiru da shehu suna kallon kayan kowa sai nuna abinda yake sukeyi da kyar tayi shiru aka cigaba da kallon kaya Inna ta nuna mata dubu hamsin tace,
"Gashi 'yarnan sunce kud'in d'inki ne."
K'ar6a INdo tayi tana godiya, tana gama kallon kayan suka rufe ta fita waje. Unguwar su kezy taje ta samesu zaune sai zuk'ar sugari sukeyi ta toshe hanci tana musu magana.
"Kai kezy aji tsoran Allah dai za'a mutu."
Tayi maganar tana sake toshe hanci, jazuli yace.
"Kefa 'yar rainin hankalice dan kinzama babbar yarinya shine zaki dinga yi mana kallon equal.."
"Kai masifaffe ni gurinku nazo, kunsan ankawo kayan aurena, toh sonake kuzo gida kuyi gadi Allah ma yace tashi intemake ka, idan ma kune 6arayin nidai kuzo gobe he'in baku dubu goma."
"Kai hajiya INdo kin zama hajjaju fa Allah."
Kezy ya fad'a tace "Eh koma dai meye nidai kuyi min."
"Karki damu zamuci uwar hegen dazaiyi gigin zuwa."
"Toh nagode."
Tafad'a ta wuce ta shiga gidan su Sahura, ta dad'e kafin ta koma gida. Haka akayi suka yi gadin gidan Allah kuma ya temakesu babu wanda yaje. Washe gari ta basu 10k suka tafi, ta ciro atamfa d'aya ta bawa Nafeesa tayi ta murna sannan ta ciro tirmi biyar ta bawa Inna tace tasa da biki. Inna tace a'a itama INdo ta dage tace tabar mata. Cikin shaddojinta kuma ta za6o wata ash tace abawa babanta, gaskiya INdo batada kyashi wajan bawa iyaye abunta amma fur taki bawa Sagiru yayi mitar yayi magiyar tace bazata bayar ba yana da kud'i. Aikuwa yaji haushi duk abinda tasashi bayayi mata shima.
Kowanne 6angare shiri akeyi ta kowanne side, 6angaran Fateema anje an fara jere haka itama INdo an fara, saidai tsarin gidan yasa bazasu iya cewa sai sun saka mata komai ba domin basu da halin yin hakan. Iya d'akinta kawai suka sawa kaya sai parlon farko dining area kuwa kokalansa basuyi ba gashi gida yayi masifar yin kyau domin yafi na Sadeeq had'uwa.
Ana sauran sati d'aya biki Abubakar ya dawo kano, gidan su harya fara cika da bak'in nesa sai tsiya suke mai da masu nuna cewar ya auro 'yar talakawa ga gida har gida amma babu kaya. Sharesu yayi yana yin wanka Sadeeq yazo suka fita. Gidan Sadeeq suka fara zuwa sai sambarka domin kayane nagani na fad'a aka zubawa Fateema, royal ne furniture d'in sannan babu inda va'a k'awata ba sannan suka wuce gidan Abubakar babu abinda yaji aransa na 6acin rai suna shiga cikin bedroom d'in INdo ya fad'a kan gado katifar ta lotsa da alama sakance kuma ba vita form bace ya ware hannuwa yana cewa Sadeeq.
"M twinnie remain 6days na kwana anan nida Humairah tah."
Sadeeq yayi murmushi tare da girgiza kai gaba d'aya INdo ta rikita mai d'an uwa, shi har yau ya kasa manta INdon da ta baya can domin duk sanda zai tuno ta a k'azamarta yake haskilota har tausayin Abubakar yake idan yaka yana wani abun dominta.
Cikin kwanaki uku Abubakar yasa aka sake zuba mai wasu k'awatattun furniture's a inda ba'a zuba ba aka sanya labulaye da site na dining area ba tare daya sanar da kowa ba sai Sadeeq domin cikin dare akaje akasa komai harda plasma TV. Koda dangin INdo suka dawo gidan ba k'aramin mamaki suka yiba.
Ana gobe kamu/yini da d'aurin aure....
*HAJJA CE*
[7/31, 5:13 PM] Aisha Galadima: *
MUSAYAR ZUCIYA...