Sashe 29
Musayar Zuciya Part 1 Complete Hausa Novel · about 10 min read
A true life story
*K.A.S Precious Hajja ce*
*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*
(Home of expert & perfect writer's)
*VOTE me on wattpad @Hajjac*
*DEDICTEED TO:* Sanah Isma'il Matazu
Page *24*
Koda sukaje kauyan Sani bak'aramin mamaki Fateema tayi ba da ganin gidan su INdo da kuma kauyan da suke, lallai Allah ya d'aukakata daya aura mata Abubakar har kuma tashiga wannan uban gidan wanda yafi nata komai da komai. Basu jima ba Sadeeq yace zasu koma ya bada dubu ashirin Inna da malam Hamza suka dinga yi mai godiya amma INdo fateema kawai tayiwa sallama ta koma gida 'yan garin suka cigaba da zuwar musu gaisuwa.
Rayuwa gaba d'aya ta sauyawa INdo komai yayi zafi tunda ta dawo kauyan Sani komai nata ya canza, tana takaba a gidan su kamar yadda malam Hamza ya buk'ata sai dai itace inzata bayan gida sai abata sanda da wuk'a wai ta tafi da ita ko idan zatayi bacci toh ruwanta a buta da wuka wai mijinta yana biye da ita duk da cewar ba'a gidansa takeba. Sannan ta dinga tafiya a hankali karya tad'iyeta. wayace haka ake zaman takaba?wannan ba musulinci ya koyar dashi ba kawai mutanene suka maidashi al'ada har hakan ya fara zama kamar ibada. Satin INdo biyu a gida lokacin sati uku kenan da rasuwar Abubakar su Mama sukaje garin domin ita sam hankalinta ya kasa kwanciya, a zaure suka tarar dasu INdo suna tsinkar zogale harta fara komawa kalarta ta dah gashi dai jikinta da kaya masu kyau amma babu tsafta tunda ta dawo sau biyu tayi wanka wai ai duk cikin takaba ne. su Hawwah suka dinga kallonta cikin tsananin mamaki ita kuwa ta kasa 6oye farin cikinta da ganinsu.
Bayan sun gaggaisa ne Mama ta kasa yin shiru ta kalli INdo dake tsakiyarsu Haleema tace.
"Aisha ya naganki haka?duk kinyi wani iri anya kina wanka da kula da lafiyar jikin ki?!"
Cikin rashin damuwa tare INdo tace.
"Ai Mama nida nake takaba ai ance ba'a wanka sai dai a sati sau d'aya shi yasa ma banayi..."
"Subahanallahi inji waye ya gaya miki haka?"
INdo tace "Su Inna ne."
Inna nacan tana k'ok'arin had'a dambu ta samu tabasu suci Mama tace.
"Zonan Aisha na shiga uku ba haka ake yi ba a musulunci, ba haka qur'ani ya gaya mana ba."
Tashi INdo tayi zuwa kusa da Mama ta zauna Mama na kallonta cikin tsananin tausayawa ta janyo ta jikinta tace.
"Mecece Takaba Aisha?!"
INdo tayi shiru sai faman wulk'ita idanuwa takeyi Mama tace.
"Aisha Takaba dai itace Zaman da mace zatayi bayan rasuwar megidanta na wad'ansu kwanaki sanannu a cikin gidanta batare da tayi ado da kwalliya ba, ba kuma data kuma yin wani auren ba, ko sanya dukkan abinda zai ja hankalin wani a jikinta ba na tufafi ko kayan k'arau. Aanan Takaba ta sha babban da Iddar saki, shi yasa naso a barki a can domin d'an zaman da kikayi a gidan mu na gano cewar kinada gyara a cikin rayuwarki. Banda iyayanki sun kafe kancewar gara kitafi babu me zuwa ya zauna dake a cikin gidanki sannan kowa yasan mijinki ya rasu gashi idan kikaga Sadeeq wani tashin hankalin ne da bazan bari ba wallahi yanzu gashi kinzo nan sun k'ara dilmiyar dake cikin wani duhun kan.
Wallahi mahaifinki gaddama garesa Aisha ba yadda ba'ayi dashi ya barki ba yace dasun dawo bakwai za'a tafi dake sabida baya son abinda kikewa Sadeeq. Shin kinsan Gwargwadon kwanakin Takaba a musulunci Aisha?"
INdo ta girgiza kai alamar a'a Mama ta d'ago ta daga jikinta tace.
"Alokacin da mutun ya rasu, to zai bar iyalin shi ne a d'ayan hali guda biyu, kodai ta zama tanada Juna biyu ko kuma bata da shi. Idan bata da juna biyu to Takabarta itace tayi Wata hud'u da kwanaki goma Kamar yadda Allah yace cikin Suratul-Bak'ara _Kumma dukkanin mazan dake rasuwa daga cikin ku subar matayan su, to matan zasu zauna wata hud'u da kwana goma aya ta d'ari biyu da talatin da hud'u 234..._
To amma idan ya rasu ya barta da juna biyu a wannan lokacin k'arshen Takabarta shine ta sauk'e abinda take dauk'e da shi koda kuwa ranar da ya rasu ne ma'ana ta haihu ko tayi 6arin cikin. Misali ya rasu 10:00am na safe ita kuma ta haihu 10:05 na safiyar, shi k'enan ta kammala takabarta, idan wani ya gani yace yana so aka d'aura aure 2:30 na ranar aure ya d'auru _(ana k'ar6ar gaisuwa ana d'aurin aure)_ Dalili kuwa shi ne. fad'in Allah (s.w. a) a cikin Suratut-Talak aya ta 4 _Kuma dukkanin mata masu juna biyu to lokacinsu shine su sauk'e abinda suke d'auk'e dashi_ da kuma Hadisin Subai'a Al-aslamiyyah, Ita ta kasance tana auran Sa'ad Dan Khaulah, shi kuma ya fito ne daga gidan Amir d'an Lu'ayy, yana daga cikin wad'an da suka halarci yak'in Badar, sai ya rasu yabarta a halin bankwana tana da juna biyu, bata ko jima ba bayan rasuwar shi saita haihu, a lokacin data kamma biki sai tai kwalliya, sai Abu-Sanabil Dan Ba'akk yazo wurinta, shi kuma ya fitone daga gidan Abduddar, sai yace da ita Lafiya naga kin cancara ado haka, ko kina son ki aure ne? Na rantse da Allah lokacin auranki bai yi ba, harsai kin yi wata hud'u da kwana goma. Sai Subai'a tace Yayinda ya fad'a min haka maraice na yi sai na tattara kayana naje wurin Ma'aikin Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi, na tambaye shi hakan, sai ya ban amsa da cewa ai na kamala Takabata tun lokacin dana haihu, ya ban dama da inyi aure a duk lokacin da naga dama. Yanzu ke Aisha kina da ciki?!"
INdo ta kalli Yayya Hawwah kafin ta maida idonta kan Mama tace "Wallahi ban sani ba nima." Mama ta sake kallonta sannan tace.
"Kinyi al'ada sanda kika dawo?!"
INdo ta sunkuyar da kai sannan tace,
"Ai yanzu ma haka inayi yau kwanana biyu kenan."
"Hazbunallahu wani'imal wak'il, yanzu duk da kina wannan jinin Aisha bakya wanka?!"
INdo tayi shiru jin yadda Mama tayi magana da alama abin mamaki ya bata da haushi ita kuma ya zatayi tunda ance mata haka akeyi. Inna ce ta shigo tana tayi musu sanna tare da kawo musu ruwa a kwanan shin ruwan malam Hamza, tsabtar kyawun kwanon da yadda ruwan ciki yake garai-garai abin sha'awa shine ya sanya su Haleema shan ruwan gidan.
Zama Inna tayi suka sake gaisawa Mama tayi gyaran murya bayan tace su Haleema su fita, suna fita tayi murmshi tare da cewa.
"Dama munzo ne mu gaida ku sannan zamu tafi da Aisha za'ayi mata wani gwajin ciki sabida shi marigayi yace yasa mata wani abu wanda koda tana da ciki toh bazata dena jinin al'adaba toh yanzu shine zamuje a duba agani kar abar mata abu ba'a saniba ko yana amfani nan da kwana biyu za'a dawo da ita kinsan likitocin nan da k'ak'ale."
Mama ta kifa Inna domin yanzu so take ta tafi da INdo can. cikin rashin damuwa Inna tace "Allah sarki ai babu komai an zama d'aya bari na aika a k'ira malam dama shine ai ke hanawa da yaji yadda takeyi idan taga shi d'an uwan marigayin."
Fitowa tayi ta lek'a waje ta samu yaro yaje ya k'ira Malam Hamza a gurin sana'ar Sa. Tare da ila suka dawo tunda yaga mota yasan bak'i sukayi yana shiga kuwa Inna tace Maman marigayi ce tazo, d'akin ya shiga suka gaisa da Mama Inna kuma ta kawo mata dambu ta kaiwa su INdo ma. A nan Mama ta kuma tsara malam Hamza yayi jim sannan kamar bazai yadda ba sai kuma yayi murmushi yace.
"Toh ai dama ni hajiya dalilin daya sa na kafe kan cewar saita dawo nan, gani nayi yadda shi Saddiqu suke tsananin kama dashi marigayin. Sannan tun a gurin gaisuwar naji ana zance ta fara rik'esa tana cewa be mutu ba harma sun fara samun sa6ani itada Saddiqun wannan dalilin yasa nace dole abani ita mu dawo nan zaman lafiya hajiya ai yafi zama d'an sarki. Amma yanzu tunda akwai wani dalili wanda kuma kune kuke da hakk'i akai toh saita shirya ku tafi idan an kammala yi mata sai a dawo da ita ai duk an zama guda.."
Wani farin ciki ya lullu6e Mama sai ta share hawaye gani takeyi tamkar Abubakar d'in take yiwa a zahiri. Malam Hamza ya dinga bata hak'uri kafin ya tashi ya fita, gurin su INdo yaje yace ta shirya zasu tafi da ita.
Wanka Mama tace tayi sannan tayi tasa kaya Mama ta girgiza kai domin duk kayan na kwalliya ne babu wanda aka ce na takaba ne dole idan sunje tasa a dinka mata wasu marasa style. Babu wanda yasani don Mama tace kar a fad'awa kowa kawai idan an tambaya tana Ina suce tana gidan su marigayi amma karsu sanar da kowa akwai abinda za'ayiwa INdo suka tafi cikin farin ciki da fatan alkairi.
*****
Tunda suka maida ita Mama ta dakatar da Sadeeq zuwa gidan tace koda itace batada lafiya bata yadda ya shigo ba bare hakan nan. Haka kuka Mama ta cigaba da kula da INdo har aka yi arba'in d'in marigayi Abubakar sannu a hankali kuma Mama tana bibiyar al'amranta na addini tana gyara mata sannan tana k'ara nusar da ita abubuwa wad'anda mafi akasari suke k'ara tunawa INdo mijinta soyayyarsa kuwa bata ta6ajin ta kankare koda d'igo d'aya ne, bata komai sai dai taci tasha tayi bacci, idan kuma su Haleema na nan sai suyi hira d'an turancin da suke yi jefi-jefi itama ta d'an fara tsintar k'ananun tana had'awa da wanda Dr yake yi mata sai dai dakyar take iya rik'ewa dan sai tayi ta rik'e kalma d'aya a kwana biyu ko uku sannan take sake fahimtar wata word d'in.
Kusan kullum sai Malam Hamza ya bugo musu waya tunda suka zo sadakar arba'in ya kar6i number abban su Sadeeq kusan kullum sai ya bugo musu yaji wai ko an cire mata abun sai suce a'a likitocin sun k'ara musu kwanaki da haka har INdo tayi watannin takabar ta wanda har lokacin Sadeeq baya shiga cikin gidan su dan ma Allah ya temake sa yana tafiya k'wara state dan wannan tafiyar tasa da Fateema sukayi sabida yana shan wahala.
Ana sauran kwana biyu INdo ta kammala takaba su Sadeeq suka dawo, Fateema ce kawai taje gidan shi kuma su Mama suka fita parking space suka gaisa ya juya ya tafi.
Ranar da INdo ta kammala takaba Abba ya k'ira Sadeeq yaje ya kaisa Sumaila suna zuwa ya samu malam Hamza bayan gaisuwa Sadeeq na mota a zaune ya bugawa Fateema waya suna hirar soyayyar su dan haka suke tamkar zasu cinye junansu Abba ya kalli malam Hamza yace.
"Toh malam Abubakar dai Allah ya d'auki rayuwarsa a lokacin da yake tunanin ya fara rayuwa, ya tafi yabar matarsa yarinya d'anya yau gashi Allah yasa ta kammala takabarta kamar yadda addini ya tanadar. A zahirin gaskiya ba wani abu da marigayi ya sanyawa Aisha a jikinta, me d'akina ce taga bazata iya barin muku Aishan ba hakan yasa tayi muku dabara kuka bata ita mu kuma duk muka had'e muku kai muka nuna cewar eh lallai haka ne abinda ta fad'a."
Malam Hamza yayi murmushi tare da cewa.
"Ai munyi mamaki har muna tunanin k'ila abin k'in fita yayi ashe soyayya ce tasa kukayi hakan ai bakomi alhaji mune da godiya da baku nuna kyama a garemu ba, Habubakar shine sila hakan yasa bazan gajiya dayi masa addu'ar samun ni'ima a cikin makwancinsa ba, alhaji Allah yajik'ansa yayi masa rahama mun gode madallah."
"Ba komai malam Aisha ma ai 'yata ce, sannan kuma babban abinda ke tafe dani shine. Kaf 'yan uwana da masu d'akina suna tausayawa Aisha, yarinya ce d'anya yau gashi Allah ya jarabce ta idan aka barta zata Shiga layin zawarci, sun had'u sun had'e kai wajan ganin bazasu iya bari matar d'ansu d'an uwansu abokinsu ta zauna a haka ba suna ganin yi mata hakan kamar basu rufawa Abubakar asiri ba hakan yasa ko wannen su yazo min da k'ok'an barar su na cewar mezai hana a mayeta da abokin haihuwar sa, ma'ana mu had'asu aure da Sadeeq domin rufin asirin mu gabaki d'aya sannan munsan Abubakar zai yi alfahari da wannan abun."
Malam Hamza yayi shiru kafin yaje ya k'ira Inna ya kuma k'ira amininsa malam kallah suka zauna, Abba ya kuma maimaita musu zancen auran INdo da Sadeeq Inna dai bata ce komai ba tace sune maza masu d'aura aure dan haka ita addu'a ce kawai tata. Bayan Inna ta koma gida malam Hamza ya amince wasu mutanan suka zo a gurin aka d'aura auran INdo da Sadeeq Abba ya bada sadaki dubu ashirin Sadeeq yana mota a zaune duk wainar da aka toya besani ba har Abba yayi sallama da mutanan garin ya shiga mota Sadeeq d'in ya ajiye wayar suka tafi...
#Fan's
#luv-all
*HAJJA CE*
[7/31, 5:13 PM] Aisha Galadima: *
MUSAYAR ZUCIYA...
*K.A.S Precious Hajja ce*
*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*
(Home of expert & perfect writer's)
*VOTE me on wattpad @Hajjac*
*DEDICTEED TO:* Sanah Isma'il Matazu
Page *24*
Koda sukaje kauyan Sani bak'aramin mamaki Fateema tayi ba da ganin gidan su INdo da kuma kauyan da suke, lallai Allah ya d'aukakata daya aura mata Abubakar har kuma tashiga wannan uban gidan wanda yafi nata komai da komai. Basu jima ba Sadeeq yace zasu koma ya bada dubu ashirin Inna da malam Hamza suka dinga yi mai godiya amma INdo fateema kawai tayiwa sallama ta koma gida 'yan garin suka cigaba da zuwar musu gaisuwa.
Rayuwa gaba d'aya ta sauyawa INdo komai yayi zafi tunda ta dawo kauyan Sani komai nata ya canza, tana takaba a gidan su kamar yadda malam Hamza ya buk'ata sai dai itace inzata bayan gida sai abata sanda da wuk'a wai ta tafi da ita ko idan zatayi bacci toh ruwanta a buta da wuka wai mijinta yana biye da ita duk da cewar ba'a gidansa takeba. Sannan ta dinga tafiya a hankali karya tad'iyeta. wayace haka ake zaman takaba?wannan ba musulinci ya koyar dashi ba kawai mutanene suka maidashi al'ada har hakan ya fara zama kamar ibada. Satin INdo biyu a gida lokacin sati uku kenan da rasuwar Abubakar su Mama sukaje garin domin ita sam hankalinta ya kasa kwanciya, a zaure suka tarar dasu INdo suna tsinkar zogale harta fara komawa kalarta ta dah gashi dai jikinta da kaya masu kyau amma babu tsafta tunda ta dawo sau biyu tayi wanka wai ai duk cikin takaba ne. su Hawwah suka dinga kallonta cikin tsananin mamaki ita kuwa ta kasa 6oye farin cikinta da ganinsu.
Bayan sun gaggaisa ne Mama ta kasa yin shiru ta kalli INdo dake tsakiyarsu Haleema tace.
"Aisha ya naganki haka?duk kinyi wani iri anya kina wanka da kula da lafiyar jikin ki?!"
Cikin rashin damuwa tare INdo tace.
"Ai Mama nida nake takaba ai ance ba'a wanka sai dai a sati sau d'aya shi yasa ma banayi..."
"Subahanallahi inji waye ya gaya miki haka?"
INdo tace "Su Inna ne."
Inna nacan tana k'ok'arin had'a dambu ta samu tabasu suci Mama tace.
"Zonan Aisha na shiga uku ba haka ake yi ba a musulunci, ba haka qur'ani ya gaya mana ba."
Tashi INdo tayi zuwa kusa da Mama ta zauna Mama na kallonta cikin tsananin tausayawa ta janyo ta jikinta tace.
"Mecece Takaba Aisha?!"
INdo tayi shiru sai faman wulk'ita idanuwa takeyi Mama tace.
"Aisha Takaba dai itace Zaman da mace zatayi bayan rasuwar megidanta na wad'ansu kwanaki sanannu a cikin gidanta batare da tayi ado da kwalliya ba, ba kuma data kuma yin wani auren ba, ko sanya dukkan abinda zai ja hankalin wani a jikinta ba na tufafi ko kayan k'arau. Aanan Takaba ta sha babban da Iddar saki, shi yasa naso a barki a can domin d'an zaman da kikayi a gidan mu na gano cewar kinada gyara a cikin rayuwarki. Banda iyayanki sun kafe kancewar gara kitafi babu me zuwa ya zauna dake a cikin gidanki sannan kowa yasan mijinki ya rasu gashi idan kikaga Sadeeq wani tashin hankalin ne da bazan bari ba wallahi yanzu gashi kinzo nan sun k'ara dilmiyar dake cikin wani duhun kan.
Wallahi mahaifinki gaddama garesa Aisha ba yadda ba'ayi dashi ya barki ba yace dasun dawo bakwai za'a tafi dake sabida baya son abinda kikewa Sadeeq. Shin kinsan Gwargwadon kwanakin Takaba a musulunci Aisha?"
INdo ta girgiza kai alamar a'a Mama ta d'ago ta daga jikinta tace.
"Alokacin da mutun ya rasu, to zai bar iyalin shi ne a d'ayan hali guda biyu, kodai ta zama tanada Juna biyu ko kuma bata da shi. Idan bata da juna biyu to Takabarta itace tayi Wata hud'u da kwanaki goma Kamar yadda Allah yace cikin Suratul-Bak'ara _Kumma dukkanin mazan dake rasuwa daga cikin ku subar matayan su, to matan zasu zauna wata hud'u da kwana goma aya ta d'ari biyu da talatin da hud'u 234..._
To amma idan ya rasu ya barta da juna biyu a wannan lokacin k'arshen Takabarta shine ta sauk'e abinda take dauk'e da shi koda kuwa ranar da ya rasu ne ma'ana ta haihu ko tayi 6arin cikin. Misali ya rasu 10:00am na safe ita kuma ta haihu 10:05 na safiyar, shi k'enan ta kammala takabarta, idan wani ya gani yace yana so aka d'aura aure 2:30 na ranar aure ya d'auru _(ana k'ar6ar gaisuwa ana d'aurin aure)_ Dalili kuwa shi ne. fad'in Allah (s.w. a) a cikin Suratut-Talak aya ta 4 _Kuma dukkanin mata masu juna biyu to lokacinsu shine su sauk'e abinda suke d'auk'e dashi_ da kuma Hadisin Subai'a Al-aslamiyyah, Ita ta kasance tana auran Sa'ad Dan Khaulah, shi kuma ya fito ne daga gidan Amir d'an Lu'ayy, yana daga cikin wad'an da suka halarci yak'in Badar, sai ya rasu yabarta a halin bankwana tana da juna biyu, bata ko jima ba bayan rasuwar shi saita haihu, a lokacin data kamma biki sai tai kwalliya, sai Abu-Sanabil Dan Ba'akk yazo wurinta, shi kuma ya fitone daga gidan Abduddar, sai yace da ita Lafiya naga kin cancara ado haka, ko kina son ki aure ne? Na rantse da Allah lokacin auranki bai yi ba, harsai kin yi wata hud'u da kwana goma. Sai Subai'a tace Yayinda ya fad'a min haka maraice na yi sai na tattara kayana naje wurin Ma'aikin Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi, na tambaye shi hakan, sai ya ban amsa da cewa ai na kamala Takabata tun lokacin dana haihu, ya ban dama da inyi aure a duk lokacin da naga dama. Yanzu ke Aisha kina da ciki?!"
INdo ta kalli Yayya Hawwah kafin ta maida idonta kan Mama tace "Wallahi ban sani ba nima." Mama ta sake kallonta sannan tace.
"Kinyi al'ada sanda kika dawo?!"
INdo ta sunkuyar da kai sannan tace,
"Ai yanzu ma haka inayi yau kwanana biyu kenan."
"Hazbunallahu wani'imal wak'il, yanzu duk da kina wannan jinin Aisha bakya wanka?!"
INdo tayi shiru jin yadda Mama tayi magana da alama abin mamaki ya bata da haushi ita kuma ya zatayi tunda ance mata haka akeyi. Inna ce ta shigo tana tayi musu sanna tare da kawo musu ruwa a kwanan shin ruwan malam Hamza, tsabtar kyawun kwanon da yadda ruwan ciki yake garai-garai abin sha'awa shine ya sanya su Haleema shan ruwan gidan.
Zama Inna tayi suka sake gaisawa Mama tayi gyaran murya bayan tace su Haleema su fita, suna fita tayi murmshi tare da cewa.
"Dama munzo ne mu gaida ku sannan zamu tafi da Aisha za'ayi mata wani gwajin ciki sabida shi marigayi yace yasa mata wani abu wanda koda tana da ciki toh bazata dena jinin al'adaba toh yanzu shine zamuje a duba agani kar abar mata abu ba'a saniba ko yana amfani nan da kwana biyu za'a dawo da ita kinsan likitocin nan da k'ak'ale."
Mama ta kifa Inna domin yanzu so take ta tafi da INdo can. cikin rashin damuwa Inna tace "Allah sarki ai babu komai an zama d'aya bari na aika a k'ira malam dama shine ai ke hanawa da yaji yadda takeyi idan taga shi d'an uwan marigayin."
Fitowa tayi ta lek'a waje ta samu yaro yaje ya k'ira Malam Hamza a gurin sana'ar Sa. Tare da ila suka dawo tunda yaga mota yasan bak'i sukayi yana shiga kuwa Inna tace Maman marigayi ce tazo, d'akin ya shiga suka gaisa da Mama Inna kuma ta kawo mata dambu ta kaiwa su INdo ma. A nan Mama ta kuma tsara malam Hamza yayi jim sannan kamar bazai yadda ba sai kuma yayi murmushi yace.
"Toh ai dama ni hajiya dalilin daya sa na kafe kan cewar saita dawo nan, gani nayi yadda shi Saddiqu suke tsananin kama dashi marigayin. Sannan tun a gurin gaisuwar naji ana zance ta fara rik'esa tana cewa be mutu ba harma sun fara samun sa6ani itada Saddiqun wannan dalilin yasa nace dole abani ita mu dawo nan zaman lafiya hajiya ai yafi zama d'an sarki. Amma yanzu tunda akwai wani dalili wanda kuma kune kuke da hakk'i akai toh saita shirya ku tafi idan an kammala yi mata sai a dawo da ita ai duk an zama guda.."
Wani farin ciki ya lullu6e Mama sai ta share hawaye gani takeyi tamkar Abubakar d'in take yiwa a zahiri. Malam Hamza ya dinga bata hak'uri kafin ya tashi ya fita, gurin su INdo yaje yace ta shirya zasu tafi da ita.
Wanka Mama tace tayi sannan tayi tasa kaya Mama ta girgiza kai domin duk kayan na kwalliya ne babu wanda aka ce na takaba ne dole idan sunje tasa a dinka mata wasu marasa style. Babu wanda yasani don Mama tace kar a fad'awa kowa kawai idan an tambaya tana Ina suce tana gidan su marigayi amma karsu sanar da kowa akwai abinda za'ayiwa INdo suka tafi cikin farin ciki da fatan alkairi.
*****
Tunda suka maida ita Mama ta dakatar da Sadeeq zuwa gidan tace koda itace batada lafiya bata yadda ya shigo ba bare hakan nan. Haka kuka Mama ta cigaba da kula da INdo har aka yi arba'in d'in marigayi Abubakar sannu a hankali kuma Mama tana bibiyar al'amranta na addini tana gyara mata sannan tana k'ara nusar da ita abubuwa wad'anda mafi akasari suke k'ara tunawa INdo mijinta soyayyarsa kuwa bata ta6ajin ta kankare koda d'igo d'aya ne, bata komai sai dai taci tasha tayi bacci, idan kuma su Haleema na nan sai suyi hira d'an turancin da suke yi jefi-jefi itama ta d'an fara tsintar k'ananun tana had'awa da wanda Dr yake yi mata sai dai dakyar take iya rik'ewa dan sai tayi ta rik'e kalma d'aya a kwana biyu ko uku sannan take sake fahimtar wata word d'in.
Kusan kullum sai Malam Hamza ya bugo musu waya tunda suka zo sadakar arba'in ya kar6i number abban su Sadeeq kusan kullum sai ya bugo musu yaji wai ko an cire mata abun sai suce a'a likitocin sun k'ara musu kwanaki da haka har INdo tayi watannin takabar ta wanda har lokacin Sadeeq baya shiga cikin gidan su dan ma Allah ya temake sa yana tafiya k'wara state dan wannan tafiyar tasa da Fateema sukayi sabida yana shan wahala.
Ana sauran kwana biyu INdo ta kammala takaba su Sadeeq suka dawo, Fateema ce kawai taje gidan shi kuma su Mama suka fita parking space suka gaisa ya juya ya tafi.
Ranar da INdo ta kammala takaba Abba ya k'ira Sadeeq yaje ya kaisa Sumaila suna zuwa ya samu malam Hamza bayan gaisuwa Sadeeq na mota a zaune ya bugawa Fateema waya suna hirar soyayyar su dan haka suke tamkar zasu cinye junansu Abba ya kalli malam Hamza yace.
"Toh malam Abubakar dai Allah ya d'auki rayuwarsa a lokacin da yake tunanin ya fara rayuwa, ya tafi yabar matarsa yarinya d'anya yau gashi Allah yasa ta kammala takabarta kamar yadda addini ya tanadar. A zahirin gaskiya ba wani abu da marigayi ya sanyawa Aisha a jikinta, me d'akina ce taga bazata iya barin muku Aishan ba hakan yasa tayi muku dabara kuka bata ita mu kuma duk muka had'e muku kai muka nuna cewar eh lallai haka ne abinda ta fad'a."
Malam Hamza yayi murmushi tare da cewa.
"Ai munyi mamaki har muna tunanin k'ila abin k'in fita yayi ashe soyayya ce tasa kukayi hakan ai bakomi alhaji mune da godiya da baku nuna kyama a garemu ba, Habubakar shine sila hakan yasa bazan gajiya dayi masa addu'ar samun ni'ima a cikin makwancinsa ba, alhaji Allah yajik'ansa yayi masa rahama mun gode madallah."
"Ba komai malam Aisha ma ai 'yata ce, sannan kuma babban abinda ke tafe dani shine. Kaf 'yan uwana da masu d'akina suna tausayawa Aisha, yarinya ce d'anya yau gashi Allah ya jarabce ta idan aka barta zata Shiga layin zawarci, sun had'u sun had'e kai wajan ganin bazasu iya bari matar d'ansu d'an uwansu abokinsu ta zauna a haka ba suna ganin yi mata hakan kamar basu rufawa Abubakar asiri ba hakan yasa ko wannen su yazo min da k'ok'an barar su na cewar mezai hana a mayeta da abokin haihuwar sa, ma'ana mu had'asu aure da Sadeeq domin rufin asirin mu gabaki d'aya sannan munsan Abubakar zai yi alfahari da wannan abun."
Malam Hamza yayi shiru kafin yaje ya k'ira Inna ya kuma k'ira amininsa malam kallah suka zauna, Abba ya kuma maimaita musu zancen auran INdo da Sadeeq Inna dai bata ce komai ba tace sune maza masu d'aura aure dan haka ita addu'a ce kawai tata. Bayan Inna ta koma gida malam Hamza ya amince wasu mutanan suka zo a gurin aka d'aura auran INdo da Sadeeq Abba ya bada sadaki dubu ashirin Sadeeq yana mota a zaune duk wainar da aka toya besani ba har Abba yayi sallama da mutanan garin ya shiga mota Sadeeq d'in ya ajiye wayar suka tafi...
#Fan's
#luv-all
*HAJJA CE*
[7/31, 5:13 PM] Aisha Galadima: *
MUSAYAR ZUCIYA...