Sashe 6
Idan Ba Ke Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Commissioners Quarter's
Haɗaɗɗiyyar unguwa ce wacce take cikin Jimeta, iya haɗuwa da tsari unguwar tayi, wanda bai saba fita kasashen waje ba idan ya shiga Commissioners Quarter's zaka ɗauka a ƙasar turawa kake. Gidajene duguwa zaka gansu kamar tangaran sbd yadda suka haɗu aka zuba dukiya. Unguwa ce ya masu kuɗi wanda talaka sam bai isa ya shige ta ba. Unguwannin masu ci da gindin biro kenan.
A hankali take sakkowa daga kan strains ɗin benan hannunta riƙe da waya tana latsawa, jikinta sanye da wani Short pencil jeans sai Balenciaga top a saman t.shirt ɗin jikinta. Ƙafarta cikin wani Hermes slippers. "Binta! Binta!!" Ta shiga kiran maid ɗin dake yi musu abinci tana zama saman Kujera, jinin Binta na rawa ta ƙaraso tana zubewa a gaban Zahrah ta ce "Hajiya gani" harara ta watsa mata cikin rashin ko ina kula ta ce "Kin san ban son buɗe murya sbd kawai zan kiraki?" Binta wacce a ƙalla zata iya yin shekaru 55 zasu iya kusan sa a da mahaifiyar Zahrah ta sunkuyar da kanta ƙasa cike da girmamawa ta ce "Afuwa Hajiya, ina can ina duba time table na list ɗin abincinki na me za a dafa miki zuwa dare" shiru Zahrah tai ba tare data ƙara cewa Binta komai ba, hankalinta yana kan wani abu da take searching akai, ita dai da karatun boko na yin magana a jikin mutum da tuni ya jima dayi a jikin Zahrah domin kaf gidan tafi kowa zurfi karatun boko shi ya sa take taka kowa hankali kwance. "Hajiya me kike buƙata?" Binta ta tambaya. Idanunta ta ɗaga ta kalli Binta a hankali taja tsaki ta ce "Nikam Binta na tambayeki?" "Ina jinki Hajiya" Zahrah ta gyara zama sosai tana ajjiye wayar hannunta a gefe kafin ta ce "Wai yaushe za kiyi hankali ki fahimci abin da nake buƙata, matsalar rashin ilimi kenan fa, gaba Binta ƙwaƙwalwarki bata riƙe abu ba lallai ko primary kin cika ba, wallahi na tsani harka da midille class,uneducated, villagers" da tsananin mamaki Binta ke kallon Zahrah ƴar cikinta ke faɗa mata wannan maganganun? "Kiyi haƙuri Hajiya" a fusace Zahrah ta ce "Sorry for yourself Binta, kije ki haɗa mini salad ki saka lemon sosai ciki" Binta ta jinjina kai tana Miƙewa tsaye tare da barin wajan idanunta cike da hawayen baƙin ciki. Wata mata wacce ta fito cikin parlourn ta kalli Zahrah ta ce "Why are you shouting?" Murmushi Zahrah tai ta ce "No Mimi ina game ne, akai mini game over" Zama Mimi tai ta ce "Ok, kwana biyu na jin labarin Deen a bakinki? Lafiya dai?" Zahrah ta ce "Baya nan ne Mimi" Mimi ta ce "Ai fa, naga idan yazo sai ku kai awa uku zuwa huɗu a part ɗinki kwana biyu shiru" Murmushi kawai Zahrah a haka Binta ta kawo mata haɗin salad ɗin. Mimi tabi Zahrah da kallo kafin ta ce "Wai lafiyarki ƙalou kuwa? Kullum cikin cin haɗin Salad kike?" "Lafiya Mimi, kawai zuwa makarantar nan ke sani gajiya da kwaɗayi naji bana son cin komai" Mimi ta jinjina kai ta ce "Lallai, ni banga me zaki da kuɗi ba da kuka zaɓi lecturing Zahrah" ba tare da data amsa ta ba ta ce "Mimi ina Daddy ne?" Mimi ta ɗauki waya ta ce "Jiya ya dawo, but yaje kano wajan wani babban abokinsa" "Ok" cewar Zahrah a nutse Mimi ta kalli Zahrah cikin damuwa sosai ta ce "Fatima-Zahrah yaushe kike tunanin yin aure ne, boko kin gama ta, completely sai abin da yai saura, familyna sun fara mini surutu akan wai na zuba miki idanu, wasu har cewa suke maybe yawonki kawai ki ke, ni dai nasan ba haka bane i trust you babyna" marairaicewa Zahrah tai kamar ƴar 20 nan kuwa shekaru 31 take da shi. "Mimi kin san familyn nan naki basu san darajar karatun boko ba, ta ya ya zan haɗa karatu da aure? Kana yin auren kuma ace ka haihu, kuma ba zan iya haɗa aikina da aure ba gsky Mimi a barni zuwa 35 na gama komai sai na fara tunanin auren, su kansu mazan ai mai ilimin boko suke buƙata ba kuwa ya damu da ilimin addinin nan ba, suna buƙatar mace wayayyiya a very educated women" murmushi Mimi tai cike da gamsuwa da maganar ƴarta kafin ta ce "Na fahimta, ko Dadynki sai dana kammala University mukai aure muna dai soyayyya a waje, dake kuma na wuri na shiga shcl shi ya sa na gama before we getting married" jinjina kai kawai Zahrah tai hankalinta akan salad ɗin da take ci sbd yadda cikin jikinta ya sanya mata kwaɗayi kala-kala. Da sauri Mimi ta ce "Subuhanallahi, maza kunna mini Plasma ɗin nan ki jonata da DS.TV tafsirin Sheikh sai shigeni" kwaɓe fuska tai kafin ta ce "Mimi wai kin damu da wani Sheikh, ni wallahi ban son tafsirin ɗin ko kaɗan, ga wata ƙinƙina da yake, da ƙyar fa yake iya karatun sbd ƙinƙina wani time ɗin har hawaye yake to me za'a gane?..." Da idanu Mimi tabi Zahrah tana mamakin jikar ƙirjinta a kullum "To ai kuwa da yadda, ƙinƙina kuma ai larura ce kuma a hakan Ubangiji ya ba shi bawai Zahrah".
Gudu take sosai hankali a tashe sai haki take ita kam sam ba zata iya irin wannan wasan na sai da rai ba, wacce ƙaddara ce take shirin bibiyarta ne? Tsayawa tai tana mai da numfashi, sai a lokacin idanunta ya sauka akan wasu fararen Kurciyo masu kyau da tsari ita a rayuwa tana son ko wacce kalar dabba ta daɗe tsaye tana kallonsu, ɗaya daga cikin kurciyoyin ya tsora mata idanu. Tunawa da tai ana gab da fara wasan macijn ya sanya ta ƙara saurayi domin samun wajan ɓoya. Girgiza kurciyoyin sukai wata iska da guguwa ta mamaye ilahirin wajan iskar data kasance mai daɗi sosai wacce ta haddasawa Halisa Dajeno rufe idanunta wani barci na fisgarta a hankali ta sulale a wajan babu jimawa barci mai nauyi ya ɗauketa. Kurciyoyin suka rikiɗe zuwa wasu samari masu zubin halitta ɗaya daga ciki wanda yake sanye da farar Alkyabba mai taushi wacce ta sauka har ƙasa ta rufe masa ƙafafuwansa yaja numfashi a hankali cikin ƙasa da murya ya ce "Danejona ba zata iya wasan nan ba" ɗayan dage gefensa ya ce "Haba Prince me ya sa kake da taurin kai ne? Sarki yace ka yanke duk wata alaƙa tsakaninka da bil-adam musamman wannan yarinyar Danejo amma kaƙi" murmushi mai taushi Wanda aka kira da Prince yai yana sake kallon Halisa Dajeno ya ce "A wannan karan ba zan iya yiwa Sarki biyayya ba, babu haɗi tsakanin mutum da aljani, amma kasan ba zan iya zutar da wani rai ba, muddin idan ba Danejo zai cutar ba? Na jima a jikin mahaifiyar Danejo tun tana da cikinta, amma rana ɗaya akai mata magani suka rabani da ita, wanda ya sanya na kwanta jinya, wannan dalilin yasa na koma kan ɗiyarta Danejo na shirya duk wani abu da sarki zai faɗa, ƙarshe dai ya ce zai koreni daga duniyar Aljanu ba?" Ɗayan zai magana Prince ya daka mishi tsawa ya ce "Ka saurara mini Safwan" ya faɗa idanunsa na juyewa zuwa kalar na aljanu a tsorace Safwan ya ce "Afuwa nake Yariman Aljanu, yanzu me ka shirya akan raba Danejo da wasan macijin nan?" Gyara Tsaiwa Prince yai tare da durƙosawa daidai inda Danejo take kwance tana barci ya ɗauke ta cikin nutsuwa ya ce "Ubangiji nake nema ya bani Sa'a, ina son Matata bana jin zan jure ganinta da duk wani wanda zai cuceta, balle kuma ya taɓa mini ɗana dake cikinta" buɗe baki Safwan yai da Mmki yace "Prince yaushe ta zama matarka? Har kuka samu ɗa?" Murmushi Prince yai yana shafa cikin halinsa wanda yake jin farin ciki na ratsa masa zuciyarsa kafin ya ce "Matata ce ita ɗin, duk wanda ya shirya rabani da ita to ya shirya zuwansa lahira, bani da lokacin magana Safwan, maza ku ɓace daga wajan nan" kamar gilmawar walƙiya haka suka ɓace, nan da nan Prince ya rikiɗe zuwa Almajiri mai yagaggun kaya. A nutse ya fara tafiya da ita zuwa cikin Rugar Rome dai da yaje daidai bakin bukkar su Danejo ya ajjiyeta da sauri ya bar wajan, sbd gaba ɗaya jama'ar Rugar suna filin da za'a gabatar da wasan Maciji. Prince ya ce "Ubangiji ka bani Sa'a da nasara" yana faɗin hakan yai Girgiza nan take ya zama ƙaton wani baƙin maciji mai narkeken kai a hankali ya sulale ya fara tafiya tsakanin bukkokin Rugar Rome har ya Ƙarasa wata bukka kai tsaye ya kutsa kansa ciki, kwance ya samu wani maciji shima baƙine sosai, da alama shi ne macijin da Matarsa Danejo zatai wasa dashi. Kallon kallo aka fara tsakanin Maciji Prince da kuma Macijin da Danejo zatai wasa dashi. Kamar haɗin baki haka suka fasa kai a tare lokaci guda kuma suka nufi kan juna.
🫣Bala'i🚶ðŸ½â€â™€ï¸kada a manta labarin ya faru a gaske babu ragi babu Æ™ari👌ðŸ¾. Muje zuwa
#Sarautar marubuta
#True life story
*🌈 IDAN BA KE 🌈*
Nimcyluv sarauta
_*Arewabooks@Nimcyluv*_
4.
A kusan tare macizan guda biyu suka ƙara fasa kai tare da kaiwa juna sara, ko wanne maciji ƙoƙarin jiwa ɗan uwansa ciwo yake da ganin ya kashesa har lahira. Gaba ɗaya macizan suka sarƙafe juna tare da nan na ɗewa waje guda ko wane huci yake yana fitar da hayaƙi ta baki nisan yadda Prince wanda ya a rikiɗe zuwa maciji ya matse macijin da Za'ai wasa dashi, gaba ɗaya ya ji masa rauni a hankali kuma Prince ya buɗe bakinsa ya fara haɗiye Macijin zuwa cikinsa sai daya haɗiyesa tsaf kafin ya sulale gefe guda ya kwanta yana mai da numfashi Wahala, sai fasa kai yake kamar zaici babu zuciyarsa tayo sama baki ɗaya zai iya sarar ko waye a wannan lokacin.
Haɗaɗɗiyyar unguwa ce wacce take cikin Jimeta, iya haɗuwa da tsari unguwar tayi, wanda bai saba fita kasashen waje ba idan ya shiga Commissioners Quarter's zaka ɗauka a ƙasar turawa kake. Gidajene duguwa zaka gansu kamar tangaran sbd yadda suka haɗu aka zuba dukiya. Unguwa ce ya masu kuɗi wanda talaka sam bai isa ya shige ta ba. Unguwannin masu ci da gindin biro kenan.
A hankali take sakkowa daga kan strains ɗin benan hannunta riƙe da waya tana latsawa, jikinta sanye da wani Short pencil jeans sai Balenciaga top a saman t.shirt ɗin jikinta. Ƙafarta cikin wani Hermes slippers. "Binta! Binta!!" Ta shiga kiran maid ɗin dake yi musu abinci tana zama saman Kujera, jinin Binta na rawa ta ƙaraso tana zubewa a gaban Zahrah ta ce "Hajiya gani" harara ta watsa mata cikin rashin ko ina kula ta ce "Kin san ban son buɗe murya sbd kawai zan kiraki?" Binta wacce a ƙalla zata iya yin shekaru 55 zasu iya kusan sa a da mahaifiyar Zahrah ta sunkuyar da kanta ƙasa cike da girmamawa ta ce "Afuwa Hajiya, ina can ina duba time table na list ɗin abincinki na me za a dafa miki zuwa dare" shiru Zahrah tai ba tare data ƙara cewa Binta komai ba, hankalinta yana kan wani abu da take searching akai, ita dai da karatun boko na yin magana a jikin mutum da tuni ya jima dayi a jikin Zahrah domin kaf gidan tafi kowa zurfi karatun boko shi ya sa take taka kowa hankali kwance. "Hajiya me kike buƙata?" Binta ta tambaya. Idanunta ta ɗaga ta kalli Binta a hankali taja tsaki ta ce "Nikam Binta na tambayeki?" "Ina jinki Hajiya" Zahrah ta gyara zama sosai tana ajjiye wayar hannunta a gefe kafin ta ce "Wai yaushe za kiyi hankali ki fahimci abin da nake buƙata, matsalar rashin ilimi kenan fa, gaba Binta ƙwaƙwalwarki bata riƙe abu ba lallai ko primary kin cika ba, wallahi na tsani harka da midille class,uneducated, villagers" da tsananin mamaki Binta ke kallon Zahrah ƴar cikinta ke faɗa mata wannan maganganun? "Kiyi haƙuri Hajiya" a fusace Zahrah ta ce "Sorry for yourself Binta, kije ki haɗa mini salad ki saka lemon sosai ciki" Binta ta jinjina kai tana Miƙewa tsaye tare da barin wajan idanunta cike da hawayen baƙin ciki. Wata mata wacce ta fito cikin parlourn ta kalli Zahrah ta ce "Why are you shouting?" Murmushi Zahrah tai ta ce "No Mimi ina game ne, akai mini game over" Zama Mimi tai ta ce "Ok, kwana biyu na jin labarin Deen a bakinki? Lafiya dai?" Zahrah ta ce "Baya nan ne Mimi" Mimi ta ce "Ai fa, naga idan yazo sai ku kai awa uku zuwa huɗu a part ɗinki kwana biyu shiru" Murmushi kawai Zahrah a haka Binta ta kawo mata haɗin salad ɗin. Mimi tabi Zahrah da kallo kafin ta ce "Wai lafiyarki ƙalou kuwa? Kullum cikin cin haɗin Salad kike?" "Lafiya Mimi, kawai zuwa makarantar nan ke sani gajiya da kwaɗayi naji bana son cin komai" Mimi ta jinjina kai ta ce "Lallai, ni banga me zaki da kuɗi ba da kuka zaɓi lecturing Zahrah" ba tare da data amsa ta ba ta ce "Mimi ina Daddy ne?" Mimi ta ɗauki waya ta ce "Jiya ya dawo, but yaje kano wajan wani babban abokinsa" "Ok" cewar Zahrah a nutse Mimi ta kalli Zahrah cikin damuwa sosai ta ce "Fatima-Zahrah yaushe kike tunanin yin aure ne, boko kin gama ta, completely sai abin da yai saura, familyna sun fara mini surutu akan wai na zuba miki idanu, wasu har cewa suke maybe yawonki kawai ki ke, ni dai nasan ba haka bane i trust you babyna" marairaicewa Zahrah tai kamar ƴar 20 nan kuwa shekaru 31 take da shi. "Mimi kin san familyn nan naki basu san darajar karatun boko ba, ta ya ya zan haɗa karatu da aure? Kana yin auren kuma ace ka haihu, kuma ba zan iya haɗa aikina da aure ba gsky Mimi a barni zuwa 35 na gama komai sai na fara tunanin auren, su kansu mazan ai mai ilimin boko suke buƙata ba kuwa ya damu da ilimin addinin nan ba, suna buƙatar mace wayayyiya a very educated women" murmushi Mimi tai cike da gamsuwa da maganar ƴarta kafin ta ce "Na fahimta, ko Dadynki sai dana kammala University mukai aure muna dai soyayyya a waje, dake kuma na wuri na shiga shcl shi ya sa na gama before we getting married" jinjina kai kawai Zahrah tai hankalinta akan salad ɗin da take ci sbd yadda cikin jikinta ya sanya mata kwaɗayi kala-kala. Da sauri Mimi ta ce "Subuhanallahi, maza kunna mini Plasma ɗin nan ki jonata da DS.TV tafsirin Sheikh sai shigeni" kwaɓe fuska tai kafin ta ce "Mimi wai kin damu da wani Sheikh, ni wallahi ban son tafsirin ɗin ko kaɗan, ga wata ƙinƙina da yake, da ƙyar fa yake iya karatun sbd ƙinƙina wani time ɗin har hawaye yake to me za'a gane?..." Da idanu Mimi tabi Zahrah tana mamakin jikar ƙirjinta a kullum "To ai kuwa da yadda, ƙinƙina kuma ai larura ce kuma a hakan Ubangiji ya ba shi bawai Zahrah".
Gudu take sosai hankali a tashe sai haki take ita kam sam ba zata iya irin wannan wasan na sai da rai ba, wacce ƙaddara ce take shirin bibiyarta ne? Tsayawa tai tana mai da numfashi, sai a lokacin idanunta ya sauka akan wasu fararen Kurciyo masu kyau da tsari ita a rayuwa tana son ko wacce kalar dabba ta daɗe tsaye tana kallonsu, ɗaya daga cikin kurciyoyin ya tsora mata idanu. Tunawa da tai ana gab da fara wasan macijn ya sanya ta ƙara saurayi domin samun wajan ɓoya. Girgiza kurciyoyin sukai wata iska da guguwa ta mamaye ilahirin wajan iskar data kasance mai daɗi sosai wacce ta haddasawa Halisa Dajeno rufe idanunta wani barci na fisgarta a hankali ta sulale a wajan babu jimawa barci mai nauyi ya ɗauketa. Kurciyoyin suka rikiɗe zuwa wasu samari masu zubin halitta ɗaya daga ciki wanda yake sanye da farar Alkyabba mai taushi wacce ta sauka har ƙasa ta rufe masa ƙafafuwansa yaja numfashi a hankali cikin ƙasa da murya ya ce "Danejona ba zata iya wasan nan ba" ɗayan dage gefensa ya ce "Haba Prince me ya sa kake da taurin kai ne? Sarki yace ka yanke duk wata alaƙa tsakaninka da bil-adam musamman wannan yarinyar Danejo amma kaƙi" murmushi mai taushi Wanda aka kira da Prince yai yana sake kallon Halisa Dajeno ya ce "A wannan karan ba zan iya yiwa Sarki biyayya ba, babu haɗi tsakanin mutum da aljani, amma kasan ba zan iya zutar da wani rai ba, muddin idan ba Danejo zai cutar ba? Na jima a jikin mahaifiyar Danejo tun tana da cikinta, amma rana ɗaya akai mata magani suka rabani da ita, wanda ya sanya na kwanta jinya, wannan dalilin yasa na koma kan ɗiyarta Danejo na shirya duk wani abu da sarki zai faɗa, ƙarshe dai ya ce zai koreni daga duniyar Aljanu ba?" Ɗayan zai magana Prince ya daka mishi tsawa ya ce "Ka saurara mini Safwan" ya faɗa idanunsa na juyewa zuwa kalar na aljanu a tsorace Safwan ya ce "Afuwa nake Yariman Aljanu, yanzu me ka shirya akan raba Danejo da wasan macijin nan?" Gyara Tsaiwa Prince yai tare da durƙosawa daidai inda Danejo take kwance tana barci ya ɗauke ta cikin nutsuwa ya ce "Ubangiji nake nema ya bani Sa'a, ina son Matata bana jin zan jure ganinta da duk wani wanda zai cuceta, balle kuma ya taɓa mini ɗana dake cikinta" buɗe baki Safwan yai da Mmki yace "Prince yaushe ta zama matarka? Har kuka samu ɗa?" Murmushi Prince yai yana shafa cikin halinsa wanda yake jin farin ciki na ratsa masa zuciyarsa kafin ya ce "Matata ce ita ɗin, duk wanda ya shirya rabani da ita to ya shirya zuwansa lahira, bani da lokacin magana Safwan, maza ku ɓace daga wajan nan" kamar gilmawar walƙiya haka suka ɓace, nan da nan Prince ya rikiɗe zuwa Almajiri mai yagaggun kaya. A nutse ya fara tafiya da ita zuwa cikin Rugar Rome dai da yaje daidai bakin bukkar su Danejo ya ajjiyeta da sauri ya bar wajan, sbd gaba ɗaya jama'ar Rugar suna filin da za'a gabatar da wasan Maciji. Prince ya ce "Ubangiji ka bani Sa'a da nasara" yana faɗin hakan yai Girgiza nan take ya zama ƙaton wani baƙin maciji mai narkeken kai a hankali ya sulale ya fara tafiya tsakanin bukkokin Rugar Rome har ya Ƙarasa wata bukka kai tsaye ya kutsa kansa ciki, kwance ya samu wani maciji shima baƙine sosai, da alama shi ne macijin da Matarsa Danejo zatai wasa dashi. Kallon kallo aka fara tsakanin Maciji Prince da kuma Macijin da Danejo zatai wasa dashi. Kamar haɗin baki haka suka fasa kai a tare lokaci guda kuma suka nufi kan juna.
🫣Bala'i🚶ðŸ½â€â™€ï¸kada a manta labarin ya faru a gaske babu ragi babu Æ™ari👌ðŸ¾. Muje zuwa
#Sarautar marubuta
#True life story
*🌈 IDAN BA KE 🌈*
Nimcyluv sarauta
_*Arewabooks@Nimcyluv*_
4.
A kusan tare macizan guda biyu suka ƙara fasa kai tare da kaiwa juna sara, ko wanne maciji ƙoƙarin jiwa ɗan uwansa ciwo yake da ganin ya kashesa har lahira. Gaba ɗaya macizan suka sarƙafe juna tare da nan na ɗewa waje guda ko wane huci yake yana fitar da hayaƙi ta baki nisan yadda Prince wanda ya a rikiɗe zuwa maciji ya matse macijin da Za'ai wasa dashi, gaba ɗaya ya ji masa rauni a hankali kuma Prince ya buɗe bakinsa ya fara haɗiye Macijin zuwa cikinsa sai daya haɗiyesa tsaf kafin ya sulale gefe guda ya kwanta yana mai da numfashi Wahala, sai fasa kai yake kamar zaici babu zuciyarsa tayo sama baki ɗaya zai iya sarar ko waye a wannan lokacin.