← Book details Kun Makaro Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 36 OF 41

Sashe 36

Kun Makaro Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Dan girman Allah ki daina mana wannan dan iskan kukan, ba zaki kira sunan Allah ba sai tonon silili da iface2, in kk mutu kina wannan hayaniyar fa?"

"Na tuba, na tuba Allah na tuba ka yafe min,ba zan qara cikin shege ba, ni ko na halal din ma ba zan ba, wayyoo Allah na, natuba,"

Hajja suka kira ta aiko da mota, sannan tace suma gasu nan zuwa, asibiti aka wuce da Hadiza mai kyau da tsada, nan midwifes suka shiga dawainiyar taimaka mata dan ta haihu lfy.

Shigar su da awa daya da mintuna Hadiza ta sauka lfy, ta samu Yaro namiji, kar ku ga kuka wajen Goggo da Hadiza, Hajja ma dik qarfin zuciyar ta da ta zo sai da ta koka, kuka tayi sosai, ganin yaro lafiyayye sun samar da shi ta gurbatacciyar hanya.

Haka akai ta zuwa asibitin har da Aeeshaa, ta zo duba Hadiza ko dan Goggo, da kma Umarnin Hajja, koma me ya faru ya faru, Hadiza dai zata shiga zuri'ar su, dan haka dole ta san ya zatai ta hada kan su, kuma ta kula da Aeeshaa bata dau abun da wani nufi ba, ko a jikin ta, har daukan yaron tayi, Hajja ce ta amsa waya.

"Ku shigo daki na biyar, nan muke, Auwal ku tsaya waje, ni dai yaron nan ya nuna ya nutsu ne amma har yanzu ina tsoron shu'umancin shi, kar ya samu hanya ya gudu,"

Khaleefa na tsaye kusa da Auwal yaji komai, kuma ran shi ya baci, ya gyarun ma amma matar nan har yanz bata yarda da shi ba, a yanda yaci azaba, kuma ya sha wa'azi kala2 da take kunna masa, da wanda take masa in yau aka bashi mace karuwa ba sai dai ido ba, na dama kullum neman gafara yake, rai a bace ya shiga dakin

"Hajja ki daina min haka bana so, ki sallami wadannan qattan banzan, ni ba zan yarda ina tafe gardawa na bina ba,"

"Gaka nan qaton banza, barka kazo an maka haihuwa amma kana zancen banza, ku bashi dan shi, ya masa addu'a, da kiran sallah, ga shi nan,"

Amsar yaron yayi, nan take soyayyar shi ta shiga ran shi, kama suke sak, amma shi baqi ne yaron, kalar maman shi ya dakko kenan, kiran sallah ya mishi dama da hagu, sannan nan take ya rada masa suna da Ahmad, hawaye yake cike da quncin samar da wannan kyakkyawar halittar ta haram, ba su yaron yayi ya fita yana kuka sosai, waje ya samu ya zauna, Auwal na kan shi, hakuri yaji Auwal na bashi, yau ce rana ta farkk kalma mai dadi da ta hada su.

Share hawayn shi yayi,ya miqa masa hannu suka gaisa John ma haka.

Aeeshaa ce ta fito tana amsa waya,

"Na'am Yah Sabeer ka iso? K gani nan zuwa, na aje masu abincin, ka dakko Ameerah? Dan na san rikicin ta yawa ne da shi, tin da akai yayen nan kamar wadda akai wa mugun abu,"

"Mugun abu akai mata mana,ke dai yi kixo mu koma gida, yau so nake mu dan je shoping, a siyo mata kayayyakin da zai debe mata kewar maman,"

Dariya Aeeshaa tayi sannan tace,

"Yah Sabeer kenan Abban Ameerah, bari na masu Hadizan Sallama kar su ga na tafi haka kawai,"

Juyawar nan da zatai ta gan shi, cikn tsananin tsoro tayi baya, tare da zaro idanu waje, fuskar shi tayi jawur kamar garwashin wuta..........

*Kai kuma fushin me ye? Ko manja ka shafa a fuskar bamu da labari?😚*
💅🏼 *KUN MAKARO* 💅🏼

*BY HAERMEEBRAERH*

Page 28:

"Da uban wa kk waya har kk cewa 'yata 'yar shi?"

"Ban gane kana tambayata da wa nake waya ba, ina ruwan ka dani? Ohhhh sorry na manta ashe fa kai yayana ne, ina magana ne da Yah Sabeer, kuma uban Ameerah ne tinda ko kaqi ko kaso qanin ka ne shi,"

"Me ye a tsakanin ku da kk kashe murya kk magana kamar kina magana da mijin ki?"

"Inshaa Allahu mijina ne, Allah ya amsa maganar ka, kana da matsala akan hakan?"

"Baki da hankali ne? Da yarinyar tawa zaki wani auren? Kuma ma Sabeer a dik mutane?"

"Yarinyar ka auren ka ne akai na? Sabeer akan dik mutane ai gwanda shi akan ka ma ba mutane ba, kaga ba zan iya sa'in sa da kai ba a mutane, yanzu bakina ya bude, zan iya kwana kana fada ina fada, amma ba mutunci na bane, saboda haka in kana da magana ka zo gida bayan mun dawo daga shooopinggggg,"

Juyawa tai ta shige dakin da aka kwantar da Hadiza, zuciyar ta wasai ko haushin shi datake ji da babu, dan ta samu ta fidda abinda ke qulle a zuciyar ta ta, ya isa haka, haba, mutum kamar wani shaidan.

Sallama ta musu Hajja ta mata fatan alkhairi, ta ce ta gaida mata su Ameenaa, ita kuma ta bada saqon gaisuwa zuwa Baba General, ta wuce, Khaleefa na ganin fitar ta, yace shima gida zashi, su kai shi ha dakko diyar shi, ba zai bar ta a hannun su ba,

"Amma dai ka san ba wai umarnin ka muke bi ba ko? Kai kk bin umarnin mu, in kana so bi umarnin ka kaje ka nemi izini wajen Hajja,"

"Comw on, yarinya ta ce fa wajen wani qato, ba zan taba yarda ta zauna wajen su ba,"

"Kaiii....zo nan,"

Bammm ta maida qofar ta rufe, kallon qofar yayi ya lumshe ido cikin bacin rai, wannan tsohuwar fa tana ban matsala.

"Meye matsalar ka da Ameerah da kuma Aeeshaa da ba saka iya barin mu koma gida ba, a asibiti zaka zo kana sai da mana halin ka kowa na karba,"

"Hajja ba ki ji wai fita zasuyi da Sabeer da Ameerah ba?"

"In na ji sai na hana su? Ba diyar su bace suma, beside kace kai baka son yarinyar nan, ga wadda kk so nan kayi cikin shi ai ba aure ko? Kuma da alama ya shiga ran ka tinda yanda ma ka dauke shi daban ne, har suna ka rada masa, so kar na sake jin maganar Aeeshaa a bakin ka balle Ameerah da Sabeer,in zaka yi maganar su inji alkhairi, yarinyar nan sai in ta girma ta ga damar kula ka amatsayin uba, ba mai bata ka a idon ta amma ba wanda zai baka ita mahaukacn banza kawai,sai kayi kamar ka samu lfy, sai ka qara bazama,"

"Hajja kina nufin banda hankali kenan,"

"Kwarai d gaske, in kana da hankali wanda yake son naka kana da kamar shi ne, Sabeer dinnan da kk gani kwanan nan na san ya dade yana son Aeeshaa a sanadin a baka ita ya hakura, ba dan haka ba da Ameeran ma tashi ce, ka mata sakin hauka saboda kan ka na hayaqi ance ka sake ta, kuma naga dai ba son ta kk ba, tinda ka fada aura maka akai ba kai kace kana so ba,"

"Ni yaushe na taba cewa ban son ta, ni ba wanda ya taba jin nace bana son ta,in ma na fada nace na janye, kawai dan ba sona ake ba shi yasa komai nayi bana daidai, dik wani abu da ba ko son nayi ba na daina ba yanzu, kum nace in son mada min mata ta da 'yata yanzu, ba shikenan b a maida ta shi ya samu wata,"

Hajja ba zata iya da wannan haukan ba, yi masa bayani ma baida amfani, saki uku a gidan uban wa aka taba maida shi?

"John ! Auwal ! Ku maida min shi gida,"

"Wai ya za a dinga min abu kamar wani barawo ko wani dan kidnerping? Ni to ba gida zani ba zanje na dakko mata ta da diyata,"

Ko kula shi basuyi ba suka sashi gaba, da kallon ka taka mu fita ko kasha na jaki kuma a ka zamu fidda ka, sarai ya san kallon, tinda ba yau yake tare da su ba almost a year now.

Ranshi bace ya fita yana zuba sauri, mota ya bude ya fada ya qame qam,sai muzurai yake yana tsaki,

Bayan sun isa gida ne ya shige dakin shi, in ya rufe ido Aeeshaa yake gani, yanda take waya take nishadi da annashuwa, bai taba sanin wannan side din nata ba, ashe mace ce mai cike da so da qauna a zuciyar ta, farin ciki da nishadi na baibaye da ita, ashe shi ne fitilar daya disashe ta, bai san yana kuka ba sai da yaji sautin a kunnen shi, ya so ya riqe kukan amma inaa ba zai riqu ba, fashewa yayi d kuka sosai, yana sambatu,

"Aeeshaa ki yafe min, k yafen dikkan munanan abubuwan da na maki, ban taba zatan zaki zama mace mai mahimmanci a rayuwa ta haka ba, a zatona jikin ki kawai nake so,ashe zuciyar ki ma ta shiga tawa, a daidai lokacin da NA MAKARO, dik abinda kk min a zaman mu mai dadi ina fatan Allah ya dadada maki fiye da hakan kema, Allah ya sa ki farin ciki Aeeshaa, Allah ya raya Ameerah, Allah ya baku zaman lfy, dole na karbi qaddara ta ta auren Hadiza, ni na jawa kai na, Allah na gode maka daka nuna min gaskiya ka bani ikon bin ta, Ya Allah ka yafe min munanan aikin dana aikata a baya,Allah ka kare ni da aikata laifi a kan sani na a gaban rayuwa ta, inna aikata laifi a bisa kuskure Allah ka yafe min,"

Shessheqar kuka yaji, ya juya daga durquson da yayi a qasa, mahaifiyar shi ce riqe da abincin shi kasancewar Hajja na asibiti bata dawo ba, yau dai tayi waya tace Maman shi ta kai masa, cikin murna kuwa ta debi abincin, ta kai masa, tana shiga taji yana kuka, yana addu'a, wani irin dadi ne ya wanke zuciyar ta, da na gari abn so ne ga kowa, samun suruka kamar Hajja abin na da wahala a wannan zamani, wadda zata tsaya ta jajirce don ganin ta kare ahalin ta daga wuta, ta samu nasara sosai, ba abinda za su ce ma Hajja sai dai Allah ya mata kyakkyawan qarshe,ya qara mata shekaru masu albarka ta ci gaba da sa su a hanya.
Chapter 36 · 0% Book details