Sashe 13
Idan Ba Ke Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Na samu Information É—in hakan, amma idan an kawo gidan sauron, asibitin nan za a Ajjiye mu zamu raba, so za a bawa Kowa akan 1500 each one" waro ido waje Dr Iliya ya yi kafin ya ce "baka ganin zamu iya samun matsala, tunda kyauta gwamnati ta bayar?" ÆŠaga hannu Dr Hamza ya yi yana dakatar da Dr Iliya da faÉ—in "Hakan shi ne ribarmu, ba za mu yi musu bauta ba kamar wasu bayi, they have to pay"
Kafin Iliya ya yi magana Hamma Yabi ya faɗo office ɗin da sauri cikin tsawa Dr Hamza ya ce "Malam ya haka zaka faɗo kamar wani mahaukaci? Me ya sa duk fulanin nan baku da ilimin zaman rayuwa ne, baku san yadda ake mu'amala ba?" Hamma baya gane zancan nasu ya ce "Don Allah ka taimaki Dadarmu, kada ta mutu cikin wannan halin ita kaɗai ta rage mana, sau wajan goma ina zuwa" "Idan munje kanta lafiya zamu bata kenan? Ko zamu hanata mutuwa? Zan maka last warning Kada na sake ganin ƙafarka cikin asibitin nan, na faɗa maka bamu da maganin ko ɗaya me kake so nayi maka? Haba kuna yi mana adalci mu likitoci sai an bimu a hankali mai ya sa zan zuciyarku ya yi yawa ne?" kasa magana Hamma yai sbd Hawayen daya cika masa idanu me ya sa su Fulani ake musu kallon mahaukata wanda basu san me suke ba? Akwai wani bambanci a jikinsu wanda ya bambanta su da sauran jama'a ne? Juyawa ya yi yana zuriyarsa babu daɗi. Danejo na ganinsa ta ce "Hamma ya naga ka daɗe, numfashi Dadata zai gudu ka taimaka, ina masu bada lafiya ɗin?" A hankali ya kama hannunta ya riƙe yana shafa kanta dake ɗauke da suma mai kyau can ƙasa ya ce "Muje gida, ba zamu ƙara zuwa asibitin nan ba, Allah ya a bamu Kuɗi mu kaita asibitin burni" shiru kawai tayi tana kallonsa tare da son fahimtar abin da yake nufi a haka suka koma gida jiki babu daɗi, kwana sukai ba su yi bacci ba, Shatu kawai ta runsta sbd ƙarancin shekarunta. A daren Danejo ta sanyawa ranta zata sai da nono iya iyawarta ta tara kuɗi masu yawa akai Dada asibiti. Hakan yasa ta tashi da asuba ta tatsi kindirmo a ƙwayar gari na fara haske ta nufi cikin burni wajan Abti America.
Mother ce ke sakkowa daga upstairs kunnanta maƙale da waya idanunta sanye cikin farin glasses ta fito a Barrister Maryam ɗinta sak. A hankali ta ce "Na riga nayi reporting case ɗin, idan ba a samu good evedance ba akan wanda suka kawo ƙarar Aliyuna, kai tsaye zan maka ko wacce ƴar banza a court dama kawai nake jira" daga cikin wayar aka ja numfashi tace "Barrister Maryam kasa aje court,idan akaje to kin bawa duniya damar zata fahimci halin da ake ciki,abi komai a sannu" ɓayayyiyar ajjiyar zuciya Mother ta sauke idanunta na sauka akan Zeefa da Fattoumah "Ok za mu yi magana bari naje wajansa Allah ya sa ya yi magana, al'amarin Sheikh na bani tsoro yana bani mamaki" ƙara tattaunawa sukai kafin sukai sallama. "sannu da sakkowa mother" idanunta akan Plasma ɗin da suke kallo ta ce "Fattoumah sau nawa zan ce bana son kuna kallon zee world ne? Ashe ban isa daku ba ko?" A sanyaye Fattoumah ta ce "We're sorry Mother ba zamu sake ba" zama tayi ta ce "Change the channel immediately Mamana" Sauya channel Fattoumah ta yi zuwa Aljazeera tana faɗin "Ok Mother" kallonsu ta yi sosai ta ce "Where's Maimoon and Auta?" Zeefa ta bata amsa da "She's inside the kitchen, Auta barci take" Mother ta ce "Bana son barcin yamma taso mini ita" tana faɗin ta miƙe tare da nufar kitchen daga bakin ƙofa ta tsaya tana kallon Maimoon dake haɗa coffee ta ce "Ina Lunch ɗin Sheikh?"... "Gashi a tray mother bari na kai masa" tsareta tayi da idanu ta ce "Bani nan" tray ɗin lunch ta bawa Mother tana ci-gaba da aikin gabanta.
Haɗaɗɗan part ɗinsa ta nufa tun daga nesa ƙirar arar Sheikh Muhammad didat ta ratsa cikin kunnuwanta da Mmkin fal fuskar Mother ganin ƙofar shiga parlournsa a buɗe. Ƙamshin air-cod ya ratsa cikin hancinta. Tana shiga idanunta ya sauka akan Umar-khan dake zaune gabansa ɗauke da system yana duba wani abu, ganin Mother ya sa Umar-khan saurin miƙewa tsaye ya ce "Sannu da zuwa Mother" "Yawwa Umar-khan ina Aliyun?" Hanyar da zata sadaka da bedroom ɗin Sheikh ya kalla yana faɗin "a Parlour na samesa lokacin da nazo, ina fara yi masa magana akan wannan case ɗin ya tashi ya shige bedroom har yanzu bai fito ba" jinjina kai tayi ta nufi bedroom ɗin, babu abin da bedroom ɗin yake sai ƙamshin turarensa ROJA wanda ya a jima da kama ɗakin duk da cewa bai fiye rayuwa a cikin gidan iyayen nasa ba, yafi rayuwa a Madina idan yana ƙasa Nigeria kuma yafi rayuwa a gidan Hakimi. ba kowa nan ma a bedroom ɗin sai tsarin ɗakin da Mother tabi da kallo wanda a kullum yake Sauya mata, komai na ɗakin fari ne tas, ɓangaren clothes, shoes, perfumes. Komai daban yake. Juyawa tayi zuwa parlourn tana faɗin "Umar-khan Aliyu baya nan fa? Ko dai ya tafi gidan Hakimi?" Umar-khan yai shiru ya ce "Bashi da ikon fita, kamar kullum ƴan jaridu na waje ta ko'ina maybe yana Library ɗinsa" sai a lokacin ta tuna da Library tana zuwa ciki ta samesa zaune akan wata ƙyakkyawar kujera wacce take juya kanta da kanta ya rufe idanunsa, sumar kansa ta ɗan bayyana sbd yanayin naɗin rawanin nasa wanda ya yi da farin hirami. Hannunsa harɗe a ƙirji. Zama tayi kujerar dake kusa dashi tana kama hannunsa ta ce "Abbana Babana" ajjiyar zuciya Sheikh Aliyu Haydar ya sauke sbd jin sunan da Mother's ta kirasa da shi amma ya kasa buɗe idanunshi domin baya son ta fahimci halin da idanunsa ke ciki wanda sune kaɗai suke fallasa raunin zuciyarsa. "Buɗe idanunka mu yi magana Babana, ba zan taɓa bari kayi gidan yari ba, zan tabbatar da kai a matsayin mai gsky ba zaka wulaƙanta ba" nan ma shiru ya yi mata bai ce komai ba kamar yadda ta tsammata. Hawayen da take maƙalewa ne ya kwance mata wanda ya zuba a tafin hannun Sheikh. Da sauri ya ƙankame hannunsu dake riƙe da nata yana buɗe idanunsa a hankali wanda suka sauya daka rinewar da sukai. Fararen idanun nasa ya ɗora akanta ganin hawaye a Fuskarta ya ƙara sashi cikin damuwa amma sam hakan bai bayyana a garesa ba. "Kayi magana Babana rashin maganarka shike sawa a dinga tunanin baka da gasky, zuciyata ba zata jure ganinka haka ba" Kallonta yake har lokacin bai ce komai ba. Ganin bashi da niyyar magana yasa Mother fashewa da kuka sosai tana miƙe tsaye da sauri ya riƙe hannunta gam! Yana miƙewa tsaye jallabiya ce jikinsa mai kyau da tsada ga laushi da tsantsi. Kai ya fara Girgiza mata yana matse hannunta sosai babu abin da Sheikh yake ƙauna sama da mahaifiyarsa sai Father daga su Hakimi sune duniyarsa. Hannunsa mother ta riƙe ta ce "Try to speak Sheikh ban damu ba nasan zan fahimce ka, zamu Court bani da wani proof da zan kareka, mene gasky?" Riƙe hannun Mother Sheikh ya yi tare da fara buga ƙafa yana ƙoƙarin buɗe bakinsa. Ganin haka yasa Mother taimaka masa wajan riƙe hannunsa tana faɗin "Ahha say something, speak Babana, say it" hannunta duk biyun ya kama ya riƙe yana runtse idanunsa sai buga ƙafa yake tuni hawaye ya fara cika idanunsa. "Yee... Ƙaƙƙƙaaa... M...mmm" kai ta ɗaga masa tana shafa kansa a fisge bayan ya buga ƙafarsa da ƙasa yana saka hannun Mother a bakinsa ya ce "Babbbban akaita ba, bbbb ba zan taɓa yin yin yin haka ba mother" yana faɗin hakan yana ƙara saka hannun Mother a bakinsa duk ya jiƙa mata hannu da yawunsa mai ƙamshi a ƙoƙarinsa na ganin ya yi magana daidai waya baiwa ta Sheikh idan koyarwa zai yana samu maganarsa ta fita yake fara karatu cikin sauri baya tsayawa sai ya gama yana gamawa baya ƙara cewa komai yake fita daga hall. Wani irin rauni ya kama zuciyar Mother tausayi da ƙaunar Sheikh ya ƙara wanzuwa a zuciyarta wacce irin larura ce haka wacce bata barin har babban mutum? Zare hannunta ya yi domin har ransa bai san lokacin daya saka hannunta a baki ba a hankali ya juya zai bar wajan da sauri mother tana goge hawaye ta ce "Aliyu" cak ya tsaya tana ƙoƙarin magana Umar-khan ya shigo wajan da sauri gaba ɗaya suka bisa da kallo Umar-khan ya ce "Sheikh na shirya mota a ƙofar baya, yanzu zamu bar gidan nan jami'ai na hanyar zuwa nan zasu kamaka" ko motsawa Sheikh bai ba shi dai ya san ba zai taɓa hana abin da Ubangiji ya tsara afkuwa ba. "Jeka Aliyu ka bisu su fitar dakai Sheikh" Mother ta faɗa tana jan hannunsu ganin haka yasa ya bita har zuwa bakin wata sabuwar mota shiga ya yi. Drivern yaja, Umar-khan shima ya shiga mota, Saif-Wazir ya shiga wata motar. Motar ƙarshe kuma Ishaq-hakim ya shiga kai tsaye suka nufi wata hanya ta daban. Sbd gujewa haɗuwa da jami'an da kuma ƴan jaridu, kasancewar duk sunyi connecting wayoyinsu dana juna yasa Umar-khan gyara bluetooth na kunansa ya ce "Saif-Wazir" Saif ya amsa da "Ina kan layi" haka Ishaq-hakim da kuma Drivern Sheikh. Cikin jin daɗi Umar-khan ya ce "Saif-Wazir idan mun isa Shatalelen gidan gwamna kabi hanyar Amado bello way" Saif-Wazir ya ce "Noted bro" Umar-khan ya ce "Ishaq-hakim kabi hanyar Asibitin nasarawa, Drivern Sheikh Kabi hanyar ƙofar nasarawa,ni kuma zanbi hanyar kasuwar tarauni, gaba ɗaya hanyoyin zasu haɗamu a titin Dawaki roud zamu sauka gidan Hakimi.." haka duk suka amince suna zuwa Shatalelen gidan gwamna ko wacce mota ta ɗauki hanyarta suka ɗauke tunanin jami'an tsaron daka hanyar da zasu bi, Sheikh na bayan mota ya zubawa ikon Allah idanu a haka suka ƙarasa Dawaki roud motocin suka haɗu waje guda kai tsaye suka ƙarasa gidan Hakimi. Sheikh na fito da ƙafarsa waje aka riƙe hannuna tare da saka masa sarƙa kamar daga sama yaji ance "You are under arrest.....
08119237616.
Kafin Iliya ya yi magana Hamma Yabi ya faɗo office ɗin da sauri cikin tsawa Dr Hamza ya ce "Malam ya haka zaka faɗo kamar wani mahaukaci? Me ya sa duk fulanin nan baku da ilimin zaman rayuwa ne, baku san yadda ake mu'amala ba?" Hamma baya gane zancan nasu ya ce "Don Allah ka taimaki Dadarmu, kada ta mutu cikin wannan halin ita kaɗai ta rage mana, sau wajan goma ina zuwa" "Idan munje kanta lafiya zamu bata kenan? Ko zamu hanata mutuwa? Zan maka last warning Kada na sake ganin ƙafarka cikin asibitin nan, na faɗa maka bamu da maganin ko ɗaya me kake so nayi maka? Haba kuna yi mana adalci mu likitoci sai an bimu a hankali mai ya sa zan zuciyarku ya yi yawa ne?" kasa magana Hamma yai sbd Hawayen daya cika masa idanu me ya sa su Fulani ake musu kallon mahaukata wanda basu san me suke ba? Akwai wani bambanci a jikinsu wanda ya bambanta su da sauran jama'a ne? Juyawa ya yi yana zuriyarsa babu daɗi. Danejo na ganinsa ta ce "Hamma ya naga ka daɗe, numfashi Dadata zai gudu ka taimaka, ina masu bada lafiya ɗin?" A hankali ya kama hannunta ya riƙe yana shafa kanta dake ɗauke da suma mai kyau can ƙasa ya ce "Muje gida, ba zamu ƙara zuwa asibitin nan ba, Allah ya a bamu Kuɗi mu kaita asibitin burni" shiru kawai tayi tana kallonsa tare da son fahimtar abin da yake nufi a haka suka koma gida jiki babu daɗi, kwana sukai ba su yi bacci ba, Shatu kawai ta runsta sbd ƙarancin shekarunta. A daren Danejo ta sanyawa ranta zata sai da nono iya iyawarta ta tara kuɗi masu yawa akai Dada asibiti. Hakan yasa ta tashi da asuba ta tatsi kindirmo a ƙwayar gari na fara haske ta nufi cikin burni wajan Abti America.
Mother ce ke sakkowa daga upstairs kunnanta maƙale da waya idanunta sanye cikin farin glasses ta fito a Barrister Maryam ɗinta sak. A hankali ta ce "Na riga nayi reporting case ɗin, idan ba a samu good evedance ba akan wanda suka kawo ƙarar Aliyuna, kai tsaye zan maka ko wacce ƴar banza a court dama kawai nake jira" daga cikin wayar aka ja numfashi tace "Barrister Maryam kasa aje court,idan akaje to kin bawa duniya damar zata fahimci halin da ake ciki,abi komai a sannu" ɓayayyiyar ajjiyar zuciya Mother ta sauke idanunta na sauka akan Zeefa da Fattoumah "Ok za mu yi magana bari naje wajansa Allah ya sa ya yi magana, al'amarin Sheikh na bani tsoro yana bani mamaki" ƙara tattaunawa sukai kafin sukai sallama. "sannu da sakkowa mother" idanunta akan Plasma ɗin da suke kallo ta ce "Fattoumah sau nawa zan ce bana son kuna kallon zee world ne? Ashe ban isa daku ba ko?" A sanyaye Fattoumah ta ce "We're sorry Mother ba zamu sake ba" zama tayi ta ce "Change the channel immediately Mamana" Sauya channel Fattoumah ta yi zuwa Aljazeera tana faɗin "Ok Mother" kallonsu ta yi sosai ta ce "Where's Maimoon and Auta?" Zeefa ta bata amsa da "She's inside the kitchen, Auta barci take" Mother ta ce "Bana son barcin yamma taso mini ita" tana faɗin ta miƙe tare da nufar kitchen daga bakin ƙofa ta tsaya tana kallon Maimoon dake haɗa coffee ta ce "Ina Lunch ɗin Sheikh?"... "Gashi a tray mother bari na kai masa" tsareta tayi da idanu ta ce "Bani nan" tray ɗin lunch ta bawa Mother tana ci-gaba da aikin gabanta.
Haɗaɗɗan part ɗinsa ta nufa tun daga nesa ƙirar arar Sheikh Muhammad didat ta ratsa cikin kunnuwanta da Mmkin fal fuskar Mother ganin ƙofar shiga parlournsa a buɗe. Ƙamshin air-cod ya ratsa cikin hancinta. Tana shiga idanunta ya sauka akan Umar-khan dake zaune gabansa ɗauke da system yana duba wani abu, ganin Mother ya sa Umar-khan saurin miƙewa tsaye ya ce "Sannu da zuwa Mother" "Yawwa Umar-khan ina Aliyun?" Hanyar da zata sadaka da bedroom ɗin Sheikh ya kalla yana faɗin "a Parlour na samesa lokacin da nazo, ina fara yi masa magana akan wannan case ɗin ya tashi ya shige bedroom har yanzu bai fito ba" jinjina kai tayi ta nufi bedroom ɗin, babu abin da bedroom ɗin yake sai ƙamshin turarensa ROJA wanda ya a jima da kama ɗakin duk da cewa bai fiye rayuwa a cikin gidan iyayen nasa ba, yafi rayuwa a Madina idan yana ƙasa Nigeria kuma yafi rayuwa a gidan Hakimi. ba kowa nan ma a bedroom ɗin sai tsarin ɗakin da Mother tabi da kallo wanda a kullum yake Sauya mata, komai na ɗakin fari ne tas, ɓangaren clothes, shoes, perfumes. Komai daban yake. Juyawa tayi zuwa parlourn tana faɗin "Umar-khan Aliyu baya nan fa? Ko dai ya tafi gidan Hakimi?" Umar-khan yai shiru ya ce "Bashi da ikon fita, kamar kullum ƴan jaridu na waje ta ko'ina maybe yana Library ɗinsa" sai a lokacin ta tuna da Library tana zuwa ciki ta samesa zaune akan wata ƙyakkyawar kujera wacce take juya kanta da kanta ya rufe idanunsa, sumar kansa ta ɗan bayyana sbd yanayin naɗin rawanin nasa wanda ya yi da farin hirami. Hannunsa harɗe a ƙirji. Zama tayi kujerar dake kusa dashi tana kama hannunsa ta ce "Abbana Babana" ajjiyar zuciya Sheikh Aliyu Haydar ya sauke sbd jin sunan da Mother's ta kirasa da shi amma ya kasa buɗe idanunshi domin baya son ta fahimci halin da idanunsa ke ciki wanda sune kaɗai suke fallasa raunin zuciyarsa. "Buɗe idanunka mu yi magana Babana, ba zan taɓa bari kayi gidan yari ba, zan tabbatar da kai a matsayin mai gsky ba zaka wulaƙanta ba" nan ma shiru ya yi mata bai ce komai ba kamar yadda ta tsammata. Hawayen da take maƙalewa ne ya kwance mata wanda ya zuba a tafin hannun Sheikh. Da sauri ya ƙankame hannunsu dake riƙe da nata yana buɗe idanunsa a hankali wanda suka sauya daka rinewar da sukai. Fararen idanun nasa ya ɗora akanta ganin hawaye a Fuskarta ya ƙara sashi cikin damuwa amma sam hakan bai bayyana a garesa ba. "Kayi magana Babana rashin maganarka shike sawa a dinga tunanin baka da gasky, zuciyata ba zata jure ganinka haka ba" Kallonta yake har lokacin bai ce komai ba. Ganin bashi da niyyar magana yasa Mother fashewa da kuka sosai tana miƙe tsaye da sauri ya riƙe hannunta gam! Yana miƙewa tsaye jallabiya ce jikinsa mai kyau da tsada ga laushi da tsantsi. Kai ya fara Girgiza mata yana matse hannunta sosai babu abin da Sheikh yake ƙauna sama da mahaifiyarsa sai Father daga su Hakimi sune duniyarsa. Hannunsa mother ta riƙe ta ce "Try to speak Sheikh ban damu ba nasan zan fahimce ka, zamu Court bani da wani proof da zan kareka, mene gasky?" Riƙe hannun Mother Sheikh ya yi tare da fara buga ƙafa yana ƙoƙarin buɗe bakinsa. Ganin haka yasa Mother taimaka masa wajan riƙe hannunsa tana faɗin "Ahha say something, speak Babana, say it" hannunta duk biyun ya kama ya riƙe yana runtse idanunsa sai buga ƙafa yake tuni hawaye ya fara cika idanunsa. "Yee... Ƙaƙƙƙaaa... M...mmm" kai ta ɗaga masa tana shafa kansa a fisge bayan ya buga ƙafarsa da ƙasa yana saka hannun Mother a bakinsa ya ce "Babbbban akaita ba, bbbb ba zan taɓa yin yin yin haka ba mother" yana faɗin hakan yana ƙara saka hannun Mother a bakinsa duk ya jiƙa mata hannu da yawunsa mai ƙamshi a ƙoƙarinsa na ganin ya yi magana daidai waya baiwa ta Sheikh idan koyarwa zai yana samu maganarsa ta fita yake fara karatu cikin sauri baya tsayawa sai ya gama yana gamawa baya ƙara cewa komai yake fita daga hall. Wani irin rauni ya kama zuciyar Mother tausayi da ƙaunar Sheikh ya ƙara wanzuwa a zuciyarta wacce irin larura ce haka wacce bata barin har babban mutum? Zare hannunta ya yi domin har ransa bai san lokacin daya saka hannunta a baki ba a hankali ya juya zai bar wajan da sauri mother tana goge hawaye ta ce "Aliyu" cak ya tsaya tana ƙoƙarin magana Umar-khan ya shigo wajan da sauri gaba ɗaya suka bisa da kallo Umar-khan ya ce "Sheikh na shirya mota a ƙofar baya, yanzu zamu bar gidan nan jami'ai na hanyar zuwa nan zasu kamaka" ko motsawa Sheikh bai ba shi dai ya san ba zai taɓa hana abin da Ubangiji ya tsara afkuwa ba. "Jeka Aliyu ka bisu su fitar dakai Sheikh" Mother ta faɗa tana jan hannunsu ganin haka yasa ya bita har zuwa bakin wata sabuwar mota shiga ya yi. Drivern yaja, Umar-khan shima ya shiga mota, Saif-Wazir ya shiga wata motar. Motar ƙarshe kuma Ishaq-hakim ya shiga kai tsaye suka nufi wata hanya ta daban. Sbd gujewa haɗuwa da jami'an da kuma ƴan jaridu, kasancewar duk sunyi connecting wayoyinsu dana juna yasa Umar-khan gyara bluetooth na kunansa ya ce "Saif-Wazir" Saif ya amsa da "Ina kan layi" haka Ishaq-hakim da kuma Drivern Sheikh. Cikin jin daɗi Umar-khan ya ce "Saif-Wazir idan mun isa Shatalelen gidan gwamna kabi hanyar Amado bello way" Saif-Wazir ya ce "Noted bro" Umar-khan ya ce "Ishaq-hakim kabi hanyar Asibitin nasarawa, Drivern Sheikh Kabi hanyar ƙofar nasarawa,ni kuma zanbi hanyar kasuwar tarauni, gaba ɗaya hanyoyin zasu haɗamu a titin Dawaki roud zamu sauka gidan Hakimi.." haka duk suka amince suna zuwa Shatalelen gidan gwamna ko wacce mota ta ɗauki hanyarta suka ɗauke tunanin jami'an tsaron daka hanyar da zasu bi, Sheikh na bayan mota ya zubawa ikon Allah idanu a haka suka ƙarasa Dawaki roud motocin suka haɗu waje guda kai tsaye suka ƙarasa gidan Hakimi. Sheikh na fito da ƙafarsa waje aka riƙe hannuna tare da saka masa sarƙa kamar daga sama yaji ance "You are under arrest.....
08119237616.