← Book details Idan Ba Ke Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 16 OF 55

Sashe 16

Idan Ba Ke Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Gari na waye Barrister Zainab ta zo suka fita zuwa State C.i.d ita da Mother abin mamaki gaba ɗaya ƴan jaridu sun cika gidan Redio, da t.v kowa yana jiran a fito da Sheikh Aliyu Haydar Aliyu. Cikin nutsuwa Barrister Zainab dake driving ta kalli mutanan ta ce "Am still wondering ta ya ya zan can nan ya shiga kunnuwan Al'umma" Murmushin taƙaici kawai Mother ta yi wai duk akan Innocent son ɗinta ake wannan tururuwar kamar wanda ya kashe mutum?. "Allah ya kyauta, mutane akwai su da son gulma musamman ƴan jarida wallahi" I.d card ɗinta wanda ke nuna ita cikakkiyar lawyer ce mai zaman kanta ta nuna kana aka basu damar shiga, tun kafin Barrister Zainab ta yi parking idanun Mother ya sauka akan Sheikh wanda aka fito dashi cikin wata ƙatuwar sarƙa tare da wasu manyan ƴan fashi, wani abu ya tsaya mata wanda bata taɓa jin irinsa ba, ko hawaye ta kasa a wannan lokacin. Da sauri ta fita haka ma Barrister Zainab ɗin, ana ƙoƙarin saka Sheikh Aliyu cikin mota wata mota ta shigo da gudu cikin haraba wajan hakan ya sa duk suka daka ta. Wani babban jami'in tsaro ne tare da Abba Hakimi suka fito daga cikin motar sai wata matashiyar budurwa wacce Fuskarta ta kumbura sosai sbd kuka. I.G ya kalli jami'an tsaron cikin tsawa ya ce "Maza a cire sarƙar nan, a bawa Sheikh Aliyu Haydar Aliyu kayansa ya saka, He's Innocent ya fita daga jikin zargi, Wannan matar ita ce wacce ta shirya komai, she's the reason behind, She is the one who harmed Aliyu"
Gaba ɗaya kallon budurwar sukai wacce take kuka kamar ranta zai fita. A karo na farko Sheikh Aliyu Haydar Aliyu ya ɗago idanunshi tare da sauke su akan budurwar wani irin lallausan murmushi ya sauke wanda ya kusan ɗauke hankali jama'a tare da basu mamaki, hatta Mother tai mamakin ganin murmushi a fuskar Aliyun. Cikin ƙaramin lokaci aka sakawa Sheikh wata jallabiya mai kama da Alkyabba tare da wani farin hirami nan da nan kamalarsa ta fito haibarsa ta cika Idanun kowa. I.G ya bada umarnin a kama budurwa Sheikh ya yi gyara murya yana tafiya a nutse cike da kamala tsayawa yai daidai inda budurwar take, for the first time a tsayin rayuwarsa daya tsaya gaban mace kana ya juya ya kalli I.G sanin cewa ba zai iya taɓa jikin I.G ba yasa ya kama hannun Abba Hakimi ya riƙe da kyau yana runtse idanunshi, ƙafarsa ya ɗaga ya buga a ƙasa cikin In-ina ya ce "Aahhhh ahhha abarta, dooo.. do.. domin ba ba ba....ba a faɗa da Aljani.

Not Edited
08119237616
🫰🏽kai tsaye ga mai buƙatar littafin.

*🌈 IDAN BA KE 🌈*

*_Arewabooks@Nimcyluv_*

11.....
Abba Hakima ya kalli Sheikh a nutse yana mai sakin murmushi shi ma, tare da juyawa ya kalli budurwar wacce taƙi yarda ta kalli inda Sheikh ɗin yake, tun daga sama zuwa ƙasa Abba Hakimi ya ƙare mata kallo kafin ya ce "A'uzu bi wajhillahil karim, Wabi kalimaatil lahillati la yujawizuhunna barran wala fajiran, wabi asma'illahil husna kulliha, ma alimtu minha wa malam a'alam min sharri ma yanzilu minas sama'i, wa zara'a fil'ardhi, wa min sharri ma yakhruju minha, wa min fitnatillaili wan nahari, wa min ɗawariƙil laili wan nahari, illa ɗariƙan yadruƙu bikhairin ya Rahamanu. Wa min sharri kulli dàabbatin Rabbi akhizun bi nasiyatuha inna Rabbi ala siraɗin mustaƙim" jikin budurwar ne ya fara rawa sosai, tsoran Abba Hakimi da Sheikh Aliyu Haydar Aliyu suka cika mata zuciya, bata son su cutar da ita tunda ita bata zo da nufin hakan ba, kuma daman Ubangiji ya ɗora mata tsoran Sheikh ɗin tun ba yanzu ba, tana jin girma da nauyinsa tare da shakkar sa kwarjininsa yafi komai dagula mata lissafi. Idan ka ɗauke Abba Hakimi, No one understands the words of Sheikh Aliyu.

"No!!!"
Sheikh Aliyu Haydar ya furta a nutse yana riƙe hannun Abba Hakimi wanda bakinsa ya kasa yin shiru da addu'ar da yake, dalilin hakan yasa budurwar ta nemi birkicewa wanda kuma daga Abba Hakimi sai Sheikh ɗin ne kawai suke ganin hakan. Shiru ya yi da addu'ar yana kallonta kafin ya juya ya kalli Sheikh fuskarsa ɗauke da annuri irin na cikakkun dadtawan nan ya ce. "Yaushe Aliyu ya samu abokai haka bani da labari" a wannan karan Sheikh bai murmushi ba sai rirriƙe hannun Abba Hakimi da ya yi yana lumshe idanunsa tare da buɗewa alamar "Bai san yadda akai hakan ya faru ba" riƙe hannu Sheikh ɗin kai tsaye Abba Hakimi ya yi domin kai tsaye ya fahimci karatun idanun na Sheikh.
I.G dake tsaye shi da Barrister Maryam yana bata haƙuri ya ce.
"I'm sorry, action was taken without investigation, we were wrong" kasa riƙe kanta mother ta yi cikin losing control ta ce. "You have defamed Sheikh's name, all those who respect him have now stopped, Sbd Kuskuren ku my son is innocent na riga dana faɗa muku, but you refused to understand me" Bar Zainab ta numfasa cikin rashin jin daɗi ta ce "Everything that has happened has already happened, kawai a kira ƴan Jaridu a shaida masa Sheikh bashi da laifi, sharri ake masa bai san komai ba a wanke sunan shi daga ɓacin da ya yi" cikin martabawa da nuna rashin daɗin abin da duk ya faru I.G ya ce.
"Aikinmu ne hakan, za muyi abin da ya dace muma ba zamu so sunan Sheikh ya lalace ba yana da girma da daraja a idanun ba" Mother gaba ɗaya haushin duk wasu jami'an tsaron take ji hakan yasa cikin sauri ta juya zuwa inda Abba Hakimi da Sheikh suke tsaye, idan ka gansu zaka ɗauka da gaske Hakimi shi ne ya haifi Sheikh sbd tsananin haibar dake maƙale a jikin ko wanne kusan duk halin Hakimi Sheikh ya kwashe shi tas.
Kallonsu ta yi cike da son ko wanne wanda ke rinjayar zuciyarta ta ce "Thank you Abba Hakimi" murmushi kawai ya yi bai ce mata komai ba, tana ƙoƙarin sake magana ya yi saurin barin wajan zuwa cikin motar da Umar-khan ya buɗe masa baya.
Tsaye Sheikh yana bin mahaifiyar tasa da kallo ganin tai shiru ya waro mata manyan Idanun shi yana son cewa wani abu amma ya ja bakinsa ya yi shiru a hankali ta ce "zaka bini ko Abban naka za kabi?" Bakinsa ya motsa yana rufe idanu tare da fara buga ƙafa yana riƙe jikinsa da kyau cikin In-ina ya ce "Zazzzza... zan zan zanje gida wajan fa... fa.. father ina soooo son ganinsa"
haushi ne ya kama Mother ganin duk abin da ake Sheikh yana maƙale da son mahaifinsa. "Father baya gari, kaje wajan Hakimi ka huta da kyau gobe sai kazo mu tattauna, ina tunanin za a haƙura da zuwa Madina haka" girgiza mata kai ya yi bai ce komai ba ya juya ganin har lokacin Abba Hakimi na zaune bayan motar, yanzu zuwa shima ya shiga baya Ishaq-hakim ya jasu. daga nan Bar Zainab gidanta ta shige hakan yasa Umar-khan ɗaukan Mother a ɗaya daga cikin motocin Sheikh suka nufi gida, Saif-Wazir kuma ya tsaya domin magana da ƴan jarida.

Suna tafe a hanya Sheikh na yiwa Abba Hakimi hira cikin nutsuwa duk da In-ina yake amma Hakimi na fahimtar komai da Sheikh ke faÉ—a, a duk maganganun Sheikh ba za kaji kalmar MACE ta fito daga bakinsa ba, balle har ya ware wata musamman yana magana a ganta, Murmushi kawai Hakimi yake Ubangiji ne shaidar son da ya kewa Sheikh a jinin jikinsa yake.
A haka suka ƙarasa haɗaɗɗan gidan Abba Hakimi dake Dawaki roud, gida ne irin na sarauta mai kyan tsari da fasali ko'ina ma'aikata ne , motar na tsayawa Sheikh ya fito ƙwayar idanunsa na nuna gajiyar da yake ciki.
Bai tsaya jiran Abba ba, kai tsaye ya nufi part ɗinsa wanda yake cikin gidan Abba Hakimin wanka ya yi da ruwa mai zafi yana gamawa ya fito ɗaure da babban towel idanunshi na janye wa barci na cin ƙarfinsa ya ɗauki wani tsadaddan lotion, Shea body butter ya shiga shafawa saman fatarsa a kasalance, Engage Cologne Spray ya fesa a fatarsa sbd ɗauke zafin da ya keji yana gamawa ya miƙe zuwa clothes ɗinsa ya ɗauki wani trousers mara nauyi ya saka ko riga bai saka ba, ya cilla mint bakinsa ya kwanta saman bed yana lulluɓe jikinsa da bargo, ganin rana ce ya sa ya kunna A.c tare da rufe idanunshi cike da fatan barci ya ɗauke shi.

Washegari gari tun da Sheikh ya farka bai koma barci ba, har ya fita sallar Subhi sai da gari ya yi haske wajan 6:30 ya dawo gida jikinsa duk ciwo yake masa sbd rashin gym da bai ba, wanka ya ƙara yi ya shirya cikin Scabal wool suit white colour sai red ɗin necktie. Sai Diamond Rolex daya maƙala a hannunsa, yau a Yaa Lee ya fito ba a Sheikh ba, domin kusan siffa biyu gare shi, idan zashi bank shigar suit yake duk abin da ya danganci addini ajjiye shi yake a gefe amma yana zuciyar shi, idan kuma ya sanya Alkyabba da rawani yana matsayin Sheikh a wannan lokacin ne ba Yaa Lee ba. Wayarsa ya ɗauka jacket ɗin sa a hannu cikin nutsuwa ya fita zuwa main parlour.
Ƙamshin ROJA shi ne ya fara kaiwa su Abba Hakimi ziraya yana zaune da jallabiya gefensa kuma Ishaq-hakim ne da Saif-Wazir shirya zasu shi wajan aiki, sai Momi A'isha tana zubawa Abba Hakimi Shayi mai zafi. "Mrng Yaa Lee" jinjina kai ya yi idanunshi akan Abba Hakimi ya furta. "B...bar bar barka da safi fifi fiya".
Chapter 16 · 0% Book details