Sashe 30
Musayar Zuciya Part 1 Complete Hausa Novel · about 11 min read
A true life story
*K.A.S Precious Hajja ce*
*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*
(Home of expert & perfect writer's)
*VOTE me on wattpad @Hajjac*
*DEDICTEED TO:* Sanah Isma'il Matazu
Page *25*
Har sukaje gida Abba be sanar da Sadeeq ba, suna zuwa Abba ya shiga gida shi kuma Sadeeq daya k'agu yaje gida ya juya kan motar ya tafi. Abba na zuwa fuskarsa cike da fara'a ya cewa su Umma.
"Toh hajiya A'i an d'aura aure yau."
"Alhamdulillah Allah ya sanya musu albarka ya kauda fitina ya basu zaman lafiya."
Cewar Umma nan da nan fa gida ya cika da murna INdo kuwa bacci take a lokacin sai bayan da ta farka ne Mama tace.
"Aisha jeki wanka kizo kuje gyaran kai."
Da sauri INdo ta mik'e cike da murna domin tunda ta dawo gidan bata sake koda lek'awa k'ofar gida ba, sam sun hanata ko unguwa Mama zasu sai ta kafa mata doka akan idan ta kuskura ta lek'a waje, yau gashi zata fita kusan kwananta d'ari da takwas raban da ta kalli waje bare taga abinda yake wakana. Ta yi kyau tayi haske fatar jikinta tayi luf-luf sannan tayi k'iba da yake hankalinta a kwance yake suna kula da ita sosai dan ko 'ya'yan gidan basu kaita jin dad'i ba.
Wanka tayi tana fitowa taga saban d'inki an d'akko mata a can gidan Abubakar da takalmi da jaka da mayafi su d'ankune sark'a da kayan kwalliyar su Haleema. Zama tayi tana kallon kayan tare da shafa jakar da takalmin sai hawaye a fili tace.
"Allah sarki dacta kai ka saimin su.."
Tashi tayi tasa kayan sai ga Mama ta shigo cikin wasa tamkar ba suruka ba tace.
"Toh wa kika tambaya da kika d'auka kika sa? Idan kuma nawa nefa..?!"
Dariya INdo tayi tana rufe baki tace,
"Ai Mama ina ganin jakar na gane su, lokacin da zai kaimu gidan abokanansa da nad'akko zan rataya yace min basu yi match da kaya na ba na ajiye ta."
"Allah sarki Abubakar Allah yayi masa rahama Allah yayi baxaku yi tsawon kwanaki tare ba."
Cewar Mama tana d'akko mata humra ta ajiye mata a kusa da kayan tana cewa.
"Daga yau zaki iya sanya komai Aisha sai dai zaki ci gaba dayin abubuwa irinna matan aure domin yanzu kema Matar aure ce."
Sam INdo bata gano inda zancen Mama ya nufa ba, a tunaninta tunda ta ta6a aure toh zata ci gaba da suturce jikinta da kuma d'ora mayafi aka. Tana gama shiryawa Mama ta bata kud'in gyaran kai tasa suka tafi dasu Haleema.
Lokacin da ta fara zura k'afarta a waje ji tayi tamkar yau aka haifeta. Wata ajiyar Zuciya ta sauk'e tare da kallon ko'ina na wajan taga mutane kowa yana harkar gabansa, wasu kuma da suka santa suna sake yi mata gaisuwa tana amsa musu har suka kai bakin titi Haleema ta tare musu napep suka shiga.
Shagon saloon suka shiga sun d'an jima sannan suka fito suka dawo gida. Da dare bayan Abba ya dawo ya k'ira Sadeeq sannan ya k'ira INdo, Mama da Umma duk suna zaune a d'akin. Cikin muryar ta med'an k'arad'i tayi sallama tare da shiga ta zauna tana gaida Abba.
A hankali Sadeeq ya d'ago ya kalleta sannan ya kawar da kai cikin ransa yana tambayar dama tana da ladabi ko kuwa har lokacin mutuwar mijinta na jikinta ta dai kusa tafiya shima ya samu 'yancin shiga gidan ubansa.
Abba ne ya k'ira sunansa ya amsa tare da kallonsa abban yace.
"Toh Sadeeq kamar yadda ka sani tagwai d'inka Allah yayi masa rasuwa ya bar matarsa, yau kuma Allah ya nuna mana cikar wa'adin takabar ta kamar yadda addini ya d'ora mata. Sadeeq kaine mutum na farko daya kamata ya rufawa matar d'an uwanka asiri ka dubi halin da zata shiga idan ta koma garin su ka kuma dubi k'ank'antar da tayi a matsayin bazawara bawai munaja da ikon Allah bane a'a duba da yadda rayuwarta zata fad'a yasa muka yanke wani hukunci akai."
"Babu komai Abba ni dama tuni nayi alk'awarin zan dinga tura mata kud'i sannan zan dinga yi mata abinda take buk'ata idan har befi k'arfina ba dama jira nake ta kammala iddar sai na tambaye ta abinda yak'e matsalarta."
Sadeeq ya fad'a ba tare da ya kawo komai ba dan sam beyi tunanin wani aure tsakaninsa da ita ba, Fateema yake so kuma ita ya aura baya tunanin zai yi *MUSAYAR ZUCIYA* da watanta nan gaba bare kuma nan kusa daga yin aure wata biyar.
"Toh Sadeeq ai wannan abubuwan daka fad'a koni zan iya yi mata shi, mu yanzu fatan mu ka rufa mata asiri a matsayin ta na mace me rauni kuma matashiya domin a d'azu da ka kaini Sumaila k'auyan su naje ne mun d'aura muku aure dakai da ita ka maye gurbin d'an uwanka...!"
A matuk'ar razana Sadeeq ya zaro idanuwa yana kallan Abban shi, zuciyar sace take rawa jikinsa na tsuma ya kalleshi yace.
"Abba wani auran zan kuma yi? Abba ko wata biyar ban cikasa ba ace na kuma yin aure? Tayaya zan iya zama da mata biyu Abba bayan yanzu nayi d'ayan? Abba matar twin d'in zan aura? Ya akayi mutuwa tayi min haka..."
"Kai ya isa haka karkayi min sakarci kaji ko? Idan baka aureta ba ya kakeso tayi bayan tana buk'atar temako da kuma mai lallashi da tausayawa a gareta...?!"
"Amma Abba yau yau d'innan fa tayi takaba amma ace ayau za'a aura mana aure ko fuskanta juna bamuyi ba? Abba ya Fateema zataji wannan labarin."
Ya fad'a tamkar wani maraya Abba ya wurga mai harara cikin 6acin rai yace,
"Da kuma ace kaine ka rasu aka ce Abubakar ya auri Fateeman zakaji dad'i ko kafison ta tafi ta auri wani bare..?!"
"Wallahi Abba gara ta auri bare haba-haba sai kace jira, dan Allah Abba kuyi tunani ni wallahi..."
Bek'arasa ba Abba yayi saurin katse sa ta hanyar cewa.
"Toh shikenan sakarta ni sai na aureta shikenan hakan yayi maka.?!"
Cikin tashin Hankali Sadeeq ya kalli mahaifinsa sai zuba uban gumi yake baki na rawa yace.
"Innalillahi wa'inna'ilaihir raji'un Abba ai babu aure tsakanin ku gara nid'in."
"A'ah aini tausayinta nakeji Sadeeq kuma abinda zanyiwa Abubakar kenan yasan nayi mai kara ka sake ta sai na aureta ko kuma uncle d'inku Ahmad."
"A'a Abba dan Allah ka rufa mana asiri na kar6i auran Allah yajik'an m twinnie yasa can tafiye masa nan."
Duk suka amsa da amin banda INdo wadda tunda taji maganar da akeyi tayi kicin-kicin zuciyarta banda bugawa babu abinda takeyi wani rad'ad'i na shigarta. Abba ya maida hankali wajan ta ya kalleta cikin kulawa yace.
"Aisha muna fatan bamuyi miki shishigi a cikin rayuwarki ba, muna fatan zaki yadda da auran Sadeeq gashi nan komai nashi iri d'aya ne dana marigayi..."
Da sauri INdo tace "A'ah Abba wallahi ba halinsu d'aya ba koda can kafin mu saba."
Abba ya kalli Mama itama shid'in take kallo sannan tace.
"Aisha ai shima Sadeeq zai miki abinda marigayi yayi miki kiyi hakuri idan kuma bakya sonshi shikenan ai ke yanzu babu batun yi miki auran dole za6i gareki a wannan karan ma. Dama munyi haka ne dan karki shiga damuwa ko da idan kinga Sadeeq d'in."
Shiru tayi batace komai ba sukayi-sukayi tayi magana amma tayi shiru Umma tace.
"Toh da alama ta yadda Allah ya bada zaman lafiya."
Tashi Sadeeq yayi ya fita Mama da INdo suma suka fita aka bar Umma kasan cewar itace da girki ranar.
Dakyar ya iya kai kansa gida, lokacin daya shiga Fateema na kwalliya cikin bedroom taji shigowarsa amma bata ga ya shigo d'akin ba, shi kuwa guri ya samu a falo ya zauna kan kujera tare da dafe k'irji kanshi na barazanar fashewa ya tarwatse.
Fateema ce ta fito cikin shirin bacci tayi kyau ta kuma fari kai da kaganta kasan tana cikin kwanciyar hankali, k'arasawa tayi kusa dashi ta d'are kan cinyarsa tana k'ok'arin d'ago mai kai. Janyo ta yayi jikinsa da k'arfi tare da sanya ta a k'irjinsa ya matseta da hannuwansa tamkar zai maida ita ciki ita kanta dakyar take numfashi zuciyar ta cike da mamakin yadda taganshi.
"Wayyo Allah baby zaka karya ni."
Ta fad'a tana k'ok'arin kwatar kanta sabida ba k'aramin azaba takesha a matsar ba. A hankali ya sassauta mata rik'on dayayi mata cikin sanyin murya Fateema ta kallesa tace.
"Baby wai meyake damunka, haka kashigo fa ba sallama kuma naga duk jikinka a sanyaye meya faru..?!"
"Bakomai kinci abinci dai ko?!"
Ya tambaya yana shafar cikinta, kad'a kai tayi tana kallon shi ya lumshe idanuwa tare da kwantota jikinsa yace.
"Toh why?!"
"Baby kasan dai bana iya ci harsai kana nan, meyasa yanzu kake tambaya na...?!"
"Kinsan ai bana son kina zama da yinwa, kinga gobe ina da lecture 9 to 11 kuma gashi banajin dad'in jikina ya zanyi ne.."
Fuskar sa ta tallafo sukayi kallon cikin ido ta sakar masa murmushi tana shafar gashin dake ha6arsa tace.
"Yanzu ai lokaci bek'ure ba goma da rabi saura minti uku kayiwa class captain waya kace musu bazaka samu damar zuwa ba suyi hakuri zaka samu wani time d'in sai kuyi musu amfani dashi..."
"Ai kuma baby ban musu lectures bafa tunda aka koma gashi har an fara tambaya na exam questions, zanje ko abu d'aya ne nayi musu tashi muje kici abinci."
"Inci abinci ko dai muci abinci?!"
Ta tambayesa tana sake lafewa a jikinsa, suna zama yana cewa.
"Kinsan Abba neya k'irani so munci abinci tare dashi."
'Dan hararasa tayi tare da cewa "Ai kasan dai nima nawa yana jiranka dan haka sai kaci babu wani batun kunci da Abba ko zakayi amai kuwa."
Shi sam yarasa ma mezai yi yinwar ma bajinta yake yi ba shi yasa yace mata haka amma dan karta shiga damuwa sai yace.
"Toh baby na ya zanyi amma nasan yau babu abinda zan iya tabuk'awa."
Shi dai dakyar ya samu yaci duk tunanin yadda zai 6ullo mata yake yi a cikin zuciyarsa, sai da ya tabbatar taci ta koshi sannan ta rakashi yayi wanka ta bashi sleeping gown ta maza yasa sannan suka bi lafiyar gado. Kamar yadda ya sabar mata koda bazai yi komai ba toh sai sunyi wasa haka yauma har sai da yaga ya kwantar da kanta kan k'irjinsa zata yi bacci ya bud'e baki dakyar ya k'ira sunanta.
"Zarah..."
Tayi jimmm jin yadda ya k'ira tsohon sunan da yake kiranta dashi tun suna saurayi da budurwa, can dai ta amsa mai tana shafar k'irjinsa shi kuma yana shafar himilin gashin kanta domin akwai suma yace.
"For example nine na rasu ba Abubakar ba idan aka ce ki auresa zaki iya..?!"
Ya k'arasa maganar yana d'an d'ago mata kai. Shiru tayi na tsawon lokaci tana tunanin abinda yasa shi yi mata wannan tambayar marar dad'in ji bare sauraro, sai da ya sake tambayar ta sannan ta numfasa dakyar tace.
"Haba baby ya zaka min wannan tambayar tunda dai bakai ne ka rasun ba?"
Yace "Eh so nake naji zaki yadda idan aka ce ki auri twinnie d'ina ya zakiyi."
"Gaskiya bazan auresa ba haba ai bashi na aura ba."
"Toh idan aka tursasa kifa ko aka aura miki shi ba tare da kin sani ba ya zajiyi..?!"
"Ta6 d'i wallahi baby sai ya sakeni uhm'um ni dan Allah ka dena yin irin wannan tunanin please."
Jikinsa ya sake janyo ta yana shafar bayanta, so yake ya sanar da ita yau basai taji a bakin wani ba amma ya rasa hanyar fad'ar ya dai daure yace.
"Toh idan hakan ta faru tunda ni bakya sona mutu aka ce na auri Humairah ya zakiyi?!"
"Bama zata yiwu ba sabida INdo bata sanka har agabana ta fad'a."
Shiru suka yi na tsawon lokaci gashi dare ya tsala ko'ina yayi shiru sai k'arar gen d'insu kawai akeji. Numfasawa Sadeeq yayi tare da janyota yace.
"Kiyi hakuri baby na yanzu dawowar da kikaga nayi Abba ne ya sanar da ni cewar an d'aura min aure da ita ni kaina ba..."
Jiyayi ta mik'e zaune a razane daga ita sai bra domin rigar ta zame Fateema ta bishi da kallo hannunta dafe da k'irji ya kalleta bayan shima ya tashi zaune. Wata shegiyar harara take wurga mai cikin zafin rai ta fara magana jikinta na rawa.
"Yanzu kana nufin har an d'aura muku aure?"
Sadeeq ya d'aga mata Kai alamar eh yasa hannunsa ya janyo ta a hankali ta fad'a jikinsa ta saki kuka me ban tausayi ya fara lallashinta shi kansa ji yake tamkar yaje ya bindige INdo. Babu yadda zatayi ita kuma haka tata k'addarar take daga yin aure sai kishiya suna cikin more rayuwarsu.
A 6angaran INdo kuwa wani uban nishi ta dinga saukewa duk iya k'ok'arin Mama na ta gaya mata matsalar ta sam tayi shiru tak'i yin magana har gari ya waye bata yiwa kowa magana ba Mama ta rasa dalili dan ta saki ranta yasa Mama cewa.
"Aisha gobe za'a kaiki gida kije kiyi kwana biyu kafin Sadeeq d'in ya ware yadda zai yi."
Sai a sannan INdo tayi magana tana dariya tace.
"Toh Mama amma dai ba shine zai maida niba...?!"
"Toh ai Aisha yanzu dai komai yana hannunsa sai abinda yace kiyi mai biyayya kedai anan zaki samu aljanna."
Ba zato cikin subutar baki tace.
"Ta6 d'ijam.."
Mama ta kalleta cikin mamaki amma sai taga INdon na mutsu-mutsu da baki alamar magana take a ranta lallai yaran nan da alama zasu basu mugun mamaki sam basuyi zaton INdo zatak'i Sadeeq ba ganin yadda suke kammani da mijinta ba....
#Fan's
#luv-all
*HAJJA CE*
[7/31, 5:13 PM] Aisha Galadima: *
MUSAYAR ZUCIYA...
*K.A.S Precious Hajja ce*
*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*
(Home of expert & perfect writer's)
*VOTE me on wattpad @Hajjac*
*DEDICTEED TO:* Sanah Isma'il Matazu
Page *25*
Har sukaje gida Abba be sanar da Sadeeq ba, suna zuwa Abba ya shiga gida shi kuma Sadeeq daya k'agu yaje gida ya juya kan motar ya tafi. Abba na zuwa fuskarsa cike da fara'a ya cewa su Umma.
"Toh hajiya A'i an d'aura aure yau."
"Alhamdulillah Allah ya sanya musu albarka ya kauda fitina ya basu zaman lafiya."
Cewar Umma nan da nan fa gida ya cika da murna INdo kuwa bacci take a lokacin sai bayan da ta farka ne Mama tace.
"Aisha jeki wanka kizo kuje gyaran kai."
Da sauri INdo ta mik'e cike da murna domin tunda ta dawo gidan bata sake koda lek'awa k'ofar gida ba, sam sun hanata ko unguwa Mama zasu sai ta kafa mata doka akan idan ta kuskura ta lek'a waje, yau gashi zata fita kusan kwananta d'ari da takwas raban da ta kalli waje bare taga abinda yake wakana. Ta yi kyau tayi haske fatar jikinta tayi luf-luf sannan tayi k'iba da yake hankalinta a kwance yake suna kula da ita sosai dan ko 'ya'yan gidan basu kaita jin dad'i ba.
Wanka tayi tana fitowa taga saban d'inki an d'akko mata a can gidan Abubakar da takalmi da jaka da mayafi su d'ankune sark'a da kayan kwalliyar su Haleema. Zama tayi tana kallon kayan tare da shafa jakar da takalmin sai hawaye a fili tace.
"Allah sarki dacta kai ka saimin su.."
Tashi tayi tasa kayan sai ga Mama ta shigo cikin wasa tamkar ba suruka ba tace.
"Toh wa kika tambaya da kika d'auka kika sa? Idan kuma nawa nefa..?!"
Dariya INdo tayi tana rufe baki tace,
"Ai Mama ina ganin jakar na gane su, lokacin da zai kaimu gidan abokanansa da nad'akko zan rataya yace min basu yi match da kaya na ba na ajiye ta."
"Allah sarki Abubakar Allah yayi masa rahama Allah yayi baxaku yi tsawon kwanaki tare ba."
Cewar Mama tana d'akko mata humra ta ajiye mata a kusa da kayan tana cewa.
"Daga yau zaki iya sanya komai Aisha sai dai zaki ci gaba dayin abubuwa irinna matan aure domin yanzu kema Matar aure ce."
Sam INdo bata gano inda zancen Mama ya nufa ba, a tunaninta tunda ta ta6a aure toh zata ci gaba da suturce jikinta da kuma d'ora mayafi aka. Tana gama shiryawa Mama ta bata kud'in gyaran kai tasa suka tafi dasu Haleema.
Lokacin da ta fara zura k'afarta a waje ji tayi tamkar yau aka haifeta. Wata ajiyar Zuciya ta sauk'e tare da kallon ko'ina na wajan taga mutane kowa yana harkar gabansa, wasu kuma da suka santa suna sake yi mata gaisuwa tana amsa musu har suka kai bakin titi Haleema ta tare musu napep suka shiga.
Shagon saloon suka shiga sun d'an jima sannan suka fito suka dawo gida. Da dare bayan Abba ya dawo ya k'ira Sadeeq sannan ya k'ira INdo, Mama da Umma duk suna zaune a d'akin. Cikin muryar ta med'an k'arad'i tayi sallama tare da shiga ta zauna tana gaida Abba.
A hankali Sadeeq ya d'ago ya kalleta sannan ya kawar da kai cikin ransa yana tambayar dama tana da ladabi ko kuwa har lokacin mutuwar mijinta na jikinta ta dai kusa tafiya shima ya samu 'yancin shiga gidan ubansa.
Abba ne ya k'ira sunansa ya amsa tare da kallonsa abban yace.
"Toh Sadeeq kamar yadda ka sani tagwai d'inka Allah yayi masa rasuwa ya bar matarsa, yau kuma Allah ya nuna mana cikar wa'adin takabar ta kamar yadda addini ya d'ora mata. Sadeeq kaine mutum na farko daya kamata ya rufawa matar d'an uwanka asiri ka dubi halin da zata shiga idan ta koma garin su ka kuma dubi k'ank'antar da tayi a matsayin bazawara bawai munaja da ikon Allah bane a'a duba da yadda rayuwarta zata fad'a yasa muka yanke wani hukunci akai."
"Babu komai Abba ni dama tuni nayi alk'awarin zan dinga tura mata kud'i sannan zan dinga yi mata abinda take buk'ata idan har befi k'arfina ba dama jira nake ta kammala iddar sai na tambaye ta abinda yak'e matsalarta."
Sadeeq ya fad'a ba tare da ya kawo komai ba dan sam beyi tunanin wani aure tsakaninsa da ita ba, Fateema yake so kuma ita ya aura baya tunanin zai yi *MUSAYAR ZUCIYA* da watanta nan gaba bare kuma nan kusa daga yin aure wata biyar.
"Toh Sadeeq ai wannan abubuwan daka fad'a koni zan iya yi mata shi, mu yanzu fatan mu ka rufa mata asiri a matsayin ta na mace me rauni kuma matashiya domin a d'azu da ka kaini Sumaila k'auyan su naje ne mun d'aura muku aure dakai da ita ka maye gurbin d'an uwanka...!"
A matuk'ar razana Sadeeq ya zaro idanuwa yana kallan Abban shi, zuciyar sace take rawa jikinsa na tsuma ya kalleshi yace.
"Abba wani auran zan kuma yi? Abba ko wata biyar ban cikasa ba ace na kuma yin aure? Tayaya zan iya zama da mata biyu Abba bayan yanzu nayi d'ayan? Abba matar twin d'in zan aura? Ya akayi mutuwa tayi min haka..."
"Kai ya isa haka karkayi min sakarci kaji ko? Idan baka aureta ba ya kakeso tayi bayan tana buk'atar temako da kuma mai lallashi da tausayawa a gareta...?!"
"Amma Abba yau yau d'innan fa tayi takaba amma ace ayau za'a aura mana aure ko fuskanta juna bamuyi ba? Abba ya Fateema zataji wannan labarin."
Ya fad'a tamkar wani maraya Abba ya wurga mai harara cikin 6acin rai yace,
"Da kuma ace kaine ka rasu aka ce Abubakar ya auri Fateeman zakaji dad'i ko kafison ta tafi ta auri wani bare..?!"
"Wallahi Abba gara ta auri bare haba-haba sai kace jira, dan Allah Abba kuyi tunani ni wallahi..."
Bek'arasa ba Abba yayi saurin katse sa ta hanyar cewa.
"Toh shikenan sakarta ni sai na aureta shikenan hakan yayi maka.?!"
Cikin tashin Hankali Sadeeq ya kalli mahaifinsa sai zuba uban gumi yake baki na rawa yace.
"Innalillahi wa'inna'ilaihir raji'un Abba ai babu aure tsakanin ku gara nid'in."
"A'ah aini tausayinta nakeji Sadeeq kuma abinda zanyiwa Abubakar kenan yasan nayi mai kara ka sake ta sai na aureta ko kuma uncle d'inku Ahmad."
"A'a Abba dan Allah ka rufa mana asiri na kar6i auran Allah yajik'an m twinnie yasa can tafiye masa nan."
Duk suka amsa da amin banda INdo wadda tunda taji maganar da akeyi tayi kicin-kicin zuciyarta banda bugawa babu abinda takeyi wani rad'ad'i na shigarta. Abba ya maida hankali wajan ta ya kalleta cikin kulawa yace.
"Aisha muna fatan bamuyi miki shishigi a cikin rayuwarki ba, muna fatan zaki yadda da auran Sadeeq gashi nan komai nashi iri d'aya ne dana marigayi..."
Da sauri INdo tace "A'ah Abba wallahi ba halinsu d'aya ba koda can kafin mu saba."
Abba ya kalli Mama itama shid'in take kallo sannan tace.
"Aisha ai shima Sadeeq zai miki abinda marigayi yayi miki kiyi hakuri idan kuma bakya sonshi shikenan ai ke yanzu babu batun yi miki auran dole za6i gareki a wannan karan ma. Dama munyi haka ne dan karki shiga damuwa ko da idan kinga Sadeeq d'in."
Shiru tayi batace komai ba sukayi-sukayi tayi magana amma tayi shiru Umma tace.
"Toh da alama ta yadda Allah ya bada zaman lafiya."
Tashi Sadeeq yayi ya fita Mama da INdo suma suka fita aka bar Umma kasan cewar itace da girki ranar.
Dakyar ya iya kai kansa gida, lokacin daya shiga Fateema na kwalliya cikin bedroom taji shigowarsa amma bata ga ya shigo d'akin ba, shi kuwa guri ya samu a falo ya zauna kan kujera tare da dafe k'irji kanshi na barazanar fashewa ya tarwatse.
Fateema ce ta fito cikin shirin bacci tayi kyau ta kuma fari kai da kaganta kasan tana cikin kwanciyar hankali, k'arasawa tayi kusa dashi ta d'are kan cinyarsa tana k'ok'arin d'ago mai kai. Janyo ta yayi jikinsa da k'arfi tare da sanya ta a k'irjinsa ya matseta da hannuwansa tamkar zai maida ita ciki ita kanta dakyar take numfashi zuciyar ta cike da mamakin yadda taganshi.
"Wayyo Allah baby zaka karya ni."
Ta fad'a tana k'ok'arin kwatar kanta sabida ba k'aramin azaba takesha a matsar ba. A hankali ya sassauta mata rik'on dayayi mata cikin sanyin murya Fateema ta kallesa tace.
"Baby wai meyake damunka, haka kashigo fa ba sallama kuma naga duk jikinka a sanyaye meya faru..?!"
"Bakomai kinci abinci dai ko?!"
Ya tambaya yana shafar cikinta, kad'a kai tayi tana kallon shi ya lumshe idanuwa tare da kwantota jikinsa yace.
"Toh why?!"
"Baby kasan dai bana iya ci harsai kana nan, meyasa yanzu kake tambaya na...?!"
"Kinsan ai bana son kina zama da yinwa, kinga gobe ina da lecture 9 to 11 kuma gashi banajin dad'in jikina ya zanyi ne.."
Fuskar sa ta tallafo sukayi kallon cikin ido ta sakar masa murmushi tana shafar gashin dake ha6arsa tace.
"Yanzu ai lokaci bek'ure ba goma da rabi saura minti uku kayiwa class captain waya kace musu bazaka samu damar zuwa ba suyi hakuri zaka samu wani time d'in sai kuyi musu amfani dashi..."
"Ai kuma baby ban musu lectures bafa tunda aka koma gashi har an fara tambaya na exam questions, zanje ko abu d'aya ne nayi musu tashi muje kici abinci."
"Inci abinci ko dai muci abinci?!"
Ta tambayesa tana sake lafewa a jikinsa, suna zama yana cewa.
"Kinsan Abba neya k'irani so munci abinci tare dashi."
'Dan hararasa tayi tare da cewa "Ai kasan dai nima nawa yana jiranka dan haka sai kaci babu wani batun kunci da Abba ko zakayi amai kuwa."
Shi sam yarasa ma mezai yi yinwar ma bajinta yake yi ba shi yasa yace mata haka amma dan karta shiga damuwa sai yace.
"Toh baby na ya zanyi amma nasan yau babu abinda zan iya tabuk'awa."
Shi dai dakyar ya samu yaci duk tunanin yadda zai 6ullo mata yake yi a cikin zuciyarsa, sai da ya tabbatar taci ta koshi sannan ta rakashi yayi wanka ta bashi sleeping gown ta maza yasa sannan suka bi lafiyar gado. Kamar yadda ya sabar mata koda bazai yi komai ba toh sai sunyi wasa haka yauma har sai da yaga ya kwantar da kanta kan k'irjinsa zata yi bacci ya bud'e baki dakyar ya k'ira sunanta.
"Zarah..."
Tayi jimmm jin yadda ya k'ira tsohon sunan da yake kiranta dashi tun suna saurayi da budurwa, can dai ta amsa mai tana shafar k'irjinsa shi kuma yana shafar himilin gashin kanta domin akwai suma yace.
"For example nine na rasu ba Abubakar ba idan aka ce ki auresa zaki iya..?!"
Ya k'arasa maganar yana d'an d'ago mata kai. Shiru tayi na tsawon lokaci tana tunanin abinda yasa shi yi mata wannan tambayar marar dad'in ji bare sauraro, sai da ya sake tambayar ta sannan ta numfasa dakyar tace.
"Haba baby ya zaka min wannan tambayar tunda dai bakai ne ka rasun ba?"
Yace "Eh so nake naji zaki yadda idan aka ce ki auri twinnie d'ina ya zakiyi."
"Gaskiya bazan auresa ba haba ai bashi na aura ba."
"Toh idan aka tursasa kifa ko aka aura miki shi ba tare da kin sani ba ya zajiyi..?!"
"Ta6 d'i wallahi baby sai ya sakeni uhm'um ni dan Allah ka dena yin irin wannan tunanin please."
Jikinsa ya sake janyo ta yana shafar bayanta, so yake ya sanar da ita yau basai taji a bakin wani ba amma ya rasa hanyar fad'ar ya dai daure yace.
"Toh idan hakan ta faru tunda ni bakya sona mutu aka ce na auri Humairah ya zakiyi?!"
"Bama zata yiwu ba sabida INdo bata sanka har agabana ta fad'a."
Shiru suka yi na tsawon lokaci gashi dare ya tsala ko'ina yayi shiru sai k'arar gen d'insu kawai akeji. Numfasawa Sadeeq yayi tare da janyota yace.
"Kiyi hakuri baby na yanzu dawowar da kikaga nayi Abba ne ya sanar da ni cewar an d'aura min aure da ita ni kaina ba..."
Jiyayi ta mik'e zaune a razane daga ita sai bra domin rigar ta zame Fateema ta bishi da kallo hannunta dafe da k'irji ya kalleta bayan shima ya tashi zaune. Wata shegiyar harara take wurga mai cikin zafin rai ta fara magana jikinta na rawa.
"Yanzu kana nufin har an d'aura muku aure?"
Sadeeq ya d'aga mata Kai alamar eh yasa hannunsa ya janyo ta a hankali ta fad'a jikinsa ta saki kuka me ban tausayi ya fara lallashinta shi kansa ji yake tamkar yaje ya bindige INdo. Babu yadda zatayi ita kuma haka tata k'addarar take daga yin aure sai kishiya suna cikin more rayuwarsu.
A 6angaran INdo kuwa wani uban nishi ta dinga saukewa duk iya k'ok'arin Mama na ta gaya mata matsalar ta sam tayi shiru tak'i yin magana har gari ya waye bata yiwa kowa magana ba Mama ta rasa dalili dan ta saki ranta yasa Mama cewa.
"Aisha gobe za'a kaiki gida kije kiyi kwana biyu kafin Sadeeq d'in ya ware yadda zai yi."
Sai a sannan INdo tayi magana tana dariya tace.
"Toh Mama amma dai ba shine zai maida niba...?!"
"Toh ai Aisha yanzu dai komai yana hannunsa sai abinda yace kiyi mai biyayya kedai anan zaki samu aljanna."
Ba zato cikin subutar baki tace.
"Ta6 d'ijam.."
Mama ta kalleta cikin mamaki amma sai taga INdon na mutsu-mutsu da baki alamar magana take a ranta lallai yaran nan da alama zasu basu mugun mamaki sam basuyi zaton INdo zatak'i Sadeeq ba ganin yadda suke kammani da mijinta ba....
#Fan's
#luv-all
*HAJJA CE*
[7/31, 5:13 PM] Aisha Galadima: *
MUSAYAR ZUCIYA...