← Book details Ameenatouh Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 12 OF 88

Sashe 12

Ameenatouh Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

White Nike loose fit shirt ya saka da white wandon me tsayi.

A single couch Dake dakin ya zauna ahankali tareda dago idanuwansa da sukai wani irin laushi sun cire Jan da sukai ya zubawa fuskanta Dake kwance kan pillow Daya Saka mata gashinta duk ya warware ya fita band da aka daure mata dashi.

Dauke kallansa yayi daga kanta ahankali tareda miqewa ya dauko magani da alluran Daya dauko daga dakinta a cikin aljihun wandon Daya cire ya dawo ya ajiye kan table tareda dauko wayarsa ya kunnata tareda dawowa office dinsa ya zauna ya Nemo wata number ya Saka Kira Dan aikata abinda yakeson aikatawan.

Har tsakan dare sosai Yana zaune ya kasa Kwanciya bayana zafin zuciya Babu abinda yake fama dashi
Daqyar yaga anyi asuba ya fice Masallacin cikin asibitin.

Yana dawowa daga masallaci sister Ashley yayi text din tazo.

Babu Bata lokaci kuwa sai gata tana zuwa ya umarceta da taje ta kawo wasu uniform din Ameenatou din tazo ta Saka mata sbd na jikinta sun yage sosai.

Bayan tafiyanta kasa barin ta dawo yayi ya shiga bedroom din ya dauko Ameenatou da har lokacin Bata iya ko motsawa ya nufi dakinta da ita a wheelchair da kansa ya turata,
Yayi Hakan ne sbd Babu Wanda yake shigan masa dakin dayasan Yana bacci bayan Mum dinsa sai Siddeeq sai Haroon da ya tafi yabar duniya sai Kuma Ameenatou din da yau ta hau gadonsa.
##MAMUH#
#DR JAMAAL JEEY SEELAH
#MAM SEELAH
#LAMEENU SEELAH
#OMAR SEELAH
#AMEENATOU SEELAH
#ARFAT SEELAH

*_ZAFAFA BIYAR_*

1 *_Ameenatou!!_*
_Mamuhgee_

2 *_Tsutsar Nama!!_*
_Billyn Abdull_

3 *_Gudun Kaddara!!_*
_Safiya huguma_

4 *_Kwankwason Jimina!!_*
_Miss xoxo_

Guda Daya 400
Guda biyu 700
Guda uku 1k
Guda hudun 1200

*_6019473875 MUSAA ABDULLAH SAFIYAH keystone bank_*

*_ATURA SHEDA ZUWA 09166221261_*

*_MTN/VTU 09134848107_*

_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din 09033181070*_

*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_**_Arewabooks@Mamuhgee_*
#ZafafaBiyar
69
Koda ya Isa dakin har lokacin block din tsit yake Babu motsin tashin patients sai motsin cleaners kawai,

Sister Ashley na ganin ya kawo Ameenatou din duk ta sake rikicewa da tashin hankalin yanda Akai take office dinsa da wannan lokacin na asuba itama yau din a asibitin ta kwana.

Itace ta gyarawa Ameenatou din gado ya dauketa kaman baby da kansa ya kwantar da ita tareda dago idanuwansa yayiwa sister Ashley kallan day Sakata Neman rikicewa sbd kwarjinsa da kyansa dayake cikawa mutane da yawa ido yace kar ta bar Ameenatou din daga yau zata dawo block din.

Wayarsa ce tayi ringing Dan haka Bai qara magana ba ya bar maganar a taqaice ya juya bayan ya sake maimaitawa sister Ashley din ko paracetamol idan ba shine yace ta Bata ba kar a Kuma Bata komai Daya danganci magani ko allura duka zaiji da komai ayau din.

Juyawa yayi ya fice Yana daga wayan
Sister Ashley tabi bayansa da kallo tana Jin duka jikinta mutuwa Amma Kuma batajin zata iya shiru zataiwa sir siddeeq magana taji matsayin Dr JEEY SEELAH a gurin Ameenatou sbd hankali da dokan aiki harma da sanin iyakar da Allah ya saka tsakanin mace da namijin da ba muharrami ba ta hanata daukan kwanan Ameenatou office din Dr JEEY duk wannan magana CE da babu wanda zai daga bakinta.

Daga Nan kwancen ta zare kayan Ameenatou din ta sake dorata wheelchair ta nufi toilet da ita Tayo mata wanka suka fito ta shiryata tareda Bata tea ta Dan gyara mata gashinta ta zauna tana magana cikin kulawa da kauna tareda lallabawa ta fice tabarta kwance idanuwanta na rufewa bacci me nauyi na daukanta.

Karfe goma na safe Dr Dee ya iso asibitin a gigice sbd mummunan sakon Daya samu Rana tsaka na daukesa da Akai Kai tsaye kwata kwata da asibitin Shima kaman yanda sukaiwa Dr Adams Dan gwara Adams da suka daukesa daga Nan guri me kyau aka turasa shi kuwa wata kaddararriyar asibitin mahaukatanta dataci uwar uban wannan da hauka aka turasa a Wani local government Dake under Lagos din hakama asibitin bama zai kirata da asibitin ba sedai gidan Tara mahaukatan kan hanya Dan kuwa mahaukata gwamnati ke kamawa na kan hanya tana tarasu acan ana Dan dubawa da yawansu tsaban haukansu data baci har kashe nurses sunsha yi da likitoci sai gashi kwatsam baisan ta inda hakan ta faru ba ya wayi gari da wannan mugun ji da mugun ganin.

Gigicen dayake ya Saka kwata kwata baisan ma wa zai fara Kira yaji inda wannan mugun abun ya samesaba Dan haka Kai tsaye yayo asibitin sbd Jin ko akwai lefi ko matsalan da aka samu da sunansa.

Yana isowa Dr JEEY ma shi yabar asibitin zuwa gida Dan hutawa ko kansa zai sake daga nauyi da ciwon dayake masa.

Rashin ganin Dr JEEY ya Saka Dr Dee sake shiga tashin hankali gashi idan yaqi zuwa kaman ya dakatar da aikinsa ne gaba Daya Dan haka yake a cikin tashin hankalin da Bai taba shiga ba a rikice ya Nemo numbern Alh Lameenu seelah Dan samun numbern Dr JEEY din batareda tinanin tin farko ai baima fada masa JEEY din Yana kasar ba.

Dad Lameenu na tareda Mam suna magana a office din Mam din Dake seelahs Kiran Dr Dee ya shigo wayar daddy Lameenu din.

Jin ringing din wayarsa ya Sanyashi juyowa ahankali ya Kalli gefensa datake a ajiye,

Ganin sunan Dr Dee ya sakashi Jin faduwan gaba Amma Bai nuna komaiba ya fuske tareda miqa hannunsa ya katse Kiran Yana cigaba da magana da Mam Wanda yake karanta sakwannin da suka samu na amincewan hadin gwiwan da suka samu daga wani Dan South Africa na aiki dashi na millions of dollars.

Sake shigowa Kiran yayi a Karo na biyu,
Qin dauka daddy lameenu din yasake yi shikuma Dr Dee din Bai Dena kiranba.

Satan kallan Mam yayi a fakaice sbd karantar yanayinsa Amma Kuma kwata kwata hankalin Mam din Baya kansa,

Yafi kowa sanin Mam Dan haka Hakan ba shine ke nufin Bai Ankara da rashin daukan wayansa ba duk da rashin daukan waya garesu normal Abu ne da kusan haka rayuwarsu take Dan ba kowane yake kira su dauka din ba tinda kusan dabia ce ta wainda Naira ta jiqa suka jiqu,
Suma Hakan ne garesu basa daukan waya Sam ta kowa Amma Kuma Mam kallo Daya yake Maka ya karanceka tsaf batareda ya nuna Hakan ba Dan shi Baya Saka ido yake gane abu,

Hakan ne ya Saka daddy lameenu din kasa samun nutsuwa Dan kobai daga ba Mam zai iya karanto Wani abin Wanda Komin qanqantar abinda zai fahimtar to tabbas Saiya gane sauran bayanin Dan haka daddy lameenu dole ya kame fuska ya daga wayar cikin nutsuwa da Kwanciyar hankalin dayake yafawa kansa na karfin hali ya Dan sake fuska Yana cewa

"Hello barka da Rana Honourable"

Cikin tashin hankali Dr Dee da baima San shi aka kira da honourable din ba yace

"Ranka ya Dade Dr JEEY SEELAH ya lalatamin career kwata kwa.....

Wani mummunan Tari me qarfin gaske ne ya tirnike daddy lameenu din sakamakon yawun bakinsa da suka wuce ba daidaiba da abinda Dr Dee din ya fada dayafi sakwon mutuwa tashin hankali a gurinsa gashi ba Daman tambayar wane JEEY SEELAH din Mam Yana zaune ya jisa,

Shi Kam wane babban bala'in ne wannan ke Naman rikito masa?
Tayaya Yana cikin masifar rashin Kwanciyar hankalin Mam karya Gano komai gameda abinda yake boyewa,
yanzu Kuma Rana tsaka wannan Yana ce masa Dr JEEY?..

Innalillahi wainna ilaihirrajiun" ya Karanta a zuciyarsa kusan so goma Yana Jin jininsa na neman tafasa ya kone a gaban Mam batareda ya iya motsawa ba Dan motsinsa kadai Mam ke jira ya fahimci abinda yake ciki.

"Ya Allah ka dauki ran Dr Dee dinnan yanzu yanzu idan ya fita daga inda yake sbd wannan mugun balain da masifar dayake Neman Sakasa."

Dr Dee dayake kan wayar yanata zuba bayani cikin tashin hankalin dayake ninkar masa baisan daddy Lameenu tini ya ajiye wayar gefensa ba batareda ya kashe wayar ba sbd rikicewa.

Tarinsa Bai tsayaba har lokacin hakama Mam Bai juyo ya kallesaba Sedai a natse hankali kwance ya dauki cup din ruwan sanyin Dake gabansu tareda roban bottle water da aka tsiyaya a glass cup din ya miqawa Lameenu din Bai dagoba har lokacin karatun emails din yakeyi a natse yace

"Lafiya dai??"

Ruwan daddy Lameenun ya karba ya Dan sha kadan Yana gyaran muryansa sbd ruwan da suka tsaya masa su qarasa wucewa Shima a nacen Yana calming kansa yace

"Eh, inaga Yana tareda mutane baimasan ya kira din ba,
Idanma Wani abin ne zai sake kira inaga."

Cigaba sukai da abinda yake gabansu Amma kusan hankalin daddy lameenu ya kasu kashi kusan goma Amma bazaka taba gane Hakan ba.

Sun jima suna tattaunawa Kuma tsawon wannan lokacin Dr Dee Bai Dena kira ba Amma dayake daddy lameenu din ya Saka wayar silent take shi yasa shi kadai ne me ganin shigowan Kiran da tsinkewansa.

Suna gamawa daddy lameenu ya fito Yana kokarin Saka Kiran BB ya nufi office dinsa sedai kafin ya Isa lift ta Bude da Dr Dee Dan haka kusan tare suka Kalli juna cikin mamaki da tashin hankali sedai na daddy lameenu din a boye yake Babu wani abu na damuwa ko tashin hankalin a tattare dashi.

Gaidashi Dr Dee yake kokarin yi ya amsa masa a taqaice tareda sanar dashi yaje zasuyi magana anjima zai nemesa yanzu yanada baqin da zai Gani.

Cikin tashin hankali Dr Dee ya biyosa zuwa office dinsa suna shiga ya Kalli Daddy lameenu din muryansa na sarqewa yace

"Dr JEEY SEELAH ya......

Dakatar dashi daddy lameenu yayi da zaunawa kan kujera ya ajiye wayarsa gefensa yace

"Wane Dr JEEY SEELAH din kake magana?
Kasan shi ne?
A Ina ya sanka dazai Maka koma Menene kake kokarin fadan ya makan?
Dr JEEY SEELAH Daya ne Kuma Baya qasar ba Kuma zai taba dawowa kasan ba..

Cikin Wani irin dacin zuciya da damuwa Dr Dee yace

"Dr JAMAAL JEEY MAM SEELAH guda Dayan daka sani nake magana Dan kuwa Yana qasar Nan.....
Chapter 12 · 0% Book details