Sashe 33
Idan Ba Ke Part 1 Complete Hausa Novel · about 5 min read
Maimoon ta kalli Halisa wacce ke zaune a ƙasan carpet ta ce "Sister tasu muje part ɗin mu" Halisa ta girgiza kai Maimoon ta ce "Anty Zahrah ta ce mu tafi tare zuwa dare sai ki dawo" ta miƙe tana faɗin "Ita ta ce haka?" Maimoon ta ce "ita ce mana" hannunta ta kama suna zuwa Main parlour El-bashir na tashi tare da ɗaga waya ya nufi ƙofa, Halisa ta bi bayan shi da kallo ta ɗauka Balarabe ne. Maimoon taja hannunta har zuwa part ɗin su, Zeefa da auta Fattoumah suna zaune ganin Halisa yasa Auta Fattoumah faɗin "Wow yaya Moon wannan kyakkyawa ce She's very beautiful she looks like bro El" Maimoon ta ce "to sarkin surutu" ta zaunar da Halisa ta shiga ɗakko mata su ice cream da chocolate amma sam Halisa taƙi ce sbd bata saba dasu ba, ta ɗago kai a hankali ta ce "bana cin irin wannan" Nazeefa ta ce "To sai me?" A hankali kanta a ƙasa ta ce "Kindirmo nake shu" a tare suka zare idanu tare da faɗin "what?" Tai shiru tana kallon su can Maimoon ta ce "Zeefa haɗa mata ruwan wanka a bathroom bari na kawo mata kindirmon" tana faɗin hakan tai waje har lokacin Maimoon ta kasa mance abin da idanunta ya gani a bedroom ɗin Zahrah. Cikin sauri Zeefa ta haɗa mata ruwan wanka tare da nuna mata komai a toilet ɗin da yadda ake amfani da su. Suna bakin toilet ɗin suka ji ana knocking "Halisa duba kiga waye?" Kamar ba zata ba sai ta nufi ƙofar jiki a sanyaye zagin da Zahrah tayi mata har yanzu damun zuciyarta yake.
Halisa ta tsaya bakin ƙofa ta rasa me za ta ce can dai ta ce "waye?" Ta faɗa cikin ƙasa da murya. El-bashir ya gyara tsaiwa hannunsa riƙe da waya da kuma chocolate ya ce "Buɗe ki gani mana?" Halisa ta murguɗa baki tana ƙoƙarin buɗe ƙofar Zeefa ta ce "jeki kiyi wankan bari na buɗe ƙila Maimoon ce" Halisa ta juya zuwa bathroom ba tare da ta ce komai ba, Zeefa na buɗe ƙofar taga El-bashir tsaye fuska ɗaure ta ce "Yaya El" ya wurga mata harara ya ce "wace take tambayar waye?" Zeefa ta juya ta kalli ƙofar bathroom ta ce "Laa Halisa ce bata sanka bane" ya ce "I'll break her legs" chocolate ya bawa Zeefa ya juya yana faɗin "Kira mini Fattoumah" ya nufi Main parlour Mother dake zaune ta ce "Yau zaka shige ne?" Ya ce "I don't think so.. sai abin da Mai martaba ya ce" ta ce "Ohh abokin Mai martaba".
Washegari Zahrah na zaune ta caɓa ado cikin wata atamfa mai kyau ruwan ƙwai ta yafa mayafi babba kamar ta Allah. A hankali ta fito zuwa Main ta samu Mother zaune ita da Jadda suna hira sai Maimoon Zeefa da Auta Fattoumah suna makaranta. Zahrah ta durƙusa ta ce "Ina yini Mother?" Mother ta ce "kina lafiya ya kwanan baƙunta?" Zahrah ta ƙara sunkuyar da kai alamar kunya ta ce "Allahamdulillah, daman cewa nayi bari nazo idan da aiki nayi" Jadda da bakinta ke rawa ta ce "Allah ya yi gutsi gutsi da maƙaryaci" Zahrah taƙi kallon Jadda. Mother ta ce "Ayyah jeki ki huta ba aiki" Zahrah dai ta kasa riƙe abin da yake ranta ta ce "Yaa Sheikh fa? daman ina son gaishe shi ne" da hannu Mother ta nuna mata wani part ta ce "zaki iya samun shi can" ta miƙe da sauri ba kunya ta nufi Part ɗin Yaa Sheikh.
Mother ta ce "Maimoon kira mini Halisa yanzu" Maimoon ta nufi part ɗin Zahrah ta samu Halisa sai zuba kayan Zahrah take cikin trolley bag tayi saurin riƙe hannunta ta ce "Kizo Mother na kiranki" Halisa ta ce "Bari na ƙarasa aikin Anty" Maimoon ta ɗaga ta tsaye ba tare da ta ce komai ba ta jata zuwa waje. Bata samu Mother a parlour ba sai suka shige bedroom ɗinta tana zaune bakin gado. Mother ta ce "shigo Halisa, Maimoon jeki ko" Maimoon ta juya Halisa ta shiga kanta a ƙasa haka kunyar Mother tai mata nauyi taji kunyarta ta ce "Saki jekin ki zo nan" ta kama hannunta tare da zaunar da ita bakin gado ta ce "Yaya sunanki ma?" A hankali ta ce "Halisa Danejo Rome" Mother ta jinjina kai ta ce "Ok Zahrah ƴar uwar ki ce?" Ta girgiza kai ta ce "A'a wai aikatau zan mata" ta faɗi haka a taƙaice. Mother ta jinjina kai sosai ta ce "Saurare ni da kyau, Zahrah matar Yaa Sheikh ce Wannan babban mutumin da kika gani fari dashi?" Halisa ta ce "Balarabe?" Mother ta ce "Yawwa shi" haka kurum idanun Halisa ya cika da ruwa Mother ta ce "Shi ne mijin Zahrah kuma kema mijinki ne, dan haka ke ba ƴar aiki bace matar shi ce ke, kamar yadda Zahrah take matar shi haka kema kike matar sa" Halisa tai ta kallon Mother har lokacin idanunta cike yake da hawaye da gaske Balarabe shi ne mijin Zahrah?. Mother ta katse mata tunani da faɗin.
"Kece uwar gida, aurenki aka fara ɗaurawa sannan na Zahrah, na kira ki muyi magana sbd Yaa Sheikh ya ce baya son ki" da sauri Halisa ta miƙe tsaye hawaye na zubu mata bakinta na rawa ta ce "Amma ni ina son shi ai.....
Ni ina team Yaa Sheikh ku fa?
08119237616
Paid book
₦500
Halisa ta tsaya bakin ƙofa ta rasa me za ta ce can dai ta ce "waye?" Ta faɗa cikin ƙasa da murya. El-bashir ya gyara tsaiwa hannunsa riƙe da waya da kuma chocolate ya ce "Buɗe ki gani mana?" Halisa ta murguɗa baki tana ƙoƙarin buɗe ƙofar Zeefa ta ce "jeki kiyi wankan bari na buɗe ƙila Maimoon ce" Halisa ta juya zuwa bathroom ba tare da ta ce komai ba, Zeefa na buɗe ƙofar taga El-bashir tsaye fuska ɗaure ta ce "Yaya El" ya wurga mata harara ya ce "wace take tambayar waye?" Zeefa ta juya ta kalli ƙofar bathroom ta ce "Laa Halisa ce bata sanka bane" ya ce "I'll break her legs" chocolate ya bawa Zeefa ya juya yana faɗin "Kira mini Fattoumah" ya nufi Main parlour Mother dake zaune ta ce "Yau zaka shige ne?" Ya ce "I don't think so.. sai abin da Mai martaba ya ce" ta ce "Ohh abokin Mai martaba".
Washegari Zahrah na zaune ta caɓa ado cikin wata atamfa mai kyau ruwan ƙwai ta yafa mayafi babba kamar ta Allah. A hankali ta fito zuwa Main ta samu Mother zaune ita da Jadda suna hira sai Maimoon Zeefa da Auta Fattoumah suna makaranta. Zahrah ta durƙusa ta ce "Ina yini Mother?" Mother ta ce "kina lafiya ya kwanan baƙunta?" Zahrah ta ƙara sunkuyar da kai alamar kunya ta ce "Allahamdulillah, daman cewa nayi bari nazo idan da aiki nayi" Jadda da bakinta ke rawa ta ce "Allah ya yi gutsi gutsi da maƙaryaci" Zahrah taƙi kallon Jadda. Mother ta ce "Ayyah jeki ki huta ba aiki" Zahrah dai ta kasa riƙe abin da yake ranta ta ce "Yaa Sheikh fa? daman ina son gaishe shi ne" da hannu Mother ta nuna mata wani part ta ce "zaki iya samun shi can" ta miƙe da sauri ba kunya ta nufi Part ɗin Yaa Sheikh.
Mother ta ce "Maimoon kira mini Halisa yanzu" Maimoon ta nufi part ɗin Zahrah ta samu Halisa sai zuba kayan Zahrah take cikin trolley bag tayi saurin riƙe hannunta ta ce "Kizo Mother na kiranki" Halisa ta ce "Bari na ƙarasa aikin Anty" Maimoon ta ɗaga ta tsaye ba tare da ta ce komai ba ta jata zuwa waje. Bata samu Mother a parlour ba sai suka shige bedroom ɗinta tana zaune bakin gado. Mother ta ce "shigo Halisa, Maimoon jeki ko" Maimoon ta juya Halisa ta shiga kanta a ƙasa haka kunyar Mother tai mata nauyi taji kunyarta ta ce "Saki jekin ki zo nan" ta kama hannunta tare da zaunar da ita bakin gado ta ce "Yaya sunanki ma?" A hankali ta ce "Halisa Danejo Rome" Mother ta jinjina kai ta ce "Ok Zahrah ƴar uwar ki ce?" Ta girgiza kai ta ce "A'a wai aikatau zan mata" ta faɗi haka a taƙaice. Mother ta jinjina kai sosai ta ce "Saurare ni da kyau, Zahrah matar Yaa Sheikh ce Wannan babban mutumin da kika gani fari dashi?" Halisa ta ce "Balarabe?" Mother ta ce "Yawwa shi" haka kurum idanun Halisa ya cika da ruwa Mother ta ce "Shi ne mijin Zahrah kuma kema mijinki ne, dan haka ke ba ƴar aiki bace matar shi ce ke, kamar yadda Zahrah take matar shi haka kema kike matar sa" Halisa tai ta kallon Mother har lokacin idanunta cike yake da hawaye da gaske Balarabe shi ne mijin Zahrah?. Mother ta katse mata tunani da faɗin.
"Kece uwar gida, aurenki aka fara ɗaurawa sannan na Zahrah, na kira ki muyi magana sbd Yaa Sheikh ya ce baya son ki" da sauri Halisa ta miƙe tsaye hawaye na zubu mata bakinta na rawa ta ce "Amma ni ina son shi ai.....
Ni ina team Yaa Sheikh ku fa?
08119237616
Paid book
₦500