Sashe 24
Idan Ba Ke Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Misalin 10:23 Abba Hakimi na zaune a Main parlour dashi da Momi kamar daga sama su kaga Sheikh ya shigo hannunsa guda ɗaya dafe da kansa, Momi zatai magana Abba Hakimi ya Girgiza mata kai alamar tai shiru,babu wanda ya kula ya shige part ɗinsa dake gidan, kai tsaye bathroom ya nufa bayan ya zame kayan jikinsa abin da bai taɓa yi ba shi ne, amfani da ruwan sanyi ya tsaya a shower na sauka akansa sanyi na ratsa masa tsakiyar kansa, sai numfashi yake fitarwa dan kansa ya kashe shower ɗin ya naɗe jikinsa a cikin wata bathroom mai ɗan kauri, idanunsa na rufewa sbd azababban ciwon kai a haka ya kwanta saman gado ya daɗe kafin barci ya ɗauke sa.
"Lafiyar Sheikh ɗaya kuwa?" Abba Hakimi ya ce "Kinga alamar bai da lafiya ne?" Momi ta ce "A'a, kawai yadda na shigo gidan ne" Apple ɗin hannunta da take miƙa masa ya amsa ya ce "Kada ki damu, duk sanda ya yi haka alheri ne ke bibiyarsa" tattaunawa sukai akan gobe za a kai kayan lefen na Sheikh ita ma zata a hankali ya ce "Allah ya kaimu" sai kusan 12 na dare Sannan Saif-wazir ya shigo ganin dare ya yi kai tsaye ya nufi part ɗinsa, motar Sheikh da ya gani ya bashi tabbacin ya dawo gida. Da batun Auren Sheikh ya kwana yana tunanin ya faɗawa Abba Hakimi ko ya yi shiru? Har barci ya ɗauke shi ba samu mafita ba.
Washegari da yamma wajan 5. Dr A'isha ta zabga tagumi Yaya Halima ta ce "Dr wai lafiya tun da muka dawo kike wata kala?" Dr A'isha ta ce "Wallahi Yaya tausayin Sheikh nake, ina zai kai wannan uwar matar? Na girgiza ban san rashin tarbiyyar ta ya kai haka ba, kalli da ita aka amshi kayan lefen fa?" Yaya Halima ta kalli Dr A'isha tana mmkin rashin control na bakinta da bata iya riƙe zance. "Kowa da tsarinsa fa Dr Allah dai ya sanya albarka" daga bakin ƙofa akace "Ba Amin ba, mugun ji da mugun gani ruɓaɓɓan baki ya kau daga kan Gadanga, yau ko ni ko uban Gadanga ya zaɓa" gaba ɗaya suka kalli bakin ƙofa, tana tsaye taci lace ɗauri har gaban goshi ta lafta uban Glasses a fuska wanda ya cinye rabin fuska. Cikin farin ciki Mother ta miƙe tsaye tana faɗin "Jadda" haɗe fuska tayi ta nemi waje ta zauna, Uncle Haroon ya shigo hannunsa riƙe da torelly ɗin Jadda ya zauna kusa da ita. Cikin farin ciki Mother ta ƙara cewa "Sannu da hanya Jadda ashe kina tafe" Jadda ta ɗauke kai sai da Mother tabar wajan, ta juya ta kalli Uncle Haroon murya can ƙasa ta ce. "Munafuka Algunguma duk masifa da yaƙin da ake a gidan fa bata sanar dani ba, shi ya sa na haɗe mata fuska na kame kai na, ba kaga jikinta ya yi sanyi ba, ai wlh yau sai sun bala'i ya sauka" murmushi kawai Uncle Haroon ya yi ta haɗe rai tana ƙanƙantar da idanu ta ce "Kaji masifa ko? Ba murmushi za kai ba cewa zakai nayi daidai" ya ƙara murmushi ya ce "Jadda duk abin da ki kai ai daidai ne" cikin ƙaramin lokaci Mother ta cika gaban Jadda da kaya kala-kala, Yaya Halima da Dr A'isha suka gaidata ta amsa a ciki. "Kinga ba kwaɗayi ya kawo ni ba, maza kira mini mijin naki" Mother ta haura sama yana zaune yana duba Invitation ɗin bikin Sheikh dana Zahrah Mother ta shiga a hankali ya ce "Barrister ya dai?" Kai tsaye ta ce "Jadda na kira" tana faɗin hakan ta juya, yabi bayanta da kallo da sauri kuma ya miƙe shima. A hankali yake sakkowa daga benen yana sakin fuska bayan ya zauna ya ce "Sannu da zuwa Jadda" banza Jadda tayi masa, ta zare Glasses ɗin idanunta ta miƙawa Uncle Haroon, ta cire mayafi shima ta miƙawa Uncle Haroon, fuskar Father cike da tsoro ya ce "Jadda lafiya me kike shirin yi haka?" Bata kula shi ba, ta buɗe rigarta tana nunawa father ta ce "mene wannan?" Kansa a ƙasa ya kasa cewa komai ta ce "Idan ba zaka iya ba, ai Ubangiji ya tsaga mini bakin magana nonon dana shayar da kai ne, kasan Allah tun nonon yana kwance ka lalata batun auren Gadanga da wannan gantalalliyar yarinyar, idan ba haka ba zan ɗaga maka nonon sama ka lalace kaje duk inda zaka...
*Not edited*
Masu tambayar yadda zasu biya kuɗin IDAN BA KE. Book 1, 2 ne. Mutum zai biya ₦500 har a gama littafin baki ɗaya. 6850917335 Na'ima Shu'aibu sulaiman fidelity bank. A tura shaidar biya ta nan 08119237616.
*🌈IDAN BA KE 🌈*
*_Nimcyluv Sarauta_*
16....
*I am proud of my fans wherever they are, nayi mamakin yadda kuka amshi littafin IDAN BA KE fiye da ZAIN-ABEED. Masoya TSINTACCIYA, MOON, UNCLE NE duk ba a barku a baya ba🥰💋for the first time zanyi rubutu akan labarin zanan Æ™addarar soyayya zallah🫰ðŸ¿a shirya a gyara zama sosai yanzu aka fara...*
#TEAM SHEIKH ALIYU HAYDAR ALIYU
#TEAM HALISA DANEJO ROME
#TEAM EL-BASHIR AHMAD SARKI
#TEAM ZAHRAH FAROUK
Jadda ta ƙara cewa "Kalle ni da kyau uwarka ce Jadda, Wallahi nono zan ɗaga maka kawai kabi duniya kaje duk inda zaka Aliyu tunda ka gagara, idan ya so ana nunaka da baki ana cewa gashi can uwar shi tai masa baki ta ɗaga masa nono shi ya sa yake ta galantuyi a duniya, duk wanda bai yarda ba, ni nai maka baki ba zaka iya kawo shi wajena na tabbatar masa" zufa ta dinga yankowa Father a hankali ya zame daga kan kujera zuwa inda take ya ce "Jadda don girman Allah kada kice haka, ki tsaya ki fahimci al'amarin nan I have a reason why I want Sheikh to get married with Zahrah." Uncle Haroon ya ce "Mene dalilin naka? Uwar yaron nan bata so, I don't agree either" Jadda dai kaɗa ƙafa take har lokacin tana riƙe da ƙirjinta cikin rarrashi Father ya ce "Jadda don ki fahimce ni Sheikh ba zai iya kula da dukkan al'amarin daya shafi kasuwancina da dukiyata ba, kullum ƙarfina ƙasa yake abubuwa na neman yi mini yawa, na bashi dama yafi sau goma akan ya kawo matar da zai aura amma yaƙi, Umar-khan yace tunda Sheikh yake magana bata taɓa haɗa shi da wata mace ba, kalli sharrin da akai masa tun daga jami'ar Madina, da ace yana da aure babu mai binsa da wannan sharrin shi ya sa na yanke hukuncin aura masa ƴar aminina tasan kan business sosai zata janye hankali Sheikh ɗin zuwa kasuwancin, Jadda ina son Sheikh Aliyu ban taɓa son wani abu kamar shi ba, kiyi mini uzuri ayi auren nan idan yarinyar ba tai miki ba sai ki ɗauki mataki" Mother ta girgiza kai cike da takaicin yadda Father yake tsara zan ce. "Aini duk bani da labarin haka, jiya jiya labari ya saman ana ta yaƙi a gidan naka, kuma yarinyar ƴar iska ce" Father ya kalli Jadda da kyau ya juya ya kalli Mother yana faɗin "ke kika faɗa mata Zahrah ƴar iska ce sbd ba ƴarki bace shi ya sa zaki ai bata musu ƴa?" Rai ɓace Mother ta ce "Ni na faɗa Engineer tunda haka zuciyarka ta shaida maka, kaga yaushe rabon da naje wajanka akan maganar Aliyu ko auren? Aje ayi aure lafiya nima zan zaɓawa Sheikh yarinyar da nayi niyya na aura masa ita" tana faɗin haka ta miƙe tare da nufar upstairs zuciyarta cike da tarin baƙin ciki. Baki buɗe Jadda ke kallon kowa kafin ta ce "Na amince ayi auren kuma na amince Maryam ta zaɓawa Gadanga yarinyar da duk tai niyya" Father ya ce "Amma Jadda daka aura masa Zahrah sai ya yi mata kishiya? Ba ai mata adalci ba" Jadda ta miƙe tsaye tana ƙanƙance idanu ta ce "Wai wacce ƙaniyar ce Zarra ko me? Ba ita ba ko uwarta ka aurawa Gadanga kwaranƙwasa sai anyi mata kishiya, Allah dai ya nuna mini ƴar banzar yarinyar da idanu naga abin da bai mini ba, maza ɓace mini da gani ko mene haɗina da kai dana tsaya shiga sabgar ka" Father ya miƙe tare da barin wajan yana faɗin "A huta lafiya Jadda" sai da yabar wajan Jadda ta sauke numfashi tana raɗawa Uncle Haroon ta ce "Ba gashi ba anyi sulhu komai ya lafa daman duk iskancin mutum ina zuwa shikenan, ai Alsulhu khair" murmushi kawai Uncle Haroon ya yi yana cewa sai Anjima zai dawo.
Sai a lokacin Jadda ta lura da Yaya Halima da kuma Dr A'isha kowa yana danna waya abinsa kasancewarsu masu ilimi da dukiya ya sanya suka kame kansu basu saka baki cikin abin da babu ruwansu ba.
"Lafiyar Sheikh ɗaya kuwa?" Abba Hakimi ya ce "Kinga alamar bai da lafiya ne?" Momi ta ce "A'a, kawai yadda na shigo gidan ne" Apple ɗin hannunta da take miƙa masa ya amsa ya ce "Kada ki damu, duk sanda ya yi haka alheri ne ke bibiyarsa" tattaunawa sukai akan gobe za a kai kayan lefen na Sheikh ita ma zata a hankali ya ce "Allah ya kaimu" sai kusan 12 na dare Sannan Saif-wazir ya shigo ganin dare ya yi kai tsaye ya nufi part ɗinsa, motar Sheikh da ya gani ya bashi tabbacin ya dawo gida. Da batun Auren Sheikh ya kwana yana tunanin ya faɗawa Abba Hakimi ko ya yi shiru? Har barci ya ɗauke shi ba samu mafita ba.
Washegari da yamma wajan 5. Dr A'isha ta zabga tagumi Yaya Halima ta ce "Dr wai lafiya tun da muka dawo kike wata kala?" Dr A'isha ta ce "Wallahi Yaya tausayin Sheikh nake, ina zai kai wannan uwar matar? Na girgiza ban san rashin tarbiyyar ta ya kai haka ba, kalli da ita aka amshi kayan lefen fa?" Yaya Halima ta kalli Dr A'isha tana mmkin rashin control na bakinta da bata iya riƙe zance. "Kowa da tsarinsa fa Dr Allah dai ya sanya albarka" daga bakin ƙofa akace "Ba Amin ba, mugun ji da mugun gani ruɓaɓɓan baki ya kau daga kan Gadanga, yau ko ni ko uban Gadanga ya zaɓa" gaba ɗaya suka kalli bakin ƙofa, tana tsaye taci lace ɗauri har gaban goshi ta lafta uban Glasses a fuska wanda ya cinye rabin fuska. Cikin farin ciki Mother ta miƙe tsaye tana faɗin "Jadda" haɗe fuska tayi ta nemi waje ta zauna, Uncle Haroon ya shigo hannunsa riƙe da torelly ɗin Jadda ya zauna kusa da ita. Cikin farin ciki Mother ta ƙara cewa "Sannu da hanya Jadda ashe kina tafe" Jadda ta ɗauke kai sai da Mother tabar wajan, ta juya ta kalli Uncle Haroon murya can ƙasa ta ce. "Munafuka Algunguma duk masifa da yaƙin da ake a gidan fa bata sanar dani ba, shi ya sa na haɗe mata fuska na kame kai na, ba kaga jikinta ya yi sanyi ba, ai wlh yau sai sun bala'i ya sauka" murmushi kawai Uncle Haroon ya yi ta haɗe rai tana ƙanƙantar da idanu ta ce "Kaji masifa ko? Ba murmushi za kai ba cewa zakai nayi daidai" ya ƙara murmushi ya ce "Jadda duk abin da ki kai ai daidai ne" cikin ƙaramin lokaci Mother ta cika gaban Jadda da kaya kala-kala, Yaya Halima da Dr A'isha suka gaidata ta amsa a ciki. "Kinga ba kwaɗayi ya kawo ni ba, maza kira mini mijin naki" Mother ta haura sama yana zaune yana duba Invitation ɗin bikin Sheikh dana Zahrah Mother ta shiga a hankali ya ce "Barrister ya dai?" Kai tsaye ta ce "Jadda na kira" tana faɗin hakan ta juya, yabi bayanta da kallo da sauri kuma ya miƙe shima. A hankali yake sakkowa daga benen yana sakin fuska bayan ya zauna ya ce "Sannu da zuwa Jadda" banza Jadda tayi masa, ta zare Glasses ɗin idanunta ta miƙawa Uncle Haroon, ta cire mayafi shima ta miƙawa Uncle Haroon, fuskar Father cike da tsoro ya ce "Jadda lafiya me kike shirin yi haka?" Bata kula shi ba, ta buɗe rigarta tana nunawa father ta ce "mene wannan?" Kansa a ƙasa ya kasa cewa komai ta ce "Idan ba zaka iya ba, ai Ubangiji ya tsaga mini bakin magana nonon dana shayar da kai ne, kasan Allah tun nonon yana kwance ka lalata batun auren Gadanga da wannan gantalalliyar yarinyar, idan ba haka ba zan ɗaga maka nonon sama ka lalace kaje duk inda zaka...
*Not edited*
Masu tambayar yadda zasu biya kuɗin IDAN BA KE. Book 1, 2 ne. Mutum zai biya ₦500 har a gama littafin baki ɗaya. 6850917335 Na'ima Shu'aibu sulaiman fidelity bank. A tura shaidar biya ta nan 08119237616.
*🌈IDAN BA KE 🌈*
*_Nimcyluv Sarauta_*
16....
*I am proud of my fans wherever they are, nayi mamakin yadda kuka amshi littafin IDAN BA KE fiye da ZAIN-ABEED. Masoya TSINTACCIYA, MOON, UNCLE NE duk ba a barku a baya ba🥰💋for the first time zanyi rubutu akan labarin zanan Æ™addarar soyayya zallah🫰ðŸ¿a shirya a gyara zama sosai yanzu aka fara...*
#TEAM SHEIKH ALIYU HAYDAR ALIYU
#TEAM HALISA DANEJO ROME
#TEAM EL-BASHIR AHMAD SARKI
#TEAM ZAHRAH FAROUK
Jadda ta ƙara cewa "Kalle ni da kyau uwarka ce Jadda, Wallahi nono zan ɗaga maka kawai kabi duniya kaje duk inda zaka Aliyu tunda ka gagara, idan ya so ana nunaka da baki ana cewa gashi can uwar shi tai masa baki ta ɗaga masa nono shi ya sa yake ta galantuyi a duniya, duk wanda bai yarda ba, ni nai maka baki ba zaka iya kawo shi wajena na tabbatar masa" zufa ta dinga yankowa Father a hankali ya zame daga kan kujera zuwa inda take ya ce "Jadda don girman Allah kada kice haka, ki tsaya ki fahimci al'amarin nan I have a reason why I want Sheikh to get married with Zahrah." Uncle Haroon ya ce "Mene dalilin naka? Uwar yaron nan bata so, I don't agree either" Jadda dai kaɗa ƙafa take har lokacin tana riƙe da ƙirjinta cikin rarrashi Father ya ce "Jadda don ki fahimce ni Sheikh ba zai iya kula da dukkan al'amarin daya shafi kasuwancina da dukiyata ba, kullum ƙarfina ƙasa yake abubuwa na neman yi mini yawa, na bashi dama yafi sau goma akan ya kawo matar da zai aura amma yaƙi, Umar-khan yace tunda Sheikh yake magana bata taɓa haɗa shi da wata mace ba, kalli sharrin da akai masa tun daga jami'ar Madina, da ace yana da aure babu mai binsa da wannan sharrin shi ya sa na yanke hukuncin aura masa ƴar aminina tasan kan business sosai zata janye hankali Sheikh ɗin zuwa kasuwancin, Jadda ina son Sheikh Aliyu ban taɓa son wani abu kamar shi ba, kiyi mini uzuri ayi auren nan idan yarinyar ba tai miki ba sai ki ɗauki mataki" Mother ta girgiza kai cike da takaicin yadda Father yake tsara zan ce. "Aini duk bani da labarin haka, jiya jiya labari ya saman ana ta yaƙi a gidan naka, kuma yarinyar ƴar iska ce" Father ya kalli Jadda da kyau ya juya ya kalli Mother yana faɗin "ke kika faɗa mata Zahrah ƴar iska ce sbd ba ƴarki bace shi ya sa zaki ai bata musu ƴa?" Rai ɓace Mother ta ce "Ni na faɗa Engineer tunda haka zuciyarka ta shaida maka, kaga yaushe rabon da naje wajanka akan maganar Aliyu ko auren? Aje ayi aure lafiya nima zan zaɓawa Sheikh yarinyar da nayi niyya na aura masa ita" tana faɗin haka ta miƙe tare da nufar upstairs zuciyarta cike da tarin baƙin ciki. Baki buɗe Jadda ke kallon kowa kafin ta ce "Na amince ayi auren kuma na amince Maryam ta zaɓawa Gadanga yarinyar da duk tai niyya" Father ya ce "Amma Jadda daka aura masa Zahrah sai ya yi mata kishiya? Ba ai mata adalci ba" Jadda ta miƙe tsaye tana ƙanƙance idanu ta ce "Wai wacce ƙaniyar ce Zarra ko me? Ba ita ba ko uwarta ka aurawa Gadanga kwaranƙwasa sai anyi mata kishiya, Allah dai ya nuna mini ƴar banzar yarinyar da idanu naga abin da bai mini ba, maza ɓace mini da gani ko mene haɗina da kai dana tsaya shiga sabgar ka" Father ya miƙe tare da barin wajan yana faɗin "A huta lafiya Jadda" sai da yabar wajan Jadda ta sauke numfashi tana raɗawa Uncle Haroon ta ce "Ba gashi ba anyi sulhu komai ya lafa daman duk iskancin mutum ina zuwa shikenan, ai Alsulhu khair" murmushi kawai Uncle Haroon ya yi yana cewa sai Anjima zai dawo.
Sai a lokacin Jadda ta lura da Yaya Halima da kuma Dr A'isha kowa yana danna waya abinsa kasancewarsu masu ilimi da dukiya ya sanya suka kame kansu basu saka baki cikin abin da babu ruwansu ba.