← Book details Kun Makaro Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 9 OF 41

Sashe 9

Kun Makaro Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Miqewa yayi, cikin fushi, ya ja hannun ta da qarfi ya matse, dole ta sa ta miqewa tsaye dan azaba, wani irin kallo yake mata na tsantsar tsana da jin zafin rashin kunyar da ta masa, lallai yarinyar nan daga ta gan shi ba kaya shiyasa take qoqarin fara kawo masa raini?

Gyaran murya suka ji daga bayan su, cikin mamakin ta kuwa Sabeer ta gani, da qarfi ta fizge hannun ta ta gudu bayan shi tana kuka, kallon kallo sukai da Khaleefa,kafin Khaleefa yayi qwafa ya fice.

Juyawa Sabeer yayi, ya na son bata hakuri, amma qamshin ta, da kyaun ta suna fizgar shi, idon ta rufe, a hankali ya taka ya bar wajen.

Bude ido tayi tare da share hawayen ta, ta bude baki zatai magana kenan taga ba kowa a wajen,

"Ina Yah sabeer? Ko dai gizo yake man? Me ye zai sa yamin gizo to? Yah Sabeerrr.............

*ku taya ta nemo Sabeer pls, tana cikamin kunne*
💅🏼 *KUN MAKARO* 💅🏼

*BY HAERMEEBRAERH*

Page 8:

Duba shi ta shiga yi, idan ta hawaye, yau so take ya fada mata me ta mishi yake gudun ta, koba komai shi kadai ta sani ta saba da shi, shi take jin zata iya sharing komai da shi vataji nauyi ko kunya ba, bata sani ba wataqila laifi ta masa shiyasa yake gudun ta.

Qofar dakin shi taje, tai ta kwankwasawa, yana tsaye jikin qofar, a hankali ya saka key, shiru ta danyi, dan taji motsin saka key din, a zaton shi ta hakura ta tafi, da sauri ya murda ya bude, zai leqa ta, sukai gware, baya yayi, yana taba wajen, itan ma haka, wayancewa yayi da,

"Me qaton kai kawai, ji yanda kk sa na bige,"

"Yah ni da kai an ga mai qaton kai ai, Yah Sabeer me nama ne, in wani laifi na maka dan Allah ka yi hakuri ka yafe min na tuba ba zan sake ba, ba zan sake makamancin shi ba ma ko mene ne balle nayi irin shi, ka daina guduna, ka sauya wajen aiki, for only god knw why, amma zaka tafi ko sallama,ina ta bin ka ina kiran sunan ka haka ka fice baka tsaya ba,nice baka son gani ko?"

Tana maganar ne cike da zubar hawaye, kukan ta na qona masa zuciya, baya son ganin koda bacin ran ta ne balle kukan ta, yana son ya bata amsa amma me zai ce mata? Ina son ki? So nake ni na aure ki ba Khaleefa ba? Inaaa ba zai taba yuwa ba.

"Look dear, ni ba wai gudun ki nake ba, yanayin aiki ne haka, kuma ranar na san inna tsaya sai na makara ban tafi ba, in ban manta shagwabar ki ba kina qarama ko nan da can naje sai kinyi ta kuka, kina rikici, ko dake ban sani ba yanzu kin zama babba wataqila kin daina ko?"

Cikn wasa ya qarasa maganar tashi, itan ma murmushi tayi,

"Yah zauna na baka labarin abubuwan da suka faru da baka nan, kuma ina son ka ban shawara, akan Yah Khaleefa, akwai wani sirri nashi da ba na son fada, amma bana son abun, bana son mai yin abun, dan haka nake jin tsanar wannan auren namu, Yah dan Allah ka ban shawara ya zanyi?"

Gaba daya ya shagaltu da kallon ta, a dan watannin da yayi sai yaga ta qara kyau da girma, ga shi for the first time ya gan ta da kwalliya mai kyau haka, hannu tasa ta gaban idon shi,

"Yah magana nake fa,"

A dan firgice ya dauke kan shi, ya kalle ta again,

"Immm kin ga ko zamu bari nayi wanka na ci abinci, bana gane komai yanzu, muguwar yunwa nake ji, kin san ni da ci,"

🙄🙄"amma dai matar ka ta shiga uku, ko daga qafar girki na rana daya ba za ta samu ba,"

Tashi tayi ta na tafiya tana sanar da shi anjima zata dawo, su qarasa magana, ya amsa da to, ta koma wajen su Hajja, nan ta samu Hussai ta dakko kudin da Khaleefa ya wurga mata, suna ta mata dariya, wai amaryar qauye an mata kyauta ta ajiye, ango ya tafi tabiyo sahu ta dauka taga babu, tana son tai kuka, yaqe ta musu ta shuge daki.

Yanda auren nan ke qaratowa haka zuciyar ta ke tsananta bugawa, Sabeer ya tare a gidan Umma, dan bai ma sake komawa ba balle ta gan shi tace zasuyi magana, ba zai juri kallon ta ba, bai san me zai iya aikatawa ba da wanda ba zai iya aikatawa ba indai a gaban ta ne.

*********************

"My baby ina kk son tafiya ne wai? Gobe fa daurin auren ka, na sani in ka tafi ba zaka sake dawowa ba,ka bari na kwashi rabona mana plssssss"

Wani irin narkewa take a jikin shi, shi kuma yana lumshe ido,kamar wadda aka mintsina ta tashi, tambayar ta yayi

"Lfy?"

"Lfy qlou ina zuwa, zan dan qaro abin sha ne, naga wannan ya kusan qarewa kuma ina jin yunwa,"

Dan gidan ta madaidaici , amma fa mai shegen kyau, dan gaskiya da alama a qasar waje aka gano tsarin itama aka mata, ko kuma wasu masu basirar ne suka tsara gidan, iya haduwa da kyau ya hadu, wani Minister ya mata kyautar shi, amma yanzu basu tare.

Kukun ta ta yi ma umarnin ya hada masu abinci, ta lissafa masa abinda take son ya kawo masu, sanan ta bashi wata kwaya ya saka masu dika a abin sha, cikin murmushi da takun qasaita ta koma dakin, in da sabo kukun ya saba ba yau yake mata aiki ba.

"Hey babe, sorry na barka kai daya,"

"Ba komai, kamar wani baqo, come here,"

Takawa tai kamar mai tausayin qasa ta kwanta gefen shi, wasannin su suke, suna ta dariya, waya ta shiga masa, yana dubawa yaga Baba General ke kiran shi, dan guntun tsaki suka ja a tare, bai ji dadin yanda tai tsaki ba, dan ba hurumin ta bane, in shi yayi bai sa ta taya shi ba, wani mugun kallo ya mata for the first time.

"Meye naki na tsaki, ko zan iya sanin dalili?"

Kame2 ta fara,dan ganin wani irin kwarjini daya mata, nan take tsoron shi ya kama ta, inda inda ta fara, cikin tsawa ta fara mata magana,

"Kina jina ko, hurumin iyalina ba naki bane, ba ruwan ki da ya nake tare da su,in ina tare dake ina tare dake, in naga dama na je wajen su na tafi, kakana ne fa, kk masa tsaki, ko wayar ki ya kira?"

"Babe plsss kar ka min wannan fassarar,ni fa nayi tsaki ne kawai duba da yanda ranka ya baci, bana son abinda zai bata maka rai ne kawai,"

"Ba hurumin ki bane, ki san matsayin ki, this is my grandpa, ba abokin wasan ki bane, ki riqe wannan,"

"Yes babe, and i am so sorry, i will make it up to u, plss don't be angry, smile for me, plsss,"

Yau fa taga kalar Khaleefa da bata san yana da ita bama, ko alamar ya sakko bai nuna mata ba, kayan shi ya fara zurawa,cikin damuwa ta taso zata hana shi ya mata wani kallo ta koma ta zauna, me wannan yake nifi ne, zata sa a hada wannan uban abincin a banza ne? Kuma yau wai har ita namiji kema wannan kallon da rashin mutuncin bata ci....... tab di jam akwai aiki gaban ta kenan, Khaleefa bai jiqu da qaunar ta ba,( lallai vata san waye Khaleefa bane, tama samu yana yi da ita ne)

Akan idon ta ya gama shiri ya fice ba ko magana.

Ranta in yayi dubu ya baci kuwa, cikin bacin rai,ta yi ma wani saurayin ta waya, na ta gayyace shi su dora abinda basuyi da Khaleefa ba, sigari kuwa ta sha ya kusa biyar, daga qarshe Shisha ta dakko ta fara zuqa( mata da maza ku kiyayi shishar nan, illa take ma bayyani ba a boye ba, wanda ke son rayuwar shi da lfy a ciki; bai wahala ba bai wahalar da dangi ba ya guje ta)

A zaune suke a kan kujeru suna ta hira, suna dariya, ga 'yan uwan su harda na Yola sun zo, gobe daurin aure, sai bayan an daura ne za a yi gagarumar dinner, wadda Baba Genera y gayyaci manya2n qasar nan, za ayi dinner din ne mata da maza, kowa zai zo da iyalan shi dika, domin taya Baba General murna.

Aeeshaa na gefe in an abun dariya ta murmusa, abinda ke damun ta ba kadan bane, ga rashin Umman ta, ga miji dan iska, yanzu ace Umman ta ta jata ajiki ai da ta sanar mata, da kunya ta ce ma Hajja jikan ta babba dan iska ne, ta ina ma zata fara mara vayani?

Wuce su yazo yi Balqis ta gaida shi, yi yayi kamar bai ji ba ya shige, bushewa da dariya sukai, babbar diyar Uncle din Aeeshaa da tazo itama Fateema ce ta dakatar dasu,

"Kuka sani ko ango ance ya kawo kudin dinner ne account yayi qasa? Kun san fa maza da biki ya qarato da sun fara fada da kowa kenan 😆"

Nan da nan kowa ya sa dariya har Bilqis data bata rai, kowa ya ci gaba da fadin albarkacin bakin shi.

"Gani,"

Kallo Baba General ya bishi da shi, cikin takaici, sannan ya nisa yace,

"Anya mun yi wa Aeeshaa adalci in muka aura mata kai? Anya ba zamuyi dana sanin wanan auren ba? Daga ina kk? Jiya ina sane da baka kwana gidannan ba,na kira ka baka ga damar amsa wa ba, ba tarbiyya ka shigo min ba sallama, sannan kace min gaka, wazaka nunawa baqar zuciya? Nine fa na haifi uban ka, ka ko san ko baban ka a wajena ya gaji zuciya bare kai dorin dosano,"

"Shifa wannan fadace2n da gore2n ne baya so, ai bashi yace a haife shi a nan din ba"
Chapter 9 · 0% Book details