← Book details Kun Makaro Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 37 OF 41

Sashe 37

Kun Makaro Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Son tashi ka ci abinci, inshaa Allahu Allah ya amsa dikkan abinda ka roqa, kai dai ka ci gaba da zama yaro na gari, in kayi haka ka gama komai a rayuwar ka, zo kaci abinci, kar yayi sanyi,"

"Mama kema ki yafen dik abinda na maki a rayuwa ta, inshaa Allahu na maki alqawarin zamowa yaro na gari abin alfaharin ku, na dau darasi, da girmana ana bani kulawar qananan yara, tarviyya aka koma ban daga farko saboda watsi da nai da wadda aka min ina yaro, na gode wa Allah daya yo ni a cikn ahalin nan,"

"Sauran Baban ka da Baba General, ya kamata ka nemi gafar su, sannan ka samu Hajja ka mata godiya na musaman akan kulawa da lamarin ka da tayi,"

"Inshaa Allahu, ita na san me zan mata, su Baba kuwa yau yau dinnan zan nemi gafarar su,"

Abinci yaci yayi sallar Asr, yayi wanka da kyau, yana zabga qamshi yaje masjid ya dawo, a parlourn Hajja ya tadda iyayen nashi maza ya basu hakuri, kuma sun gamsu Khaleefa ya shiryu, dan haka sun yafe masa, sun kuma sanya masa albarka, Hajja ce ta fito cikin kwalliya kamar kullum, Khaleefa ne ya kalle ta, cikin zolaya yace,

"Gaskiya uwargida kin hadu, da zaki ban dana da yau mun fita on a date just me and u, dan na nuna maki irin yanda nake son ki a raina, kuma na nuna maki godiya ta a gare ki bata da iyaka,"

Cike da jin dadi Hajja ta kada ido kamar wata budurwa tace,

"Why not?"

"Da izinin wa?"

"Ohhh dear don't be a jalouse husband,"

"K na bada izini amma a dawo da wuri,"

"Yes sir"

Mayafin ta ta dakko, ska jera, ya riqe hannun ta, Baba General yayi gyaran murya, juyawa sukai sika kalle shi,cikin daure fuska ya nuna da hannun shi alamar ya sake mata hannu, dariya aka dauka a wajen, Baban Khaleefa har yana kwallar farin ciki, suna fita su John suka taso,

"Not even today man, we ar going on a date, a date, bama buqatar kowa, na sauya ku kun sani, ba saida ta zan je nayi ba,"

"Kuje abun ku muma fita zamuyi, ina ruwan mu da kai?"

"Ba ku da ruwa tabbas amma kar ku ce zaku bi mu yau, i want to show her my appreciation thats all,"

"K man sai kun dawo, Allah ya kiyaye, u better watch it,dik inda ka shiga muna da ido a wajen,"

Hannun Auwal ya saka a gaban idanun shi, alamin muna ganin ka.

Budewa Hajja mota yayi wadda take ta dariya, wato kowa bai yarda da Khaleefa ba, ta yarda da fitar nan ne dan shima ya shaqata, ya dade a nade a gida, sannan hakan zai sake bata damar cusa mishi aqidar da take son ya kasance yana da ita.

Wanj fancy restaurant suka je, ga kudi ga kyau, zama sukai, aka kawo masu abinci da abin sha, suna ci suna hira, mutane ana ta kallon su, ga tsohuwa ta sha gayu kamar amarya, ga yaro, matashi mai jini a jiki, kowa dai ya gan ta yaga kamilar dattijuwa, kamannin da suke ne ke korewa kowa shakku da zargi, dan mu ta nan wajejen hausawa ba kowa ke fita da matar shi on a date, ko a je cin abinci ba da sauran irin dabi'un nan na turawa da larabawa.

Hajja tayi nasara wajen koyar da Khaleefa wasu abubuwan na rayuwa masu mahimmanci, yaji dadin fitar d sukai sosai, bayan sun fita ya kaita shoping, taji dadi kwarai, ashe Khaleefa is so sweet ba wanda ya san hakan, yanzu gashi yana ta nuna masu halin shi mai kyau.

Daf magrib suka isa gida, kusan sai da ya yi wa kowa siyayya, musamman Ameerah da Aeeshaa,sai Hadiza da yaron su, Hajja ta taya shi zaban kayayyakin wanda suka dace.

**********************

Yau wata hudu kenan da haihuwar Hadiza,Hadiza ta murmure, sai dai har yanzu bata dawo da hasken ta ba dan tayi alqawarin daina sabon Allah ta hanyar shafe2n mai da zasu qara mata fari, Goggo ta tsoratar da ita sosai, akan hukuncin masu sauya halittar Allah.

Parlourn Hajja a cike yake da baqi, Aeeshaa da Umman ta da su Ameena dik sun zo, Iyayen Ammar gau zasu zo, da wasu dangin Baban Hadiza dan saka ranar aure, abinci da abin sha ne cike a parlourn, sai raha ke tashi da hirarrakin iyayen nasu, Hassana kuka kawai take na farin ciki, wai yau ita za a sakawa rana, Aeeshaa na ta lallashin ta, can qasan ran ta tana tinani bata ji fa ance saka ranar harda nasu ba, ko dai ba yanzu su za a mallaka masu junan su ba ne? Gaskiya sun matsu su gan su a inuwa daya, ai ya kamata a hada dika a huta.

"Tinanin me kk?"

"Ummah ban ji ance za a saka rana har da mu ba, naji ance na Adda Hassana da Yah Ammar, Yah khaleefa da Hadiza,mu fa?"

"Aeeshaa qaniyar ki, wato kin matsu ki bar ni ko?"

Kwatawa tai a cinyar Umma nata cike da shagwaba ta dora habar ta kan kafadar ta,

"Ummaah u knw how much i love u,just curious to knw za a hada dami kk a'a,"

"To nima ban sani ba, sai ki bari in sun fito muji,.....ke kuma ki daina mana kuka haka, ai murna zaki ba lokacin kuka bane wannan, ki godewa Allah, dama wani jinkirin alkhairi ne, gwanda ki aure a makare, akan ki auri wrong parson,"

"Haka ne Ummah, can't help it, kukan kawai ji nake yana zuwa,"

Ummeen ta da ta shigo dauke da abin sha ta zauna, tace,

"Yaran Ummee me ake tattaunawa ne?"

Da sauri Aeeshaa tace,

"Ba komai,"

Dariya suka sa dika, tabbas akwai wani abu kenan tinda take sauri kar a sani,

"Tambaya ta take wai da su za a saka rana ko ba su,"

"Su su wa?"

"Ita da Sabeer mana,"

"Ummaaaahhh,"

Tashi tayi ta bar wajen tana buga qafa irin na shagwaba, daidai lokacin Sabeer da Ammar suka shigo, Ammar baki har kunne, Sabeer fuskar shi a daure, kallon shi tai idon ta a waje, kar dai ba sa rana da su ba...........😨😨😨😨😨😨

*Tabdi jamm aiko da na je na sake dasa sabon zama a gidannan, wa zai raka ni😡😡*
💅🏼 *KUN MAKARO* 💅🏼

*BY HAERMEEBRAERH*

Page 29:

Da hannu ya mata alamar su je waje, ta kitchen suka je suka tsaya daga waje,

"Yah Sabeer me ya faru, naga fuskar ka babu walwla?"

Dan sosa kan shi yayi ya gyara tsaiwa,

"Naji ana ta saka rana ba a kira sunan mu ba, sai daga baya wai naji Baba General na cewa mu in an tashi nasu an daura auren mu, kamar bamu da wani mahimmancin da za a mana yanda aka masu, cikin bayyana muma fa ranar mu za a sa, kamar yanda ake maganar nasu,"

Dan murmushi tayi, ta kai fuskar ta tana leqa tashi, wai d gaske fushi, qin kallon ta yayi da, sai daga baya suka hada ido, nan da nan idon shi ya kawo haske saboda nutsuwar daya samu ta hanyar kallon fuskar ta.

(Ya ke 'yar uwata, kin san kuwa tasirin kallo? Kallo ya na da mabanbantan amfani, daya daga cikin amfanin kallo shine ki kwantar ma da mijin ki hankali ta hanyar kallo, in kina da zuciya mai kyau kallon ki xai tasiri a wajen dik wanda kk kalla da kyautatawa, amma zuciyar ki in ba alkhairi cikin ta kallon kwantar da hankali ba zai tasiri awajen ki ba,a lokuta da dama, ki gwada ki gani, komai fushin mijin ki, ki daure ku hada ido dashi, ki sakar masa murmushi mai qayatarwa, ki masa kallon da zai tafi direct zuwa zuciyar shi, inshaa Allahu zaki ga ya sassauta,koda so kk ya tausaya maki akan wani abun, kallo cike da fuskar tausayawa na tasiri, sai dia ina sake tinatar da mu ki kyauta ta zuciyar ki kafin kallon ki ya zama mai tasiri da isar d saqon ki inda ya dace)

"Yah Sabeer, Abban Ameerah, ko ka manta kai mijin bazawara ne wai? So kk a maka komai irin na samari ko? To ka qaro budurwa ka hada mu kaga in ba ai maka ba,"

Dariya take cike da sautin tsokana a ciki, shima dariya ya sake, sannan a hankali ya fara rage dariyar shi, yana kallon ta,tana dariya, cikin husky voice din shi ya furta mata,

"Ko a burwai ba za a samu budurwa da kamar ki ba a waje na, kin fi min 'yan mata kyawawa masu saura da mulki d kudi guda hudu, ko za a aura min su a rana daya dan gata in aka ha a ni ke an gama dani, so nake na raya sunnar auren bazawara nima,tinda wasu suna dabbaqa sunnanr auren budurwa, kinga ni harda kyauta mai girma ta diya na samu, Allah ya sanya mana albarka my love,"

"Ameen mine alone, ban hada son ka da kowa ba Yah Sabeer, sai yanzu nake tausaya maka, lokuta da dama har kuka nake, inna tina lokacin da ka dauka kana dakon so na, ka sha azaba matuqa, dan dik sanda na so ganin ka ban gan ka ba ina jin zuciya ta na zafi har sai na gan ka ko naji muryar ka nake jin dadi, ya Allah ka bamu rai d lafy ka mallaka mana junan mu da dikkan albarka d alkhairi,"

"Ameen my wife,"

Ba qaramin dadi taji ba da kunya shige shi tai tana dariya, ganin su Umma still a parlour ne ya sa ta yin turus, kusan kowa na wajen har Hajja, ana ta hirar yanda biki zai kasance, domin Sati biyu kawai aka saka, sai dariya ake ma Sabeer ya da ya nuna rashin jin dadin shi dan kawai Baba General yace shida Aeeshaa an hada su da 'yan uwan su, kamar cewa akai ba za a aura masa Aeeshan ba.

"Ni fa na zaci daga nan gidan su suka wuce ma da naji shiru,"

"Yah Ammar dan kai ne xan kyale ka, amma da ba kai bane da nace ai gwanda mu, wasu kuma ji suke kamar su bar garin ma suje qasashen turawa dan shaqatawa,"

Dariya wajen ya dauka dan a fakaice dai ta rana kenan,
Chapter 37 · 0% Book details