Sashe 34
Musayar Zuciya Part 1 Complete Hausa Novel · about 10 min read
A true life story
*K.A.S Precious Hajja ce*
*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*
(Home of expert & perfect writer's)
*VOTE me on wattpad @Hajjac*
*DEDICTEED TO:* Sanah Isma'il Matazu
*Godiya mai yawa tare da d'inbin farin cikina zuwa ga fan's, na gode da addu'o'inku garemu munje Lafiya mun dawo lafi na gode sosai da sosai.
HAJARAH (MUM ILHAM) godiya mai tarin yawa a gareki domin kin nuna mana soyayya nida 'yar uwata STYLISH BCH da kuma 'yata IHSAN, Allah ya saka da alkairi ya bar kauna da soyayya Allah ya raya Ilham
UMMUL MEENAL, BILLY S FARI & OLO addu'atw gareku bazata fad'u ba sai dai ince Allah ya baku abinda kuke nema duniya da lahira domin kuna nuna min sayayya ta hak'ik'a HAJJA CE na sonku fiye da yadda kuke nunan kauna.
Page *28*
Tunda suka tafi koda wasa Sadeeq be ta6a gigin k'iran INdo a waya ba, bashi dama phone number d'inta bare yace zai nemeta. A 6angaranta itama bata ko tunaninsa tana gidanta hankalinta kwance babu abinda yake damunta. Ranar da su Sadeeq suka cika sati d'aya da tafiya a ranar INdo ta fara fita, kullum tana gidan mak'ota bata nan layin bata can sam bata zama cikin kwanaki takwas mutanan unguwar sun santa maza da mata yara da manya. Yayin da a 6angaran Sadeeq yana son ya kirata tunda yasan tana da hakki akan sa amma baya kaunar ya kirata tayi mai rashin kunya ko ta gaya mai maganar da zai kasa bacci dan ya lura akwaita da shuka magana ba kuma ta barinta indai harka gaya mai toh zata baka amsa hakan yasa ya shareta.
Misalin k'arfe hud'u ta fito daga wanka tana shafa mai tajiyo me tallah a k'ofar gida, cikin sauri ta janyo doguwar riga a cikin wardrobe ta zura tare da d'aukar mayafi ta fita. A k'ofar gate d'in ta tsaya dan sake tabbatarwa da kunnuwanta abinda me tallar yake cewa still taji yana cewa.
"A sai kajin gidan gona matasa..!"
INdo tayi saurin fita tare da kwala mai k'ira ya dawo baya kasan cewar harya wuce gidan nata. Tsayawa tayi suka fara ciniki zata siya har yace zai siyar mata a yadda cinikin ya tsaya, guda bakwai ta siya ta shiga gida ta d'akko mai kud'in ta bashi ya tafi ita kuma ta shiga da 'yan kajinta sai kuka sukeyi iya-iya-iya tana ta murna taje ta zuba su jikin bathroom d'in tsakar gida dama ba'a shigar sa.
A hankali ta ci gaba da kiwonsu tana bayarwa ana siyo mata abincin su hankalinta a kwance su Haleema idan suka zo suyi ta mata dariya ita kuma tace da tayi kud'i saudiya zata tafi idan ta dawo a dinga k'iranta Hajiya INdo kasan cewar sunan ya bazu cikin gidajen mak'ota k'annan su Sadeeq ne kawai ke kiranta da aunty Humairah kamar yadda marigayi ke fad'a mata.
Rayuwar INdo ta cigaba da canzawa sana'o'i take yi kala-kala kajinta ma sunata girma har ta samu sun fara kwai tana tarawa taci takai gidan su Sadeeq sai da Mama tace ta fara siyarwa sannan ta fara.
Da daddare tana kallon arewa 24 Sumayya tana gabatar da shirin tauraruwa taji yadda wata mata da ake hira da ita yadda rayuwarta ta faro tun daga tushe har yanzu da takai wannan matsayin nan da nan INdo tayi sha'awar yin karatu itama tana son ta iya turanci sai dai tayaya zata iya? Sam kwakwalwarta bata gane turanci ba kuma ta iya rubutawa sannan ba ta iya maida hankali wajan koya tayaya zata iya zama tauraruwa kamar yadda taga ana haskilo mata masu aji ana kuma alfahari dasu, tasa a ranta zata fara koyan turanci kamar yadda marigayi yaso tayi kafin mai rabawa ta rabasu.
Sannu a hankali tana jin takaicin Sadeeq nak'in nemanta tun ranar da Aminatu ta guntsa mata cewar ai dan batajin turanci ne yasa Yaya Sadeeq cewa baxai tafi da ita can ba hakan yasa abin ya kuma ba ta haushi tsanarsa ta kuma hauhawa a cikin zuciyarta dama ya saba yi musu wulak'anci tun a tsefawa.
M.M Haruna English academic taji anata tallar makarantar a gidan redion express, ta fara tunanin yadda zata yi ta samu shiga cikin ta.
Tanason zuwa tana tsoron kar da taje ta tarrar da garzazzu wad'anda basa Hausa sai turancin, wai shin ma meyasa aka maida turanci tamkar saukar alkur'ani da komai za'a ce in zaka yi sai ka iyasa? Ga larabci yaran annabi amma ba a dagewa da zuwa islamiyoyi ba'a basu muhimmanci kamar yadda ake baya yaran jajayan farar fatar nan. idan aka kyaro baka iya bama sai ka zama wani hulugu ka zama abin raini da wulak'anci a wajan al'umma.
Zata yi turanci itama za kuma taje ta koya badan wulak'ancin Sadeeq kad'ai ba sai dan wata rana itama ak'irata ayi hira da ita a kuma tambayeta tauraronta tace Abubakar ne,haka zakila kuma a Dama da ita ita duniya wannan burinta ne ba kuma zata canza shi ba koda Sadeeq zai saketa.
"Hello mubassheer, kana Ina yanzu.?!"
"Ina majalisa ya akayi ta samu ne..?!"
"Kai d'an rainin wayo ne, kazo dan Allah zamuyi sirri."
"Toh aunty Humaira gani nan zuwa amma fa zaki ban jarkar kunun aya guda biyu."
"Dallah idan baxaka zo ba sai na kira khaleefa wallahi."
"Sorry Matar broth ina zuwa."
Kashewa yayi yana dariya sannan ya d'auki abokinsa guda d'aya suka tafi gidan a mashin. A falo suka zauna ta kawo musu kunun ayar da zobo da jallop d'in taliya suka ci sukayi dam sannan mubashsheer ya kalli INdo yana cewa.
"Toh meye sirrin Matar broth, tunda kin bamu munci..!"
Sai da ta hararesa sannan tace mai.
"Dallah kaga ni ba surutu na tambaye ka ba, jujun labo store zaka dan Allah ka siyo min farm (form) d'in shiga makarantar M.M Haruna Englihi menene ma d'ayan na gaban ma oho na manta."
"Ah Matar broth wai kina nufin shiga zaki yi..?!"
INdo tace "Eh ya ranka? Zakaje kayi min duk abinda za'ayi na fara zuwa kokuwa wulak'anci zaka yi min Kai ma..?!"
"Ah Matar broth na isa, kawo kud'in toh sai muje muji ya za'ayi, amma tukunna kin sanar da broth Sadeeq d'in zaki fara ne dan karya zo yayi min masifa."
"Kai zaka siyo min ko kuwa na sake wani?!"
"Ah na isa kawo kud'in muje muji ya za'ayi."
"Toh nawa zan baka..?!"
"Haba ki kawo ten thousand muje mu fara manage dasu."
"Kana nufin nawa kenan?!"
"Kai Matar broth dubu goma zaki kawo naga kina min wani kallo."
"Ta6 goma fa kace? Wallahi ku tafi na fasa ai ba dole."
Ta fad'a tana shiga cikin d'aki Mubasheer ya dinga yi mata magiyar ta fara bada ten thousand d'in tace ta yafe bazata ba sai da yace.
"Toh kawo five thousand, dubu biyar wallahi Matar broth kin fiye san Kud'i da yawa, duk sati dubu biyar broth yake badawa a kawo miki ga kud'in zobo ga kunun aya ga gullisuwa da kwan kaji dan Allah mekikeyi da kud'i bayan duk akwai abinci a gidan..?!"
Dubu biyar d'in ta bashi ya kar6a ya k'irga sannan suka tashi zasu tafi INdo tace.
"Dan Allah k'anin miji a rage sa ido, duk lissafin ka yana kaina toh da ba kud'in zaka ci naman dakaci a cikin abinci ne? Ko zaka ci harda vegetables d'in ne d'an rainin wayo."
"Magana ta wuce bari muje mu dawo."
Yana fad'a suka fice ita kuma ta shiga d'aki. Ko Ina tas-tas a gidanta bata barin k'azanta sannan kullum cikin k'anshin turaran tsinke d'akin yake dan haka INdo tana samun customers a rana sai ta dura jarkokin zobo dana kunun aya guda d'ari biyu a
mma baya kaiwa dare Allah yasanya mata nasibi a ciki.
A ranar bataga Mubasheer ba har kwana biyu sai gashi yazo, tsayawa yayi yace ya gama mata komai zuwa kawai zata farayi domin sai da ya sanar da abban su ya kuma bada goyan baya sosai. Juma'a na zuwa ta fara zuwa cikin tsoro da fargabar yadda zata tun kari malamai da d'alibai dan tasan duk sun fita k'ok'ari.
"Matar broth ga class d'inku nan."
Mubasheer ya fad'a yana nunawa INdo ajinsu. Ido ta dinga kwalowa waje hannun ta na dama dafe da k'irji ta kalli Mubasheer cikin tsoro tace.
"Anya bazan koma gida ba, Mubasheer tsoro nakeji wallahi."
"Kai Matar broth wallahi karkiji tsoro kowa fa da kika gani zuwa yayi a koya mai, idan kika nuna musu kina jin tsoro zasu raina ki kedai karki fasa yin abinda kike so ki shiga kawai."
"Toh bari naje idan mun tashi zan yi maka waya kazo ka maidani gida."
"Toh Matar broth Allah ya bada sa'a."
A hankali INdo ta shiga tashin farko ganin yadda hall d'in yake yasa gabanta bugawa da k'arfi sannan ga d'alibai nan a zazzau ne duk sai ta daburce ta rasa inda zataje cikin sauri ta juya zata fita sai taga Mubasheer a tsaye yana dariya, cikin tsananin jin kunya tace.
"Maidani gida bazan shiga ba."
"Hahaha...! Wallahi babu inda zaki, muje na shigar dake haka kurum dan ayi asarar kud'i sai da aka gama komai zaki wani ce kin fasa."
Yana gaba tana bayansa har ya k'arasar da ita tsakiyar kujerun sannan yayi wa wata budurwa magana cewar gata nan dan Allah ta fara helping d'inta ta wasu abubuwan. Karimatu tayi murmushi tare da mik'awa INdo hannu suka gaisa ta zauna a d'ari-d'ari kamar munafuka sai wulkita idanuwa take a haka Mubasheer ya barta yayi tafiyarsa.
Malami na shiga ta fara sunkuyar da kai, nan aka fara gabatar da lesson kasan cewar ajin masu koyan turanci ne hakan yasa komai ake yi musu dalla-dalla cikin hikima da kuma kwarewar malaman ita dai INdo tayi tsit bata ko kwakwaran motsi dan karma malamin yayi mata tambaya koya saka mata ido. Alhamdulillahi kuma ta tsinto abubuwa kasan cewar sai anta maimaita musu abu anji kowa ya gane an kuma fahimta sannan za'a shiga wani abun haka aka dinga yi musu tana kuma zuwa duk juma'a asabar da lahadi da safe.
****
Wata d'aya da sati biyu su Sadeeq sukayi a kwara state sannan suka juyo suka dawo kano. Lokacin satin INdo biyu da fara zuwa makaranta, sam bata yi wani murna da dawowarsa ba sema haushi da takaici dataji. Sai da yayi kwana biyu a gidan Fateema sannan ya waiwayo yau zaije gidan da INdo take.
K'ofar gidan ta tsaya wajan k'arfe sha biyu na dare, key d'insa na gidan ya zura ya dan bud'e abu ya gagara sai yahau buga mata tana kwance a kan gado da littafi a hannunta tana Home work d'in da aka basu, tanaji saidai batasan kowaye ba dan haka batayi ma niyar tashi zuwa ta gano ba.
Mtwwww yaja tsaki tare da ciro wayarsa ya nemo layin Haleema, mtwww ya kuma jan wani tsakin jin tana amfani da ita ya sake kiran khaleel cikin sa'a ya d'auka murya a shak'e Sadeeq tace.
"Dan turo min da number'n Aisha."
Khaleel yace "Yaya bani da ita sai dai ko yah Mubasheer."
"Cene masa ya turo min."
Ya fad'a a dak'ire sabida babu kowa unguwar sai shi kad
ai ga duhu. Yana tsaye yaji an turo ya kira number'n kamar bazata d'auka ba sai kuma tayi picking tare dayin shiru dan taji me maganar.
"Ke zoki bud'e min gida kinaji Ina bugawa kik'ak'i zuwa ki bud'e min."
Harzai katse yaji tace. "Waye kai d'in? Wa kuma kake nema..?!"
"Au bakima san waye ba dan rainin hankali Aisha?!"
Tace "Kai kaga k'ila wrong number ne go and check."
Kafin yayi magana ta katse kiran ta cigaba da aikin ta, Sadeeq yabi fuskar wayar da kallon mamaki ya sake buga gate d'in da karfi cikin jin haushi amma tak'i bud'ewa cikin 6acin rai ya buga number'n Mama tana bacci Haleema ta d'auka tana dubawa taga Sadeeq dan haka ta d'an janye wayarta daga kunne da takeyi da saurayinta ta kara tare da cewa.
"Yaya lafiya? Mama tayi bacci fa."
"Yauwa Haleema kira number'n Aisha kice ta bud'e min gidan Ina waje."
"Okey tom Yaya sai da safe."
Tana kashewa ta kira layin INdo, tana kwance duk tama rasa yadda zatayi Home work d'inta taga kira ta duba a tunaninta number'n d'azu ce tayi niyar d'agawa tayi mai rashin mutunci sai kuma taga Mmn dacta da haka akayi mata saving sunan tayi murmushi tare da karawa a kunne tana shirin gaida ita taji Haleema na cewa.
"Aunty Humairah Yaya fa yana k'ofar gida yace kije ki bud'e mai nidai sai da safe."
"Dama shine? No wonder naji ya fad'a da gadara zoki bud'e min gida, d'an rainin hankali ai na d'auka harka koma bazaka zo ba."
Hijabi tasa ta d'auki mukulli tayi waje, cire kwad'on (pad lock) d'in tayi ta bud'e mai ya shigo sannan ta juya ta koma, shi ya bud'e gate din yasa motar sannan ya rufe gidan ya shiga ciki. Bata falo ya bita bedroom fuskarsa a had'e yana shiga ya ganta kwance da littattafai a gabanta da biro da alama rubutu takeyi baki bud'e cikin tsananin mamaki yace...
*HAJJA CE*
[7/31, 5:13 PM] Aisha Galadima: *
MUSAYAR ZUCIYA...
*K.A.S Precious Hajja ce*
*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*
(Home of expert & perfect writer's)
*VOTE me on wattpad @Hajjac*
*DEDICTEED TO:* Sanah Isma'il Matazu
*Godiya mai yawa tare da d'inbin farin cikina zuwa ga fan's, na gode da addu'o'inku garemu munje Lafiya mun dawo lafi na gode sosai da sosai.
HAJARAH (MUM ILHAM) godiya mai tarin yawa a gareki domin kin nuna mana soyayya nida 'yar uwata STYLISH BCH da kuma 'yata IHSAN, Allah ya saka da alkairi ya bar kauna da soyayya Allah ya raya Ilham
UMMUL MEENAL, BILLY S FARI & OLO addu'atw gareku bazata fad'u ba sai dai ince Allah ya baku abinda kuke nema duniya da lahira domin kuna nuna min sayayya ta hak'ik'a HAJJA CE na sonku fiye da yadda kuke nunan kauna.
Page *28*
Tunda suka tafi koda wasa Sadeeq be ta6a gigin k'iran INdo a waya ba, bashi dama phone number d'inta bare yace zai nemeta. A 6angaranta itama bata ko tunaninsa tana gidanta hankalinta kwance babu abinda yake damunta. Ranar da su Sadeeq suka cika sati d'aya da tafiya a ranar INdo ta fara fita, kullum tana gidan mak'ota bata nan layin bata can sam bata zama cikin kwanaki takwas mutanan unguwar sun santa maza da mata yara da manya. Yayin da a 6angaran Sadeeq yana son ya kirata tunda yasan tana da hakki akan sa amma baya kaunar ya kirata tayi mai rashin kunya ko ta gaya mai maganar da zai kasa bacci dan ya lura akwaita da shuka magana ba kuma ta barinta indai harka gaya mai toh zata baka amsa hakan yasa ya shareta.
Misalin k'arfe hud'u ta fito daga wanka tana shafa mai tajiyo me tallah a k'ofar gida, cikin sauri ta janyo doguwar riga a cikin wardrobe ta zura tare da d'aukar mayafi ta fita. A k'ofar gate d'in ta tsaya dan sake tabbatarwa da kunnuwanta abinda me tallar yake cewa still taji yana cewa.
"A sai kajin gidan gona matasa..!"
INdo tayi saurin fita tare da kwala mai k'ira ya dawo baya kasan cewar harya wuce gidan nata. Tsayawa tayi suka fara ciniki zata siya har yace zai siyar mata a yadda cinikin ya tsaya, guda bakwai ta siya ta shiga gida ta d'akko mai kud'in ta bashi ya tafi ita kuma ta shiga da 'yan kajinta sai kuka sukeyi iya-iya-iya tana ta murna taje ta zuba su jikin bathroom d'in tsakar gida dama ba'a shigar sa.
A hankali ta ci gaba da kiwonsu tana bayarwa ana siyo mata abincin su hankalinta a kwance su Haleema idan suka zo suyi ta mata dariya ita kuma tace da tayi kud'i saudiya zata tafi idan ta dawo a dinga k'iranta Hajiya INdo kasan cewar sunan ya bazu cikin gidajen mak'ota k'annan su Sadeeq ne kawai ke kiranta da aunty Humairah kamar yadda marigayi ke fad'a mata.
Rayuwar INdo ta cigaba da canzawa sana'o'i take yi kala-kala kajinta ma sunata girma har ta samu sun fara kwai tana tarawa taci takai gidan su Sadeeq sai da Mama tace ta fara siyarwa sannan ta fara.
Da daddare tana kallon arewa 24 Sumayya tana gabatar da shirin tauraruwa taji yadda wata mata da ake hira da ita yadda rayuwarta ta faro tun daga tushe har yanzu da takai wannan matsayin nan da nan INdo tayi sha'awar yin karatu itama tana son ta iya turanci sai dai tayaya zata iya? Sam kwakwalwarta bata gane turanci ba kuma ta iya rubutawa sannan ba ta iya maida hankali wajan koya tayaya zata iya zama tauraruwa kamar yadda taga ana haskilo mata masu aji ana kuma alfahari dasu, tasa a ranta zata fara koyan turanci kamar yadda marigayi yaso tayi kafin mai rabawa ta rabasu.
Sannu a hankali tana jin takaicin Sadeeq nak'in nemanta tun ranar da Aminatu ta guntsa mata cewar ai dan batajin turanci ne yasa Yaya Sadeeq cewa baxai tafi da ita can ba hakan yasa abin ya kuma ba ta haushi tsanarsa ta kuma hauhawa a cikin zuciyarta dama ya saba yi musu wulak'anci tun a tsefawa.
M.M Haruna English academic taji anata tallar makarantar a gidan redion express, ta fara tunanin yadda zata yi ta samu shiga cikin ta.
Tanason zuwa tana tsoron kar da taje ta tarrar da garzazzu wad'anda basa Hausa sai turancin, wai shin ma meyasa aka maida turanci tamkar saukar alkur'ani da komai za'a ce in zaka yi sai ka iyasa? Ga larabci yaran annabi amma ba a dagewa da zuwa islamiyoyi ba'a basu muhimmanci kamar yadda ake baya yaran jajayan farar fatar nan. idan aka kyaro baka iya bama sai ka zama wani hulugu ka zama abin raini da wulak'anci a wajan al'umma.
Zata yi turanci itama za kuma taje ta koya badan wulak'ancin Sadeeq kad'ai ba sai dan wata rana itama ak'irata ayi hira da ita a kuma tambayeta tauraronta tace Abubakar ne,haka zakila kuma a Dama da ita ita duniya wannan burinta ne ba kuma zata canza shi ba koda Sadeeq zai saketa.
"Hello mubassheer, kana Ina yanzu.?!"
"Ina majalisa ya akayi ta samu ne..?!"
"Kai d'an rainin wayo ne, kazo dan Allah zamuyi sirri."
"Toh aunty Humaira gani nan zuwa amma fa zaki ban jarkar kunun aya guda biyu."
"Dallah idan baxaka zo ba sai na kira khaleefa wallahi."
"Sorry Matar broth ina zuwa."
Kashewa yayi yana dariya sannan ya d'auki abokinsa guda d'aya suka tafi gidan a mashin. A falo suka zauna ta kawo musu kunun ayar da zobo da jallop d'in taliya suka ci sukayi dam sannan mubashsheer ya kalli INdo yana cewa.
"Toh meye sirrin Matar broth, tunda kin bamu munci..!"
Sai da ta hararesa sannan tace mai.
"Dallah kaga ni ba surutu na tambaye ka ba, jujun labo store zaka dan Allah ka siyo min farm (form) d'in shiga makarantar M.M Haruna Englihi menene ma d'ayan na gaban ma oho na manta."
"Ah Matar broth wai kina nufin shiga zaki yi..?!"
INdo tace "Eh ya ranka? Zakaje kayi min duk abinda za'ayi na fara zuwa kokuwa wulak'anci zaka yi min Kai ma..?!"
"Ah Matar broth na isa, kawo kud'in toh sai muje muji ya za'ayi, amma tukunna kin sanar da broth Sadeeq d'in zaki fara ne dan karya zo yayi min masifa."
"Kai zaka siyo min ko kuwa na sake wani?!"
"Ah na isa kawo kud'in muje muji ya za'ayi."
"Toh nawa zan baka..?!"
"Haba ki kawo ten thousand muje mu fara manage dasu."
"Kana nufin nawa kenan?!"
"Kai Matar broth dubu goma zaki kawo naga kina min wani kallo."
"Ta6 goma fa kace? Wallahi ku tafi na fasa ai ba dole."
Ta fad'a tana shiga cikin d'aki Mubasheer ya dinga yi mata magiyar ta fara bada ten thousand d'in tace ta yafe bazata ba sai da yace.
"Toh kawo five thousand, dubu biyar wallahi Matar broth kin fiye san Kud'i da yawa, duk sati dubu biyar broth yake badawa a kawo miki ga kud'in zobo ga kunun aya ga gullisuwa da kwan kaji dan Allah mekikeyi da kud'i bayan duk akwai abinci a gidan..?!"
Dubu biyar d'in ta bashi ya kar6a ya k'irga sannan suka tashi zasu tafi INdo tace.
"Dan Allah k'anin miji a rage sa ido, duk lissafin ka yana kaina toh da ba kud'in zaka ci naman dakaci a cikin abinci ne? Ko zaka ci harda vegetables d'in ne d'an rainin wayo."
"Magana ta wuce bari muje mu dawo."
Yana fad'a suka fice ita kuma ta shiga d'aki. Ko Ina tas-tas a gidanta bata barin k'azanta sannan kullum cikin k'anshin turaran tsinke d'akin yake dan haka INdo tana samun customers a rana sai ta dura jarkokin zobo dana kunun aya guda d'ari biyu a
mma baya kaiwa dare Allah yasanya mata nasibi a ciki.
A ranar bataga Mubasheer ba har kwana biyu sai gashi yazo, tsayawa yayi yace ya gama mata komai zuwa kawai zata farayi domin sai da ya sanar da abban su ya kuma bada goyan baya sosai. Juma'a na zuwa ta fara zuwa cikin tsoro da fargabar yadda zata tun kari malamai da d'alibai dan tasan duk sun fita k'ok'ari.
"Matar broth ga class d'inku nan."
Mubasheer ya fad'a yana nunawa INdo ajinsu. Ido ta dinga kwalowa waje hannun ta na dama dafe da k'irji ta kalli Mubasheer cikin tsoro tace.
"Anya bazan koma gida ba, Mubasheer tsoro nakeji wallahi."
"Kai Matar broth wallahi karkiji tsoro kowa fa da kika gani zuwa yayi a koya mai, idan kika nuna musu kina jin tsoro zasu raina ki kedai karki fasa yin abinda kike so ki shiga kawai."
"Toh bari naje idan mun tashi zan yi maka waya kazo ka maidani gida."
"Toh Matar broth Allah ya bada sa'a."
A hankali INdo ta shiga tashin farko ganin yadda hall d'in yake yasa gabanta bugawa da k'arfi sannan ga d'alibai nan a zazzau ne duk sai ta daburce ta rasa inda zataje cikin sauri ta juya zata fita sai taga Mubasheer a tsaye yana dariya, cikin tsananin jin kunya tace.
"Maidani gida bazan shiga ba."
"Hahaha...! Wallahi babu inda zaki, muje na shigar dake haka kurum dan ayi asarar kud'i sai da aka gama komai zaki wani ce kin fasa."
Yana gaba tana bayansa har ya k'arasar da ita tsakiyar kujerun sannan yayi wa wata budurwa magana cewar gata nan dan Allah ta fara helping d'inta ta wasu abubuwan. Karimatu tayi murmushi tare da mik'awa INdo hannu suka gaisa ta zauna a d'ari-d'ari kamar munafuka sai wulkita idanuwa take a haka Mubasheer ya barta yayi tafiyarsa.
Malami na shiga ta fara sunkuyar da kai, nan aka fara gabatar da lesson kasan cewar ajin masu koyan turanci ne hakan yasa komai ake yi musu dalla-dalla cikin hikima da kuma kwarewar malaman ita dai INdo tayi tsit bata ko kwakwaran motsi dan karma malamin yayi mata tambaya koya saka mata ido. Alhamdulillahi kuma ta tsinto abubuwa kasan cewar sai anta maimaita musu abu anji kowa ya gane an kuma fahimta sannan za'a shiga wani abun haka aka dinga yi musu tana kuma zuwa duk juma'a asabar da lahadi da safe.
****
Wata d'aya da sati biyu su Sadeeq sukayi a kwara state sannan suka juyo suka dawo kano. Lokacin satin INdo biyu da fara zuwa makaranta, sam bata yi wani murna da dawowarsa ba sema haushi da takaici dataji. Sai da yayi kwana biyu a gidan Fateema sannan ya waiwayo yau zaije gidan da INdo take.
K'ofar gidan ta tsaya wajan k'arfe sha biyu na dare, key d'insa na gidan ya zura ya dan bud'e abu ya gagara sai yahau buga mata tana kwance a kan gado da littafi a hannunta tana Home work d'in da aka basu, tanaji saidai batasan kowaye ba dan haka batayi ma niyar tashi zuwa ta gano ba.
Mtwwww yaja tsaki tare da ciro wayarsa ya nemo layin Haleema, mtwww ya kuma jan wani tsakin jin tana amfani da ita ya sake kiran khaleel cikin sa'a ya d'auka murya a shak'e Sadeeq tace.
"Dan turo min da number'n Aisha."
Khaleel yace "Yaya bani da ita sai dai ko yah Mubasheer."
"Cene masa ya turo min."
Ya fad'a a dak'ire sabida babu kowa unguwar sai shi kad
ai ga duhu. Yana tsaye yaji an turo ya kira number'n kamar bazata d'auka ba sai kuma tayi picking tare dayin shiru dan taji me maganar.
"Ke zoki bud'e min gida kinaji Ina bugawa kik'ak'i zuwa ki bud'e min."
Harzai katse yaji tace. "Waye kai d'in? Wa kuma kake nema..?!"
"Au bakima san waye ba dan rainin hankali Aisha?!"
Tace "Kai kaga k'ila wrong number ne go and check."
Kafin yayi magana ta katse kiran ta cigaba da aikin ta, Sadeeq yabi fuskar wayar da kallon mamaki ya sake buga gate d'in da karfi cikin jin haushi amma tak'i bud'ewa cikin 6acin rai ya buga number'n Mama tana bacci Haleema ta d'auka tana dubawa taga Sadeeq dan haka ta d'an janye wayarta daga kunne da takeyi da saurayinta ta kara tare da cewa.
"Yaya lafiya? Mama tayi bacci fa."
"Yauwa Haleema kira number'n Aisha kice ta bud'e min gidan Ina waje."
"Okey tom Yaya sai da safe."
Tana kashewa ta kira layin INdo, tana kwance duk tama rasa yadda zatayi Home work d'inta taga kira ta duba a tunaninta number'n d'azu ce tayi niyar d'agawa tayi mai rashin mutunci sai kuma taga Mmn dacta da haka akayi mata saving sunan tayi murmushi tare da karawa a kunne tana shirin gaida ita taji Haleema na cewa.
"Aunty Humairah Yaya fa yana k'ofar gida yace kije ki bud'e mai nidai sai da safe."
"Dama shine? No wonder naji ya fad'a da gadara zoki bud'e min gida, d'an rainin hankali ai na d'auka harka koma bazaka zo ba."
Hijabi tasa ta d'auki mukulli tayi waje, cire kwad'on (pad lock) d'in tayi ta bud'e mai ya shigo sannan ta juya ta koma, shi ya bud'e gate din yasa motar sannan ya rufe gidan ya shiga ciki. Bata falo ya bita bedroom fuskarsa a had'e yana shiga ya ganta kwance da littattafai a gabanta da biro da alama rubutu takeyi baki bud'e cikin tsananin mamaki yace...
*HAJJA CE*
[7/31, 5:13 PM] Aisha Galadima: *
MUSAYAR ZUCIYA...