← Book details Musayar Zuciya Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 38 OF 53

Sashe 38

Musayar Zuciya Part 1 Complete Hausa Novel · about 9 min read

A true life story
*K.A.S Precious Hajja ce*
*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*
(Home of expert & perfect writer's)
*VOTE me on wattpad @Hajjac*
*DEDICTEED TO:* Sanah Isma'il Matazu.
*THANKS ALL FAN'
S, baki, hannu bazasu iya rubuta yawanku ba domin kunada yawa wlh. Na gode all grps da sukayi ma ihsan wishes. Allah yabar so da kauna.*
_My wattpad so sorry please wallahi nayi nayi yaki yin update kuyi hakuri wallahi tun safe yak'i yi nasara dalili
Page *31*
"Wallahi ni dai baza ni ba, haba-haba da bakin kafa kace wai ba zaka je dani ba sabida ni banajin turanci, toh wallahi yasin yanzu dakaji na faraji ba zan bika ba Allah kuwa."
"Idan nace kuma sai kinje fa ya zaki yi?!"
"Ai karka ma fad'a dan ba binka zanyi ba, kaje ku tafi da Fateema."
"Aisha...!"
Ya fad'a cikin gentle mood wanda yasa INdo saurin kallonsa cikin ido hudu, hannunta ya janyo yana kallon fuskarta a fili ya fara magana besan ma a filin yake yi ba.
"Aisha My heart is filled with instant joy, you give me everlasting warmth. Aisha your eye's, your nose, your pretty cheeks your mouth, your chin, the whole of you all are sweet and so you are. Please Aisha ki bini wallahi babu abinda zan miki kinji na rantse."
Kallonsa kawai INdo tayi sam duk ta kasa gane abinda yake cewa hasalima dabarbarta ta yayi kwakwalwarta ta fara hasashe kafin tace.
"Dare nayi malam Sadeeq kaje ka kwanta nima kwanciya zanyi na gaji."
"Toh zaki bini mu tafi d'in..?!"
"A'ah wallahi bance ba."
"Wai me yasa kike da taurin Kai ne Aisha.?!"
"Malam Sadeeq wane kai ne me laushi?!"
Mtwwww yaja tsaki tare da sakin mata hannu yaje ya d'auki mukulli ya tafi rufe gidan sannan ya dawo, yana dubawa ya tarar ta rufe d'akin ta ya san ko magana yayi ba bud'e mai zata yi ba kawai ya kwanta a falo. Washe gari yana yin sallah yabar gidan bayan ya ajiye mata 10k ya tafi gidan Fateema.
Yana zuwa ya tarar harta gama had'a mai kayansa ita kuma tana k'ok'arin shirin zuwa gurin aiki. Sai da ta temaka masa ya samu relief sannan suka shirya tare suka fito ta samu napep shi kuma ya Shiga mota yayi gidan su dan yi musu sallama. Suna gamawa ya juya ya d'auki hanya bayan yasawa ransa cewar zai gwada musu shi d'in namijin duniya ne sai sun nemesa musamman INdo da bata ganinsa da gashi aka.
**** ****
Bayan watannin uku.
12:30pm tana tsaye a mak'ale jikin bishiyar darbejiya sai makaka ruwan sama ake yi, ta jik'e tayi sharkaf da ita, ganin tamkar ruwa da iskar yana k'ok'arin jijjige bishiyar yasa ta ci gaba da tafiya sai faman tangad'i take tamkar ana tura ta, sam ba tayi tunanin ruwan zai yi yawan haka ba kafin ta k'arasa gida data fito daga school. Hakan ne ya bata damar tahau napep tayi gidan Asma'u tsautsayi kuma yasa ta fito tace ita gida zata tafi.
Horn d'in mota taji amma bata juya ba sabida ko ganin hanya bata yi sabida k'arfin ruwan. Kuma yi mata horn yayi da nufin idan tana son temako idan kuma yayi mata sau uku toh zai rabu da ita ya k'ara gaba k'ila ba bil'adam bace.
Tana jin ya kuma yi ta fara lalu6en inda taji mutar har Allah ya temake ta ta6ota, a hankali taje wajan k'ofar ta bud'e a she ta saitinsa ce sai ji tayi ya ce.
"Ke daga ina kike haka..? Ki zagaya ba ta nan zaki shigo min ba."
"I am not ke sir..., I am Aishat Hamza by name so please don't call me ke again..!"
Ta fad'a tare da d'an bud'e ido ta kalli motar, da sauri ta zagaya ta d'ayan gefen ta shiga ganin Sadeeq ne jikinta sharkaf ya kalleta baki bud'e ta zauna sai ya kauda kai tare da mik'a mata wani d'an kyalle ta kar6a tana goge fuska dashi kafin shi kuma yaja motarsa suka fara tafiya a hankali kasan cewar ruwa ake yi sosai tamkar da bakin kwarya.
"Ke wai daga ina kike haka cikin wannan ruwa?"
"Please sir I told you am not ke, kace min Aisha and daga school nake.."
"K'arya ne ya aka yi banga students ko d'aya ba sai ke kad'ai zaki tsaya yi min wani turancin banza."
"Hmmm oga Sadeeq you don't know justice is the best policy ko?!"
"Kut..!" Ya fad'a ba tare da ya san ya fito fili ba sabida tsananin mamakin ta da d'aurewar kai jin abinda take ce mai. Juyawa yayi yana kallonta tana goge fuska ya cije lips d'insa na k'asa har suka k'arasa bakin gate d'in gidan ta, tayi niyar fita taji motar a kulle sai ta kallesa tace.
"Malam Sadeeq we are here fa, please ka bud'e min zan fita thanks for the help."
"Karki fito ki zauna a ciki na gaya miki."
Yafad'a tare da zarar mukullinsa na gidan ya fita da kanshi. Kallo tabishi dashi sai tayi murmushi lokacin ta tuno da Abubakar sam baya d'aure mata fuska tun lokacin da ya d'akkota daga Saye, yakan yi mata duk abinda zai satayi dariya ko tayi farin ciki amman wannan gadai kaman nin sak amma zuciyar ta banbanta.
Dawowa yayi cikin motar shima duk ya jiki, shigar dasu yayi har parking lot da yake k'arami ne dai-dai mota d'aya INdo ta bud'e ta shige d'aki kasan cewar babu nisa befi taku hudu ba. Shima yana gama parking ya shiga falo bata nan ya wuce bedroom d'inta, tsaye ya ganta d'aure da zani ta juya baya wanda da alama da taji motsinsa ne tayi saurin yi.
A hankali ya taka yaje har kusa da ita ya tsaya, matsawa yaga tayi gaba shima ya matsa har takai k'arshe sannan yace.
"Go on.."
"Aisha you're beyond my control ko meye dalili ne?!"
"Because we don't love each other."
"You dai but me...."
Yayi shiru yana kallon keyarta don har lokacin bata juyo ba sabida wani dalili nata da bata son ya gani. Ji tayi ya rungumeta ta tayi saurin rintse idanuwa jin yadda tsigar jikinta ta tashi yarrr yana k'ok'arin d'ora hannun a saman cikinta tayi saurin rik'e mai hannu.
"Please don't touch me."
"Akan wane dalili? Shin Aisha an hanaki yin yaren Hausa ne?"
Tayi shiru tana kauce mai da sauri ya finciko ta suka fad'a kan gado har zanin da tayi d'aurin k'irji dashi yana zamewa tayi saurin tashi a firgice shi kuma yasa hannu ya dawo da ita duk da cewar kayan jikinsa a jik'e suke.
"Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un malam Sadeeq ka tak'aita ni k'il...!"
Da sauri ya mik'e zaune jin abinda ta fad'a, itama ra mik'e cikin kid'ima ta sauke zanin k'asa ya zamana bra ce kawai tayi saura daga cibinta zuwa sama, hannunta a saman cikinta daya d'an fito wanda ba kowa yake gani ba idan ba kwance pzani tayi ba ko kuma tasa t.sheet yaga tana shafar cikin bakinta a cune tana shirin yin kuka yace.
"Aisha what's going on.? Ciki gare..Ki..ne...!"
Bata lokacin da ta d'aga mai kai ba sabida Asma'u tace mata kar tayi abinda zai sa cikin ya samu matsala yau gashi Sadeeq zai nakasa mata shi. A zabure ya dawo k'asa idanuwa waje INdo na hawaye ta narkamai harara mai tattare da tsananin bak'in ciki ya kalleta k'irjin nan fam ya kuma yin kyau cikin in'ina yace.
"How come's daga yi d'aya...?!"
"Ka kaini asibiti nidai, idan ba bakayi ba yau ai gashi ka dauje ni."
Ya akai haka daga one day wanda yasha matuk'ar wahala ace mai tana da ciki ga Fateema da suka dad'e tare ko 6atan wata bata ta6a yiba amma INdo nada Ciki.., ya kuma kallonta sai hawaye take yi bayan ta gyara d'aurin zaninta gashi har lokacin ruwa ake tsugawa Sadeeq ya koma kan gadon tare da zama a bayanta a hankali ya rungume ta tare da rintsa idanuwansa yana jin wani feelings har cikin k'ahon zuciyarsa.
"Aisha Allah ne ya baki Abubukar a lokacin da zaku fara sabuwar rayuwa sai ya d'auke sa ba tare da kowa yasan manufar yin hakan ba, an had'a mu aure ba tare da muna so ba sai dai ko wannen mu ya d'auki hakan a matsayin kaddara. Aishi kiyi hakuri ki gafarce ni wallahi ko wanne tafiyar dani nayi tane cikin damuwa da tashin hankali amma ke babu abinda ya dameki why."
"Nidai ka kaini asibiti kawai dan Allah."
"A cikin ruwan nan? Dama gashi kinje kin kaimin shi ruwa ya jibgeshi k'ilama kinja mata/masa mura."
Sake rik'ota yayi sosai a jikinsa yana yawo da hands d'insa tayi d'if, ganin haka yasa Sadeeq matsawa ya kwantar da ita kan gadon ya kura mata kyawawan idanunsa yana shafar cikin ta a hankali saitin kunnanta yace.
"How many months."
INdo ta kawar da kai tace "Ai bakaso ka dawo ka tarar dani a raye ba malam Sadeeq, sabida tunda ka tafi ko please call me baka ta6a gigin yi min ba. A gabana kasha yiwa Fateema waya sabida ita *Son ranka ce* ni kuma *Za6in iyayanka* hakan yasa baka san komai daya danganceni ba. Duk surutuna wallahi danaga kana yin haka ka watsar dani yasa nak'i nunawa kowa ina da ciki sai Asma'u da Mama sune kawai suka sani, sai gashi Allah ya raya ni da abinda yake cikina cikin k'oshin lafiya. Baya sani wani laulayi yadda neke komai a baya haka nake yi har yanzu.
Malam Sadeeq baka sona sabida kasan cewa ta 'yar kauye, matalauciya, marar Ilimi. Karka manta Allah dayayo ka cikin wadata bawai yafi sonka bane, Allah dayayo ka hazik'i fasihi mai d'in bin basira bawai dan yafi sonka bane ko kuma dabarar ka da iyawarka ba kawai hakan ma jarabawa ce sai gashi kana min gori akan hakan. Shin ka manta twinnie broth d'inka duk ya fika wannan felek'an amma da Allah ya tashi sai ya bashini, ya zamto a duniya ni yake so har ya koma ga mahaliccinsa. Shine mutum na farko daya fara tsamoni daga k'angin wahala da toshewar kwakwalwa Allah ya gafarta mai haka kuma har cikin zuciya ta yana nan I will never forget him..never..never...."
"Kiyi hakuri Aisha."
Yayi maganar jikinsa a sanyaye, INdo ta share hawayen fuskarta tana cizon lips, ruwan da akeyi ne ya haddasa wani sanyi me ratsa cikin tsokar mutum hakan yasa INdo takure guri d'aya, Sadeeq na ganin haka ya xura kansa cikin wuyanta idanunta a lumshe yace.
"Aishi kinyi hakuri kin yafe min? Namiki alk'awarin maye miki wanda yafi Twinnie d'ina, bazaka sake yin kuka dani ba har nima lokacin da tawa zata kasance. Ina son ki bani dama na shiga cikin rayuwarki nima na d'an yi miki koda rabin abinda Marigayi yayi miki ne, ina rok'onki alfarma ko yaya ne ki bari muyi rayuwa tare."
*HAJJA CE*
[7/31, 5:13 PM] Aisha Galadima: *
MUSAYAR ZUCIYA...
Chapter 38 · 0% Book details