Sashe 8
Kun Makaro Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Tana karairaya tana shafo shi take maganar, can qasan zuciyar ta kuwa wani irin azababben kishi ne taji ya kama ta, a rana daya da tai da shi ta banbance shi da dikkan mazan da tai mu'amala da su, ta bashi lambar yabo mai girma, dan haka dik yanda zatai ta ajema kan ta shi sai tayi,ba aure ba Allah yasa shine tantabara, sai ya raba mata kwana da matar shi, in ma bata dau kaso mai tsoka ba kenan.
"Look young gurl,thanks for the company, i really enjoyed yesterday, infact, it was the best nyt ever, but u c the problem is that, i can't......"
Hana shi qarasa mai zai ce tayi, ta hanyar sakar masa da kasala, da salon ta.
Khaleefa mabuqaci ne sosai,dan haka ba abinda yafi masa a yanzu irin ya biye mata kawai.
Sai da suka nutsu sosai sannan take fada masa,
"Kaga ni ba zan hana ka aure ba, wa ce ce ni? Wane matsayi na ke da shi a wajen ka? Daga biya ma kai buqata? Ni ba sai ka biyani ba,nima na gani ina so, so kawai in kaje kaga amarya bata maka ba zaka iya dawowa nan, ko da yaushe qofa bude take a wajen ka, haka zalika koda ta maka in kaji kwadayin zuwa ka sha madara zaka iya zuwa nan, baka da case,"
Bai musa mata ba, kuma bai amsa mata ba, wanka ya shiga,biyu har ta gota, alwala ya yo, ya fara sallolin da bai ba, yana idarwa tana kwance daidai tana kallon shi, ya kula in bai da gaske ba ba zata barshi zuwa ko ina ba,
"Ai ka bari kaci abinci ko?"
"No thanks zani gida,qanne na na san sun zo, nemana da zasuyi tayi ne zai tabbatar ma da mutan gidan mu ba gida na kwana. Ba, so sai wataran,"
Har bakin qofa ta raka shi, tana zuba masa salon karuwancin ta.
*******************
"Gaskiya amarya ki fito mana da angon nan naki haka, mun gaji da jira, tin dazu ko wayar shi ma ta daina shiga,"
Cikin jin kunya Aeeshaa ta sauke kai qasa,
"Adda Hussai ni ina ni ina boye babban mutum kamar Yah khakeefa, na san aiki ne dai ya boye shi,"
Hassana dake gefe tai murmushi, dan yanzu ta sauke komai a ran ta, tin bayan zuwan 'Yan uwan nata da suka bata shawarwari, da kuma nuna mata rashin dacewar su ma kwata2 da Khaleefa, suka bata shawarar ta yi hakuri, ta tsananta addu'a inshaa Allah mijin ta na nunawa sa'a na nan tafe, sun yi ta bata misalai kala2 kafin zuciyar ta ta aminga da bayann su.
Qarar motar shi ce ta sa Balqis miqewa da kyar tana tura tsohon cikn ta,
"Sai na riga ku, dan na gane qarar motar shi har na gaji,"
"Taka da sauri Iya beji, Allah ya sa kije ya gwasale ki, kin san halin shi ai, ba a iya masa ya dangin gidan maza,"
"Habaa kar ki masa mummunan zato, muna kyautata wa 'yan uwan mu zato, yanzu mu dade bamu ga juna ba haka ya gwasale ni?
Miqewa tayi da kyar da qaton cikin ta a gaba, ta nufi waje, rufe mota yayi dauke da tarkacen shi a hannu, ya nufi cikin gida, cikin zumudi ta tarbe shi,
"Yah Khaleefa barka da dawowa, mun dade muna ta jiran ka, sai yanzu ka dawo, nayi missing din ka sosai,"
"Ah Balqis ya kk? Ya mai gidan? Sannun ku da zuwa, bari na dan huta a gajiye nake,"
"Muna lfy Yah, ban so hakan ba, na so mu zauna mu yi hirar yaushe gamo,"
Murmushi ya mata sannan ya yi gaba, ba tare da yace komai ba.
Dariyar su Hussai taji a bayan ta, aiko nan da nan ta hau,su kuma cike da tsokana suka maimaita me Khaleefa ya fada,
"Ah Balqis, ya kk? Ya mai gidan, bari na dan huta a gajiye nake,"
A tare suka kwashe da dariya, banda Aeeshaa da take murmushi, da kuma Balqis da ta cika tayi famm.
Bata kula su ba ta wuce bangaren Hajja, kayan lefe ne a qasa Hajja na dagawa tana ajewa,tana ganin su kuwa ta manta da haushin su Hassana, cikin fara'a ta qarasa ta zauna daf da Hajja.
"Hajja ba ko gayya,abun 'yar haka ne ma?"
"Na so kiran ku sai na manta na bar wayata daki, shine nake ta roqon Allah ya kawon wani a cikin ku, sai a kira mutan gidan suga lefe, abinda babu sai a fada a saka,"
"Hajja hoo, wannan kaya haka meye babu, ai komai sai son barka, ni fa tinda aka fara maganar bikin nan banji kuna maganar Aunty khadeeja ba, ko ita ba ita a harkar ne?"
"Bar wannan baqauyiyar,ko wa ya fada mata ana kunyar dan fari oho, ni da nake da namiji ma, hirar mu muke sha, da auren baban ku ni na tsaya nayi komai, amma ita wai kunyar diyar fari take, diyar fari ai abokiyar hirace,abokiyar shawara; abokiyar farin ciki da koka baqin ciki,ita ta sani, ba abinda ba zan ma Aeeshaa ba tinda takwara ta ce,"
"Wannan gaskiya ne,mun shaida,dan baki hada ta da kowa ba,"
Inji cewar Hussai da ta shigo, tare da Aeeshaa da Hassana,Aeeshaa na ganin kayan tasan na lefe ne dan haka ta gudu daki, dariya sukai ta mata, dan itama akwai kunya.
"Amma Hajja banga turaren da nake matuqar so ba, wanda kk sai min zuwan ki Hajji na qarshe, har yanzu ko saudiya naji za aje sai na bada sautun shi,"
"Ohhh haka ne abun, ni ai ba turare aka ban ba, tashi ka fiya naci aka ba wa Mine, sai jallabiyya da aka ban, meye sunan turaren?"
"Ni da ke daya ne? Ni ce qarama dole aban tsaraba tafi taki, sunan shi Sirrati, Arebian ne, ya hadu matuqa, suna shigen qamshi da lailatussahrah,"
"Ai kuwa sai an nemo shi, ko sautu sai a bayar,"
"Ohh yaran zamani, wato kun yaba turaren, nima ba a barni a baya ba, sai an siyo dani,"
Dariya sukai, a haka suka ci gaba da kawo abubuwan gayu da qamshi wanda ba a saka ba, sun kira 'yab uwan su dan ganin lefe, anyi2 Umma tazo taqi, ta turo Ameena da Abdul.
Baban su sabeer har Katsina ya je ya kai masu katin daurin auren Aeeshaa da Khaleefa, sunyi kurna sosai, na nuna masu mahimmancin su, sun kuma yi alqawarin ziyartar bikin.
*********************
Sauran kwana uku biki, har yau ango da amarya basu zauna waje daya sun tattauna ba da sunan zasu zauna a inuwa daya nan da wasu kwanaki, kullum sai dai su hadu a kan hanya, General ya ma Khaleefa umarni yau ya je bangaren Ummeen su Sabeer ya gana da Amaryar shi, kar kuma yaji ance bai je ba.
A yau din ne mutan Kt suka iso, mata uku, namiji daya, wanda yake shine Yayan mahaifin Aeeshaa, ta yi kuka sosai da kuma murnar ganin shi, yana matuqar kama da mahaifin ta, matan shi masu kirki, kamar su goya ta dan murnar ganin ta,sun kawo mata tsaraba kala2, wanda yake namu na mata sai suka damqa shi hannun Umman Sabeer, yamma nayi Uncle din ta ya dau matan shi suka koma gidan su Aeeshaan, can zasu sauka, dik da cewar Hajja taso su zauna anan, a cewar ta, in Umman taga an barta ita daya ta zo harkar bikin dan dole ai.
**********************
Khaleefa ke ta tinanin ya zai yaje bangaren ummeen su Sabeer zance da wannan yarinyar da baifi ya aike ta kira masa budurwa ba, ga shi Rebecca sai waya take masa, dan yau kwata2 bai fita ba, 'yan kwanakin nan ko laptop bai cika dauka ba, dan ya samu mace ba sadakin kowa, ya more ya kama gaban shi.
Turaren shi ya qarasa fesawa, dan so yake daya gan ta ya wuce wajen beccan shi.
Hussaina ce ke tsarawa Aeeshaa kwalliya, kamar yau za a kaita dakin ta, dik dan Khaleefa ya gani ya yaba, ta tsaya sosai ba dan komai ba sai dan Balqis da ke zaune tana miqo kayayyakin, yanda ta ke zumudi kai kace wani auren soyayya ake shiryawa.
Simple make up suka mata, amma fuskar ta sai sheqi take dan kyau,hijabi ta dakko zata saka, har suna hada baki wajen fadin,
"Habaaa yarinya ai ko a riga aka haife ki ba zaki saka hijab dinnan ba,"
Dariya sukai dika, sannan Balqis ta yafa mata mayafi kalar kayan ta
"Adda a haka zanje?"
"Wataran ma ba kaya zak yawo a gaban shi,"
Duka Hassana ta kai ma Hussai.
"Babbar banza kawai,"
Cikin jin kunya ta sinqe hijabin ta a jikin ta, tana zuba gaban Parlourn ta warware ta saka, a ranta tace,
'Ina na isa yawo a gaban wannan mayunwacin matan da wannan shigar, inaaa Ya Allah ka taimakeni, ni tsoro ma yake ban'
"In bazaki shigo ba ki fadan ina da abin yi,"
Da sauri ta shiga ta samu waje ta zauna nesa da shi, a takure, cike da jin tsoron shi.
'Ji wannan ko meye haka taje yi? An fada mata kowacce mace nake bi oho?'
(Yo ba gwanda ita ba ma, kai da ke shiga ramin shaddar kasuwa dan rainin wayo kawai😏)
Shiru sukai,ba mai cewa komai, a qashin gaskiya turaren ta ya masa dadi, ba kadan ba kuwa amma dan baqin hali ya hana ya yaba ko da kwalliyar ta ta ne ma.
Karkacewa yayi ya zaro kudi masu yawa, da gani zasu kai dubu dari ko sama, wurgawa yayi a gaban ta.
"Ga shi nan na san wataqila ace na bada, dan ku mata akwai ku da bidi'a baku tinanin ya aka samo kudi amma kuna son kashe su,"
Wani kallo ta masa, sannan ta tura kudin har gaban shi da hannun ta.
"Kar ka damu Yah, ai ba kai ka nemi aure na ba dama, kar ka manta matar sadaka ce ni, baka ni akai kyauta,ba mai buqatar kudin ka,"
Cike da mamaki, ya kalle ta, itan ma shi take kallo, tana jin tsoron shi yes, amma ba ta daukan wulaqanci musamman akan abinda bata roqa ba.
"Look young gurl,thanks for the company, i really enjoyed yesterday, infact, it was the best nyt ever, but u c the problem is that, i can't......"
Hana shi qarasa mai zai ce tayi, ta hanyar sakar masa da kasala, da salon ta.
Khaleefa mabuqaci ne sosai,dan haka ba abinda yafi masa a yanzu irin ya biye mata kawai.
Sai da suka nutsu sosai sannan take fada masa,
"Kaga ni ba zan hana ka aure ba, wa ce ce ni? Wane matsayi na ke da shi a wajen ka? Daga biya ma kai buqata? Ni ba sai ka biyani ba,nima na gani ina so, so kawai in kaje kaga amarya bata maka ba zaka iya dawowa nan, ko da yaushe qofa bude take a wajen ka, haka zalika koda ta maka in kaji kwadayin zuwa ka sha madara zaka iya zuwa nan, baka da case,"
Bai musa mata ba, kuma bai amsa mata ba, wanka ya shiga,biyu har ta gota, alwala ya yo, ya fara sallolin da bai ba, yana idarwa tana kwance daidai tana kallon shi, ya kula in bai da gaske ba ba zata barshi zuwa ko ina ba,
"Ai ka bari kaci abinci ko?"
"No thanks zani gida,qanne na na san sun zo, nemana da zasuyi tayi ne zai tabbatar ma da mutan gidan mu ba gida na kwana. Ba, so sai wataran,"
Har bakin qofa ta raka shi, tana zuba masa salon karuwancin ta.
*******************
"Gaskiya amarya ki fito mana da angon nan naki haka, mun gaji da jira, tin dazu ko wayar shi ma ta daina shiga,"
Cikin jin kunya Aeeshaa ta sauke kai qasa,
"Adda Hussai ni ina ni ina boye babban mutum kamar Yah khakeefa, na san aiki ne dai ya boye shi,"
Hassana dake gefe tai murmushi, dan yanzu ta sauke komai a ran ta, tin bayan zuwan 'Yan uwan nata da suka bata shawarwari, da kuma nuna mata rashin dacewar su ma kwata2 da Khaleefa, suka bata shawarar ta yi hakuri, ta tsananta addu'a inshaa Allah mijin ta na nunawa sa'a na nan tafe, sun yi ta bata misalai kala2 kafin zuciyar ta ta aminga da bayann su.
Qarar motar shi ce ta sa Balqis miqewa da kyar tana tura tsohon cikn ta,
"Sai na riga ku, dan na gane qarar motar shi har na gaji,"
"Taka da sauri Iya beji, Allah ya sa kije ya gwasale ki, kin san halin shi ai, ba a iya masa ya dangin gidan maza,"
"Habaa kar ki masa mummunan zato, muna kyautata wa 'yan uwan mu zato, yanzu mu dade bamu ga juna ba haka ya gwasale ni?
Miqewa tayi da kyar da qaton cikin ta a gaba, ta nufi waje, rufe mota yayi dauke da tarkacen shi a hannu, ya nufi cikin gida, cikin zumudi ta tarbe shi,
"Yah Khaleefa barka da dawowa, mun dade muna ta jiran ka, sai yanzu ka dawo, nayi missing din ka sosai,"
"Ah Balqis ya kk? Ya mai gidan? Sannun ku da zuwa, bari na dan huta a gajiye nake,"
"Muna lfy Yah, ban so hakan ba, na so mu zauna mu yi hirar yaushe gamo,"
Murmushi ya mata sannan ya yi gaba, ba tare da yace komai ba.
Dariyar su Hussai taji a bayan ta, aiko nan da nan ta hau,su kuma cike da tsokana suka maimaita me Khaleefa ya fada,
"Ah Balqis, ya kk? Ya mai gidan, bari na dan huta a gajiye nake,"
A tare suka kwashe da dariya, banda Aeeshaa da take murmushi, da kuma Balqis da ta cika tayi famm.
Bata kula su ba ta wuce bangaren Hajja, kayan lefe ne a qasa Hajja na dagawa tana ajewa,tana ganin su kuwa ta manta da haushin su Hassana, cikin fara'a ta qarasa ta zauna daf da Hajja.
"Hajja ba ko gayya,abun 'yar haka ne ma?"
"Na so kiran ku sai na manta na bar wayata daki, shine nake ta roqon Allah ya kawon wani a cikin ku, sai a kira mutan gidan suga lefe, abinda babu sai a fada a saka,"
"Hajja hoo, wannan kaya haka meye babu, ai komai sai son barka, ni fa tinda aka fara maganar bikin nan banji kuna maganar Aunty khadeeja ba, ko ita ba ita a harkar ne?"
"Bar wannan baqauyiyar,ko wa ya fada mata ana kunyar dan fari oho, ni da nake da namiji ma, hirar mu muke sha, da auren baban ku ni na tsaya nayi komai, amma ita wai kunyar diyar fari take, diyar fari ai abokiyar hirace,abokiyar shawara; abokiyar farin ciki da koka baqin ciki,ita ta sani, ba abinda ba zan ma Aeeshaa ba tinda takwara ta ce,"
"Wannan gaskiya ne,mun shaida,dan baki hada ta da kowa ba,"
Inji cewar Hussai da ta shigo, tare da Aeeshaa da Hassana,Aeeshaa na ganin kayan tasan na lefe ne dan haka ta gudu daki, dariya sukai ta mata, dan itama akwai kunya.
"Amma Hajja banga turaren da nake matuqar so ba, wanda kk sai min zuwan ki Hajji na qarshe, har yanzu ko saudiya naji za aje sai na bada sautun shi,"
"Ohhh haka ne abun, ni ai ba turare aka ban ba, tashi ka fiya naci aka ba wa Mine, sai jallabiyya da aka ban, meye sunan turaren?"
"Ni da ke daya ne? Ni ce qarama dole aban tsaraba tafi taki, sunan shi Sirrati, Arebian ne, ya hadu matuqa, suna shigen qamshi da lailatussahrah,"
"Ai kuwa sai an nemo shi, ko sautu sai a bayar,"
"Ohh yaran zamani, wato kun yaba turaren, nima ba a barni a baya ba, sai an siyo dani,"
Dariya sukai, a haka suka ci gaba da kawo abubuwan gayu da qamshi wanda ba a saka ba, sun kira 'yab uwan su dan ganin lefe, anyi2 Umma tazo taqi, ta turo Ameena da Abdul.
Baban su sabeer har Katsina ya je ya kai masu katin daurin auren Aeeshaa da Khaleefa, sunyi kurna sosai, na nuna masu mahimmancin su, sun kuma yi alqawarin ziyartar bikin.
*********************
Sauran kwana uku biki, har yau ango da amarya basu zauna waje daya sun tattauna ba da sunan zasu zauna a inuwa daya nan da wasu kwanaki, kullum sai dai su hadu a kan hanya, General ya ma Khaleefa umarni yau ya je bangaren Ummeen su Sabeer ya gana da Amaryar shi, kar kuma yaji ance bai je ba.
A yau din ne mutan Kt suka iso, mata uku, namiji daya, wanda yake shine Yayan mahaifin Aeeshaa, ta yi kuka sosai da kuma murnar ganin shi, yana matuqar kama da mahaifin ta, matan shi masu kirki, kamar su goya ta dan murnar ganin ta,sun kawo mata tsaraba kala2, wanda yake namu na mata sai suka damqa shi hannun Umman Sabeer, yamma nayi Uncle din ta ya dau matan shi suka koma gidan su Aeeshaan, can zasu sauka, dik da cewar Hajja taso su zauna anan, a cewar ta, in Umman taga an barta ita daya ta zo harkar bikin dan dole ai.
**********************
Khaleefa ke ta tinanin ya zai yaje bangaren ummeen su Sabeer zance da wannan yarinyar da baifi ya aike ta kira masa budurwa ba, ga shi Rebecca sai waya take masa, dan yau kwata2 bai fita ba, 'yan kwanakin nan ko laptop bai cika dauka ba, dan ya samu mace ba sadakin kowa, ya more ya kama gaban shi.
Turaren shi ya qarasa fesawa, dan so yake daya gan ta ya wuce wajen beccan shi.
Hussaina ce ke tsarawa Aeeshaa kwalliya, kamar yau za a kaita dakin ta, dik dan Khaleefa ya gani ya yaba, ta tsaya sosai ba dan komai ba sai dan Balqis da ke zaune tana miqo kayayyakin, yanda ta ke zumudi kai kace wani auren soyayya ake shiryawa.
Simple make up suka mata, amma fuskar ta sai sheqi take dan kyau,hijabi ta dakko zata saka, har suna hada baki wajen fadin,
"Habaaa yarinya ai ko a riga aka haife ki ba zaki saka hijab dinnan ba,"
Dariya sukai dika, sannan Balqis ta yafa mata mayafi kalar kayan ta
"Adda a haka zanje?"
"Wataran ma ba kaya zak yawo a gaban shi,"
Duka Hassana ta kai ma Hussai.
"Babbar banza kawai,"
Cikin jin kunya ta sinqe hijabin ta a jikin ta, tana zuba gaban Parlourn ta warware ta saka, a ranta tace,
'Ina na isa yawo a gaban wannan mayunwacin matan da wannan shigar, inaaa Ya Allah ka taimakeni, ni tsoro ma yake ban'
"In bazaki shigo ba ki fadan ina da abin yi,"
Da sauri ta shiga ta samu waje ta zauna nesa da shi, a takure, cike da jin tsoron shi.
'Ji wannan ko meye haka taje yi? An fada mata kowacce mace nake bi oho?'
(Yo ba gwanda ita ba ma, kai da ke shiga ramin shaddar kasuwa dan rainin wayo kawai😏)
Shiru sukai,ba mai cewa komai, a qashin gaskiya turaren ta ya masa dadi, ba kadan ba kuwa amma dan baqin hali ya hana ya yaba ko da kwalliyar ta ta ne ma.
Karkacewa yayi ya zaro kudi masu yawa, da gani zasu kai dubu dari ko sama, wurgawa yayi a gaban ta.
"Ga shi nan na san wataqila ace na bada, dan ku mata akwai ku da bidi'a baku tinanin ya aka samo kudi amma kuna son kashe su,"
Wani kallo ta masa, sannan ta tura kudin har gaban shi da hannun ta.
"Kar ka damu Yah, ai ba kai ka nemi aure na ba dama, kar ka manta matar sadaka ce ni, baka ni akai kyauta,ba mai buqatar kudin ka,"
Cike da mamaki, ya kalle ta, itan ma shi take kallo, tana jin tsoron shi yes, amma ba ta daukan wulaqanci musamman akan abinda bata roqa ba.