Sashe 1
Kun Makaro Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
💅🏼 *KUN MAKARO* 💅🏼
*BY HAERMEEBRAERH*
*Ina farawa d sunan Allah,mai rahama mai jin qan bayin shi, tsira da aminci su tabbata ga Annabi Muhammad sallahu alaihi wa sallam, bayan lokaci mai tsaho yau inshaa Allah zan kawo maku sabon labari, wanda nake fatan ya sauya rayuwar mutane da dama, ta fuska kala2, labari ne mai qunshe da darrusa mabayyana, ina fatan zaku bude zuqatan ku masu albarka, kamar yanda kuka saba, domin fahimta da daukan darussan dake ciki.*
*Kamar koda yaushe ina roqon makaranta novels dina,ku na adanawa koda bakuyi sha'awar bi ba a yanxu, kar sai gaba ku zo kuna nema lokacin an wuce kuuu, wannan rubutun ina son nayi d sauri fiye da da, saboda kunsan na koma makaranta, ina roqon addu'ar ku akan samun nasara akan wannan karatun nawa, na gode maku*
Page 1:
Aeeshaa ke zaune a kan kujerar zaman mutum daya, dauke da wuqa da kwano, tare da kubewa tana yankawa, tana yi tana kallon lokaci, aiki take kamar wata inji, ba hutu, abinda ke tsaida ita wannan aiki, sallah.
Cikin sauri ta tashi ta koma kitchen ta dau turmi da tabarya, ta saba wannan kubewar da ta yanka, tana gamawa ta je ta zuba a tukunyar miyar data ji nama da kifi, ta kada ta rufe kadan, sannan ta koma kan tuwon semo da ta tuqa tin minti biyar da ya wuce, tuqawa tayi taga yayi,maza ta dakko leda da mazubi ta fara zubawa tana murde ledar tana sawa a inda ya dace, da sauri ta juya kan miyar dataji ta fara alamar zubewa, ta kashe gas din, ta qarasa rufe tukunyar, sannan ta qarasa kwashe tuwon ta.
Tana kammalawa ta diba fridge taga zobon data hada ya dau sanyi, murmushi ne ya kwace mata, da sauri ta koma ta wanke dik abinda ya dace, ta fara jera abincin akan dinning, sai da ta kammala komai, ta juya da sauri dan wucewa dakin ta tai wanka ta shirya islamiyya, kar ta makara kamar yanda tai da safe, zuwa makarantar boko, taji kiran Umman su, zuciyar ta ce ta buga da qarfi.
"Na'am Umma gani nan zuwa"
Cikin azama ta nufi dakin Umman nasu, inda ta tsaya a bakin qofa, tai sallama tare da qwanqwasa qofar, shiru kafin daga bisani ta amsa mata cikin tsawa,
"Dan ubanki sai yaushe zaki riqe akan ki inna kira ki kina shigowa? Sai ki tsaya dan gulma kina wani jira sai na baki izinin shiga,kina abu sai kace wata uwar mata, da ban son ganin ki zan kira ki ne?"
Shiga Aeeshaa tayi, ta samu gefe ta tsaya tace,
"Umma kiyi hakuri,gani,"
"Yauwa nace kin gama abincin ne?"
"Eh na gama,na hada komai kan dinning, yanzu shirin islamiyya zan, kar na makara kinsan yau banje boko ba saboda makara da nai, na kammala komai har dare nai abincin ma tinda naga tiwo ne"
"Waya saka ki yi har dare? Ni nace ki dafa har dare ko iyayi? Ko kin fini sanin me ya fi dacewa da ayi ne?"
"Umma dan Allah kiyi hakuri bana son ranki na baci, bari inna dawo islamiyya kome kk so zan dafa, dan Allah ko zan fashin boko bana son nai fashin islamiyya,"
"Alhuda huda kenan sarkin karatu, wuce ki tafi,kina dawowa kizo akwai wankin da zaki hada dana qannen ki kimin, kinga sai kisa uniform dinki ma dika ki wanke ko?"
"Eh hakan ma yayi Umma na tafi sai na dawo,"
"To"
Aeeshaa da sauri ta shirya ta fito, dan ko wankan bata samu yi ba gudun makara, in ta dawo tayi.
"Aunty Aeeshaa muma mun shirya,"
"To Ameena maza muje kar mu amshi bulalan latti ko? Ina Abdul hakeem?"
"Gani meye?"
"Kai dai Allah ya shirye ka baka da kunya ko kadan har yanzu,girma kk amma kana shiga daji,"
"An shiga din, ni na tafi kar ku taho ku tsaya surutu,"
"Aunty Abdul baida kunya, amma karki fada masa nace haka,"
Murmushi Aeeshaa tayi, ta shafa kan qaramar qanwar ta, sannann suka fita daga gate din gidan nasu, sannan tace.
"Kar ki damu, ba zan fada masa ba,ai dama baida kunya ko baki fada ba, muyi sauri,kinga ga yara can sai gudu suke suma,"
Qara sauri sukai, dankar su makara, suna zuwa suka shige ajujuwan su, Abdul Hakeem ajin su daya da Aeeshaa,Ameena na ajin dake qasa danasu, domin itace qaramar su.
Karatu ake amma hankalin ta yau sam baya jikin ta,yana can wajen tinanin rayuwar gidan su, gaba daya basu tausaya mata, basu san tayi abu a gode mata ba dik da qoqarin da take yi, tana baut masu kamar bata son jikin ta,amma ko a jikin su, burin su kawai ta masu aiki, su amfana da ita kuma su zage ta, sai kace ba Umman tasu ce ta haife ta ba, tinawa da mahaifin ta da ya rasu ne yasa wata kwalla me zafi ta saukar mata,to ko dai ba Umman ce mahaifiyar ta ba ne? Tinda mahaifin ta ya rasu tin tana shekara bakwai, sabida cancer, .......
"Aeeshaa tinanin me kk haka? Har da kuka?"
A firgice ta miqe tsaye ta fara rera karatun da ta haddace jiya,a zaton ta an tashe ta ne dan tai karatu, nan da nan kuwa ajin ya dau dariya,banda Abdul,wanda ya bata rai, ya juya ido, ya kalli waje.
Shiru tayi,dan ta kula da abinda ta yi, nan ta sunkunyar da kan ta, tana son taji me malamar tasu ta fada da farko.
"Aeeshaa tambayar ki nake me ya same ki?"
"Kaiii kaiinaaa ke ciwoo"
"Wayyoo sannu maza jeki gida,tinda ba nisa, sai kisha magani, ki zauna, gobe kin bada haddar ki,"
Da sauri ta fara karatun ta,dan bata son abinda zai sa ace ta koma gida ba a tashi ba aiki na can na jiran ta, bata huta da aikin da tagama tiqa ba tin safe.
Kyale ta malamar tayi, ta kammala, sannan suka dora sabon karatu.
Qarfe 5:30pm suke tashi,dan haka suna tashi gida ta nufa,ita da qannen ta.
Suna shiga taga kan dinning kaca2,ga qawayen Umman ta a parlour suna ta hira, ana shewa, an barbaza kayan sayarwa a qasa,ga cups nan da plates anci snaks, sai ciniki sike ma Umman nata,suna yi suna hirar batsa, lura da dawowar yaran yasa suka nutsu,
"Ah Aeeshaan Umman ta,kun dawo kenan, yanzu nake cin wani daddadan abinci, Umman ki tace ke kk dafa, ina matuqar mamakin ki Aeesha, dika dika shekarar ki sha shida amma kin iya abinci kala2, kamar wata babba,"
Wani irin dadi ne ya kama Aeeshaa,yau a rayuwar ta gaba daya an yabe ta, ji tai kamar ta kama Aunty Safnaa ta rungume dan murna, ta bude baki zatai magana kenan Umman ta ta amshe.
"Wannan me shegen son zaman dakin? In ba dan nayi qoqari na tsaya tsayin daka ba da ko ruwan zafi bazata iya dafawa ba,sai shegen son karatu, kamar wata babbar mace, kullum ina nuna mata hanyar kasuwancin nan tana kauda kai, bata san ko kayi karatu ba wani aiki zaka samu ba, maza ma wahala suke sha bare ke mace da zaki qare a dakin miji,"
Aeesha bata ji dadin kalaman Umman ta ba amma cikin murmushi tace,
"Umma me za a dafa? Ko kawai naje na dora abinda ya dace?"
"Kije ki yi dik abinda kk ga ya dace, ga wankin nan karki manta"
"To Ummana"
miqewa tayi ta shiga ciki, ta sauya kayan jikin ta, ta koma Office din nata wato kitchen, taliya ta dafa da miya, dan ta samu sauqi, da sauri cikin kazar2 ta wuce dakin Umman nata ta hada kayan wankin su, ta koma ta dauki na qannen nata ta fita qofar baya ta kama wanki,ba ita ta gama ba sai ana kiran magrib.
Bayan tayi sallar magrib, tayi azkar,tayi karatun ta na qur'ani, sannan ta yi isha'i, ta nadr abun sallah, ta leqa wajen umman ta ta tambaye ta ko akwai abinda zata mata?
"Ba abinda za ki min yanzu, ki tabbatar dai kin gyara kan dinning kan ki kwanta,"
"To Ummana sai fa safe,"
"Allah ya tashe mu lfy,"
Tana mamakin Umman ta, wai ace magana mai dadi bazata hada su ba, komai a cikin fada yake da kushewa, ga qannen ta nan suma sun dauka, musamman Abdul,gwanda2 Ameena, wataqila itan ma dan yarinya ce,ba zata wuce shekara 5 ba.
Daga komai tayi takai kitchen, ta kashe fitulu ta kulle masu qofa ta tofa ayatul kursiyyu sannan ta yi dakin ta.
Tana Assignment din ta bacci ya dauke ta ko kammalawa batai ba tsabar gajiya.
********************
"Wai makaranta nan da can ki taka kije sai na kai ki na dawo dake, ga su Ameena dake nesa, suma saina kaisu, na aje su, ke ko tausaya min bakiyi,"
Hawaye ne ya gangaro ma Aeeshaa, tai saurin saka hannu ta share, ita dik wahalhalun da take ba'a gani sai kaita makarantar da ake shine zai zama abin magana, lallai bin iyaye yana da wahala, Allah ya bata ikon cin wannan jarabawa, yanzu in ta amsa ta tace ta barta tana zuwa ta jama kan ta aiki, taje ta dawo ta tiqi aiki, ga shi dama ta fita a gajiye, a boko sam ba ta da wani qoqari, saboda aiki ya mata yawa, ga uban fashi datake dokawa.
"Kiyi hakuri Ummana"
"Mtss da an magana kiyi hakuri, kiyi hakuri, ya zan ai dole na hakura"
Sun isa gida, kowa ya fita ya rufe qofa, suka ganshi tsaye a bakin qofar shiga parlourn gidan, riqe da Cup a hannin shi, da shi da Umman sukai dariya, dan ta san da dawowar shi.
Bakin su sake, zuqatan su cike da murna suka nufe shi a guje, banda Aeeshaa da ta kasa koda motsawa.
Binta yake da wani irin kallon da ba mai iya fassara shi, dan shi kan shi bai san meke cikin zuciyar shi ba game da wannan halitta da ya gani a gaban shi........
*Casssss my fiful how do u like this page? Hope ya maku dadi? In yayi dadi wanna see ur comment to give u more page💃🏻💃🏻*
💅🏼 *KUN MAKARO* 💅🏼
*BY HAERMEEBRAERH*
Page 2:
"Ke wato kin girma shine ba zaki zo ba?"
Cike da jin kunya ta kalle shi, ta isa gare shi, ya kai hannu zai taba ta ta dan ja baya cikin dabara,
*BY HAERMEEBRAERH*
*Ina farawa d sunan Allah,mai rahama mai jin qan bayin shi, tsira da aminci su tabbata ga Annabi Muhammad sallahu alaihi wa sallam, bayan lokaci mai tsaho yau inshaa Allah zan kawo maku sabon labari, wanda nake fatan ya sauya rayuwar mutane da dama, ta fuska kala2, labari ne mai qunshe da darrusa mabayyana, ina fatan zaku bude zuqatan ku masu albarka, kamar yanda kuka saba, domin fahimta da daukan darussan dake ciki.*
*Kamar koda yaushe ina roqon makaranta novels dina,ku na adanawa koda bakuyi sha'awar bi ba a yanxu, kar sai gaba ku zo kuna nema lokacin an wuce kuuu, wannan rubutun ina son nayi d sauri fiye da da, saboda kunsan na koma makaranta, ina roqon addu'ar ku akan samun nasara akan wannan karatun nawa, na gode maku*
Page 1:
Aeeshaa ke zaune a kan kujerar zaman mutum daya, dauke da wuqa da kwano, tare da kubewa tana yankawa, tana yi tana kallon lokaci, aiki take kamar wata inji, ba hutu, abinda ke tsaida ita wannan aiki, sallah.
Cikin sauri ta tashi ta koma kitchen ta dau turmi da tabarya, ta saba wannan kubewar da ta yanka, tana gamawa ta je ta zuba a tukunyar miyar data ji nama da kifi, ta kada ta rufe kadan, sannan ta koma kan tuwon semo da ta tuqa tin minti biyar da ya wuce, tuqawa tayi taga yayi,maza ta dakko leda da mazubi ta fara zubawa tana murde ledar tana sawa a inda ya dace, da sauri ta juya kan miyar dataji ta fara alamar zubewa, ta kashe gas din, ta qarasa rufe tukunyar, sannan ta qarasa kwashe tuwon ta.
Tana kammalawa ta diba fridge taga zobon data hada ya dau sanyi, murmushi ne ya kwace mata, da sauri ta koma ta wanke dik abinda ya dace, ta fara jera abincin akan dinning, sai da ta kammala komai, ta juya da sauri dan wucewa dakin ta tai wanka ta shirya islamiyya, kar ta makara kamar yanda tai da safe, zuwa makarantar boko, taji kiran Umman su, zuciyar ta ce ta buga da qarfi.
"Na'am Umma gani nan zuwa"
Cikin azama ta nufi dakin Umman nasu, inda ta tsaya a bakin qofa, tai sallama tare da qwanqwasa qofar, shiru kafin daga bisani ta amsa mata cikin tsawa,
"Dan ubanki sai yaushe zaki riqe akan ki inna kira ki kina shigowa? Sai ki tsaya dan gulma kina wani jira sai na baki izinin shiga,kina abu sai kace wata uwar mata, da ban son ganin ki zan kira ki ne?"
Shiga Aeeshaa tayi, ta samu gefe ta tsaya tace,
"Umma kiyi hakuri,gani,"
"Yauwa nace kin gama abincin ne?"
"Eh na gama,na hada komai kan dinning, yanzu shirin islamiyya zan, kar na makara kinsan yau banje boko ba saboda makara da nai, na kammala komai har dare nai abincin ma tinda naga tiwo ne"
"Waya saka ki yi har dare? Ni nace ki dafa har dare ko iyayi? Ko kin fini sanin me ya fi dacewa da ayi ne?"
"Umma dan Allah kiyi hakuri bana son ranki na baci, bari inna dawo islamiyya kome kk so zan dafa, dan Allah ko zan fashin boko bana son nai fashin islamiyya,"
"Alhuda huda kenan sarkin karatu, wuce ki tafi,kina dawowa kizo akwai wankin da zaki hada dana qannen ki kimin, kinga sai kisa uniform dinki ma dika ki wanke ko?"
"Eh hakan ma yayi Umma na tafi sai na dawo,"
"To"
Aeeshaa da sauri ta shirya ta fito, dan ko wankan bata samu yi ba gudun makara, in ta dawo tayi.
"Aunty Aeeshaa muma mun shirya,"
"To Ameena maza muje kar mu amshi bulalan latti ko? Ina Abdul hakeem?"
"Gani meye?"
"Kai dai Allah ya shirye ka baka da kunya ko kadan har yanzu,girma kk amma kana shiga daji,"
"An shiga din, ni na tafi kar ku taho ku tsaya surutu,"
"Aunty Abdul baida kunya, amma karki fada masa nace haka,"
Murmushi Aeeshaa tayi, ta shafa kan qaramar qanwar ta, sannann suka fita daga gate din gidan nasu, sannan tace.
"Kar ki damu, ba zan fada masa ba,ai dama baida kunya ko baki fada ba, muyi sauri,kinga ga yara can sai gudu suke suma,"
Qara sauri sukai, dankar su makara, suna zuwa suka shige ajujuwan su, Abdul Hakeem ajin su daya da Aeeshaa,Ameena na ajin dake qasa danasu, domin itace qaramar su.
Karatu ake amma hankalin ta yau sam baya jikin ta,yana can wajen tinanin rayuwar gidan su, gaba daya basu tausaya mata, basu san tayi abu a gode mata ba dik da qoqarin da take yi, tana baut masu kamar bata son jikin ta,amma ko a jikin su, burin su kawai ta masu aiki, su amfana da ita kuma su zage ta, sai kace ba Umman tasu ce ta haife ta ba, tinawa da mahaifin ta da ya rasu ne yasa wata kwalla me zafi ta saukar mata,to ko dai ba Umman ce mahaifiyar ta ba ne? Tinda mahaifin ta ya rasu tin tana shekara bakwai, sabida cancer, .......
"Aeeshaa tinanin me kk haka? Har da kuka?"
A firgice ta miqe tsaye ta fara rera karatun da ta haddace jiya,a zaton ta an tashe ta ne dan tai karatu, nan da nan kuwa ajin ya dau dariya,banda Abdul,wanda ya bata rai, ya juya ido, ya kalli waje.
Shiru tayi,dan ta kula da abinda ta yi, nan ta sunkunyar da kan ta, tana son taji me malamar tasu ta fada da farko.
"Aeeshaa tambayar ki nake me ya same ki?"
"Kaiii kaiinaaa ke ciwoo"
"Wayyoo sannu maza jeki gida,tinda ba nisa, sai kisha magani, ki zauna, gobe kin bada haddar ki,"
Da sauri ta fara karatun ta,dan bata son abinda zai sa ace ta koma gida ba a tashi ba aiki na can na jiran ta, bata huta da aikin da tagama tiqa ba tin safe.
Kyale ta malamar tayi, ta kammala, sannan suka dora sabon karatu.
Qarfe 5:30pm suke tashi,dan haka suna tashi gida ta nufa,ita da qannen ta.
Suna shiga taga kan dinning kaca2,ga qawayen Umman ta a parlour suna ta hira, ana shewa, an barbaza kayan sayarwa a qasa,ga cups nan da plates anci snaks, sai ciniki sike ma Umman nata,suna yi suna hirar batsa, lura da dawowar yaran yasa suka nutsu,
"Ah Aeeshaan Umman ta,kun dawo kenan, yanzu nake cin wani daddadan abinci, Umman ki tace ke kk dafa, ina matuqar mamakin ki Aeesha, dika dika shekarar ki sha shida amma kin iya abinci kala2, kamar wata babba,"
Wani irin dadi ne ya kama Aeeshaa,yau a rayuwar ta gaba daya an yabe ta, ji tai kamar ta kama Aunty Safnaa ta rungume dan murna, ta bude baki zatai magana kenan Umman ta ta amshe.
"Wannan me shegen son zaman dakin? In ba dan nayi qoqari na tsaya tsayin daka ba da ko ruwan zafi bazata iya dafawa ba,sai shegen son karatu, kamar wata babbar mace, kullum ina nuna mata hanyar kasuwancin nan tana kauda kai, bata san ko kayi karatu ba wani aiki zaka samu ba, maza ma wahala suke sha bare ke mace da zaki qare a dakin miji,"
Aeesha bata ji dadin kalaman Umman ta ba amma cikin murmushi tace,
"Umma me za a dafa? Ko kawai naje na dora abinda ya dace?"
"Kije ki yi dik abinda kk ga ya dace, ga wankin nan karki manta"
"To Ummana"
miqewa tayi ta shiga ciki, ta sauya kayan jikin ta, ta koma Office din nata wato kitchen, taliya ta dafa da miya, dan ta samu sauqi, da sauri cikin kazar2 ta wuce dakin Umman nata ta hada kayan wankin su, ta koma ta dauki na qannen nata ta fita qofar baya ta kama wanki,ba ita ta gama ba sai ana kiran magrib.
Bayan tayi sallar magrib, tayi azkar,tayi karatun ta na qur'ani, sannan ta yi isha'i, ta nadr abun sallah, ta leqa wajen umman ta ta tambaye ta ko akwai abinda zata mata?
"Ba abinda za ki min yanzu, ki tabbatar dai kin gyara kan dinning kan ki kwanta,"
"To Ummana sai fa safe,"
"Allah ya tashe mu lfy,"
Tana mamakin Umman ta, wai ace magana mai dadi bazata hada su ba, komai a cikin fada yake da kushewa, ga qannen ta nan suma sun dauka, musamman Abdul,gwanda2 Ameena, wataqila itan ma dan yarinya ce,ba zata wuce shekara 5 ba.
Daga komai tayi takai kitchen, ta kashe fitulu ta kulle masu qofa ta tofa ayatul kursiyyu sannan ta yi dakin ta.
Tana Assignment din ta bacci ya dauke ta ko kammalawa batai ba tsabar gajiya.
********************
"Wai makaranta nan da can ki taka kije sai na kai ki na dawo dake, ga su Ameena dake nesa, suma saina kaisu, na aje su, ke ko tausaya min bakiyi,"
Hawaye ne ya gangaro ma Aeeshaa, tai saurin saka hannu ta share, ita dik wahalhalun da take ba'a gani sai kaita makarantar da ake shine zai zama abin magana, lallai bin iyaye yana da wahala, Allah ya bata ikon cin wannan jarabawa, yanzu in ta amsa ta tace ta barta tana zuwa ta jama kan ta aiki, taje ta dawo ta tiqi aiki, ga shi dama ta fita a gajiye, a boko sam ba ta da wani qoqari, saboda aiki ya mata yawa, ga uban fashi datake dokawa.
"Kiyi hakuri Ummana"
"Mtss da an magana kiyi hakuri, kiyi hakuri, ya zan ai dole na hakura"
Sun isa gida, kowa ya fita ya rufe qofa, suka ganshi tsaye a bakin qofar shiga parlourn gidan, riqe da Cup a hannin shi, da shi da Umman sukai dariya, dan ta san da dawowar shi.
Bakin su sake, zuqatan su cike da murna suka nufe shi a guje, banda Aeeshaa da ta kasa koda motsawa.
Binta yake da wani irin kallon da ba mai iya fassara shi, dan shi kan shi bai san meke cikin zuciyar shi ba game da wannan halitta da ya gani a gaban shi........
*Casssss my fiful how do u like this page? Hope ya maku dadi? In yayi dadi wanna see ur comment to give u more page💃🏻💃🏻*
💅🏼 *KUN MAKARO* 💅🏼
*BY HAERMEEBRAERH*
Page 2:
"Ke wato kin girma shine ba zaki zo ba?"
Cike da jin kunya ta kalle shi, ta isa gare shi, ya kai hannu zai taba ta ta dan ja baya cikin dabara,