Sashe 93
A Zato Na Complete Hausa Novel · about 8 min read
Wasu matasan yan mata biyu naci karo dasu, ba laifi dukansu kyawawa ne. Dayar zata yi sa'ata, fara ce ba can ba, doguwa mai dan jiki, yayin da dayar kuma daga ganinta kasan kanwar dayar ce, yanayin kamanninsu da surarsu kusan daya ce, kawai dai karamar tafi babbar kiba da fari.
Nayi yar fara'a duk da cewa ban san su ba, na musu iso zuwa ciki. Sai da suka zauna akan kujera, sannan naje na dauko lemu da ruwa na kawo musu.
Na zauna muka gaisa dasu, nace "ko kuna neman wani gida ne?".
Karamar ce tayi saurin cewa "a'ah, Yaya Bilal ne ya kawo mu nan!".
Na karkata kai ina kallonsu cikin mamaki, me zai hadinsu da Bilal? Na gyada kai a hankali nace "Allah sarki!".
Karamar ta sake cewa "ni sunana Zainab, wannan kuma Hajara". Ta nuna babbar.
Sai lokacin na kula da yadda babbar take ta sunke kai tunda suka shigo. Wow!! Sai lokacin na fahimci komi. Ita ce Hajarar dama? What a nerve she has! Da har ta iya kwaso kafafu tazo min gida.
Kafin in iya daga baki in ce wani abu, Yaya ya shigo cikin falon. Ya zauna a gefena, Allah ne ya iya bani ikon samun dauriya, na cije ban dankara mishi harara ba.
Yace "Madam, ga Hajara na kawo miki".
Na gyada kai ina dan murmushin yake, "aikuwa na ga Hajara"...
Shi ya zama jagorar hirar tamu, ga mamakina cikin dan lokaci kankani muka saki jiki daga ni har su. Ko lokacin da lokacin sallah yayi, tafiya yayi ya barmu. Na kaisu dakina suka yi sallah, muka koma falo. Dana shiga kicin haka suka biyo ni, duk da magiyar dana musu akan su koma falo suyi kallo ko wani abu, fir suka ki. Duk wannan abin da ake yi, Muhaaseen na bayan Hajara a goye.
Kafin Yaya ya dawo mun gama girki. Muka zauna mu duka muka ci ana ta hira.
Anan na fahimci cewa dukansu a Abuja suka tashi, shima Babansu matanshi biyu, in fact, Zainab step sister din Hajarar ce. Ita Zainab tana Abuja uni tana karantar mass com, tana aji daya. Ita kuma Hajara wannan shekarar ta gama degree dinta akan architecture a jami'ar Tafawa 'Balewa, Bauchi.
A abinda na karanta a cikin dan lokacin, shine suna da wani irin sanyin hali da hangen nesa, haka iliminsu ya tabo ta kowane fanni.
Zuwa lokacin da yamma tayi, suka mana sallama akan zasu tafi, sai naji kamar kada su tafi. Allah ya gani, naji dadin zuwansu sosai. Suma daga ganin yadda suka mike din zasu tafi, hakan take. Shima sai da direban da aka turo ya daukesu yazo, sannan suka tashi.
Na shiga daki cikin drawers dina da nake ajiyar abubuwa saboda bakin ba zata, na ciro musu turaruka masu kamshi, chocolates, kayan kwalliya, cike da leda na fito. Muka musu rakiya har gaban motarsu ni da Yaya. Sai da zasu shiga sannan Yaya ya karbi Muhasseen a hannun Hajara, na kula Allah ya hada jininsu sosai.
Na mikawa Zainab ledar hannuna, da taki karba, na harareta cikin wasa, "ko dai kin raina ne?".
Ta zaro ido da sauri, a lokaci guda kuma ta sanya hannu ta karba, "haba dai Anty! Mungode sosai, Allah ya amfana!". Wani halin nasu mai burgewa kenan, akwai godiya. Daidai da abinci wannan dana zuba mana, sai da suka biyo mu da godiya da addu'a.
Nace "babu komi wallahi, ku gaida su Mama Sai mun zo ziyara".
Hajara tace "sai mun ganku!". Daga haka direban yaja mota suka fita daga cikin farfajiyar gidan.
Yaya ya sakalo hannunshi daya akan kafadata, dayan kuma yana rike da Muhaaseen. Yace "ya?".
Na daga kai na kalleshi ina dan murmushi, "uhmm, ba laifi. She doesn't look that bad!".
Yaya yayi murmushi a hankali, ya shafo hancinshi da nawa, "haka ne?".
Na gyada kai ina murmushi. Da gaske ne kuma, haka kawai naji hankalina ya kwanta da ita sosai. Kai duk da cewa tun kafin zuwansu dama na saddakar, amma hankalina bai kwanta ba.
Yanzu kuwa dana ganta, sai naji hankalina ya kwanta da ita sosai, shima auren hankalina ya kwanta dashi.
Watakila maybe, just maybe, ba zata yi halin Ramata, Ameerah ko Raheemah ba. Kila ita za ayi zaman mutunci da ita!.
K'arshe!
'THE GREATEST HAPPINESS OF LIFE IS THE CONVICTION THAT WE ARE LOVED; LOVED FOR OURSELVES, OR RATHER, LOVED IN SPITE OF OULSELVES!'.
VICTOR HUGO
*☆⋆Epilogue⋆☆*
Bayan Shekaru Biyar...
"Ni abinda yake daure min kai shine, babu fa abinda na mishi, kawai daga sama kamar saukar aradu naji maganar, ya sakar min ita aka kamar tashin bomb!".
Janan take fada cikin tsananin kunar zuci.
Ni kuwa me zanyi in ba shekewa da dariya ba? Na dinga kya-kyatata kamar ba zan daina ba. Tana gefena tana jefo min bama-baman harara ita kuma. Sai da nayi ta isheni, na gyara zamana ina kwashe kwallar data zubo min.
Tayi kwafa, "baki da kirki wallahi Na'ilah. Saboda ke kina da kishiya, shi yasa kike sheka min dariyar mugunta nima don za'a min?".
Na daga kafada, "tunda na dandana, kowa ma ya dandana mana. Ke dalla ki kwantar da hankalinki, ki daina wani daga hankalinki akan abinda bai taka kara ya karya ba. Ita fa kishiyar nan, wallahi gane mata ne mutane basu yi ba saboda kawai sun riga sun fadawa kansu ba abokiyar zama bace, amma da gaske abokiyar zama ce. Ke ni yanzu wallahi Abban Maama ko ta uku da hudu yace zai karo, zamana zan gyara kawai ince Allah ya shigo dasu gidan lafiya. Ga fili ga mai doki, to ma wai, a kaina zasu zauna ne? Wasu ayyukan ma zasu rage min karewa. Ko ba komi, kin samu rarar kwanakin girki, kin samu abokiyar tayin ayyuka da hira, kin samu yar tayin raino da hidimar gida, sannan at least, wulakancin namiji ba sai kare a kanki ke kadai ba, ya dinga rabawa biyu yana bata rabi itama".
Janan ta kame baki, tace "Innalillahi! Na'ilah, kece kuwa ko dai wata ce mai kama dake?".
Nayi murmushi nace, "shafa ki ji!".
Ta jinijina kai, "Allah kenan! Kuma rayuwa kenan, babu abinda ta bari. Idan wani yace min akwai rana da zata zo ki tausar da wani akan zama da kishiya, wallahi ba zan taba yarda ba".
Na gyada kai a hankali, ko ni kaina ina mamakin kaina.
A shekaru biyar ko shida da suka wuce, idan wani ya fada min cewa zan zauna in fadi wani alkhairi game da zama da kishiya, hakika da idan muka fara fada dashi babu wanda zai iya raba mu dashi sai Allah.
Ban taba zaton akwai lokacin da zai zo, in so kishiya ba, in kuma kaunace ta, ban taba ba.
Duk a zato na, kishiyar bala'i, masifa ce, wadda zata kawo maka rashin zaman lafiya da kowa naka, wadda zata kawo maka bakin jini ta sanya maka cuta a cikin jiki da zuciyarka. Ashe duk rashin fahimta ce ta kawo hakan.
A zato na, bata nufar kowa da alkhairi sai sharri. Nayi zaton tana shigowa tunanin fitar dani daga cikin gidan aurena zata fara yi, sai naga banbanci.
Tabbas Anty Sailu tayi gaskiya, da tace ba duka aka taru aka zama daya ba. Duniyar Allah mai fadi ce, ba'a rasa mutanen kirki a cikinta. Kamar yadda ba'a rasa abokan zama na gari a cikinta.
Ina ga ni nayi dace ne sosai, Allah ya hada ni da wadda ban taba zaton zan hadu da ita ba.
Koma dai menene, ta dalilinta sai gashi ina kallon abokiyar zama da wani ido daban, in a different way, in a different light.
Ta saka ni fahimtar cewa, tsanar kishiya dana taso ina yi, saboda banyi dacen haduwa da mai halin kirki bane, wadda take kaunar zaman lafiya da zaman aminci da amana.
Ramata dama can halinta mara kyau ne, irin mutanen nan ne da dama can tun asali basa son wani daban ya rabe su ko wani nasu, sun fi son komi ya kasance nasu ne su kadai, basa son cigaban kowa sai nasu. Saboda haka ne suke yin duk abinda suka ga zasu iya, don su ga cewa sun kawar da duk wani abu da zai yi threatening dinsu da cigaban su. Saboda haka ne su son kishiya ko diyanta, baya cikin lissafinsu, me yasa zaka so abinda kasan cewa ya fika matsayi a inda kake so kaga cewa kafi kowa matsayi?.
Haka Raheemah, haka ma Ameerah.
Na fahimci cewa su irin wadannan mutanen, son zuciya da son kai ya musu yawa. Shi yasa basa tunanin komi, kuma basa tunanin kowa sai kansu.
Ita kuma duniyar yanzu, cike take da mutane masu son kai da son zuciya, yan kalilan ne masu son farincikin wasu da cigaban wasu.
Duk ban fahimci hakan ba sai a dalilin zaman da nayi da abokiyar zama na, Hajara. Yanzu zan iya fada da alfaharina, cewa ita ba kishiya ta bace, 'yar uwa ce. Ta dalilinta idanu na suka washe sosai, har nake iya dauko uzurirrika akan dalilin da yasa wadanda na zauna dasu a baya suka dinga yin abubuwan da suka yi din, sai naji na dan fahimce su. Duk da cewa naga rashin wayonsu, tausayinsu yafi rinjayata.
Dama sun bi ta wata hanyar da ba wannan ba.
Dama basu biyewa rudin duniya, shawarar abokan banza, da bakar zuciyarsu ba.
Dama sun bi ta hanyar data dace, dama sun sowa wasu daban irin rayuwar da suke sowa kansu.
Watakila da yanzu muna tare dasu cikin aminci kamar yadda muke zaune da Hajara.
Nayi yar fara'a duk da cewa ban san su ba, na musu iso zuwa ciki. Sai da suka zauna akan kujera, sannan naje na dauko lemu da ruwa na kawo musu.
Na zauna muka gaisa dasu, nace "ko kuna neman wani gida ne?".
Karamar ce tayi saurin cewa "a'ah, Yaya Bilal ne ya kawo mu nan!".
Na karkata kai ina kallonsu cikin mamaki, me zai hadinsu da Bilal? Na gyada kai a hankali nace "Allah sarki!".
Karamar ta sake cewa "ni sunana Zainab, wannan kuma Hajara". Ta nuna babbar.
Sai lokacin na kula da yadda babbar take ta sunke kai tunda suka shigo. Wow!! Sai lokacin na fahimci komi. Ita ce Hajarar dama? What a nerve she has! Da har ta iya kwaso kafafu tazo min gida.
Kafin in iya daga baki in ce wani abu, Yaya ya shigo cikin falon. Ya zauna a gefena, Allah ne ya iya bani ikon samun dauriya, na cije ban dankara mishi harara ba.
Yace "Madam, ga Hajara na kawo miki".
Na gyada kai ina dan murmushin yake, "aikuwa na ga Hajara"...
Shi ya zama jagorar hirar tamu, ga mamakina cikin dan lokaci kankani muka saki jiki daga ni har su. Ko lokacin da lokacin sallah yayi, tafiya yayi ya barmu. Na kaisu dakina suka yi sallah, muka koma falo. Dana shiga kicin haka suka biyo ni, duk da magiyar dana musu akan su koma falo suyi kallo ko wani abu, fir suka ki. Duk wannan abin da ake yi, Muhaaseen na bayan Hajara a goye.
Kafin Yaya ya dawo mun gama girki. Muka zauna mu duka muka ci ana ta hira.
Anan na fahimci cewa dukansu a Abuja suka tashi, shima Babansu matanshi biyu, in fact, Zainab step sister din Hajarar ce. Ita Zainab tana Abuja uni tana karantar mass com, tana aji daya. Ita kuma Hajara wannan shekarar ta gama degree dinta akan architecture a jami'ar Tafawa 'Balewa, Bauchi.
A abinda na karanta a cikin dan lokacin, shine suna da wani irin sanyin hali da hangen nesa, haka iliminsu ya tabo ta kowane fanni.
Zuwa lokacin da yamma tayi, suka mana sallama akan zasu tafi, sai naji kamar kada su tafi. Allah ya gani, naji dadin zuwansu sosai. Suma daga ganin yadda suka mike din zasu tafi, hakan take. Shima sai da direban da aka turo ya daukesu yazo, sannan suka tashi.
Na shiga daki cikin drawers dina da nake ajiyar abubuwa saboda bakin ba zata, na ciro musu turaruka masu kamshi, chocolates, kayan kwalliya, cike da leda na fito. Muka musu rakiya har gaban motarsu ni da Yaya. Sai da zasu shiga sannan Yaya ya karbi Muhasseen a hannun Hajara, na kula Allah ya hada jininsu sosai.
Na mikawa Zainab ledar hannuna, da taki karba, na harareta cikin wasa, "ko dai kin raina ne?".
Ta zaro ido da sauri, a lokaci guda kuma ta sanya hannu ta karba, "haba dai Anty! Mungode sosai, Allah ya amfana!". Wani halin nasu mai burgewa kenan, akwai godiya. Daidai da abinci wannan dana zuba mana, sai da suka biyo mu da godiya da addu'a.
Nace "babu komi wallahi, ku gaida su Mama Sai mun zo ziyara".
Hajara tace "sai mun ganku!". Daga haka direban yaja mota suka fita daga cikin farfajiyar gidan.
Yaya ya sakalo hannunshi daya akan kafadata, dayan kuma yana rike da Muhaaseen. Yace "ya?".
Na daga kai na kalleshi ina dan murmushi, "uhmm, ba laifi. She doesn't look that bad!".
Yaya yayi murmushi a hankali, ya shafo hancinshi da nawa, "haka ne?".
Na gyada kai ina murmushi. Da gaske ne kuma, haka kawai naji hankalina ya kwanta da ita sosai. Kai duk da cewa tun kafin zuwansu dama na saddakar, amma hankalina bai kwanta ba.
Yanzu kuwa dana ganta, sai naji hankalina ya kwanta da ita sosai, shima auren hankalina ya kwanta dashi.
Watakila maybe, just maybe, ba zata yi halin Ramata, Ameerah ko Raheemah ba. Kila ita za ayi zaman mutunci da ita!.
K'arshe!
'THE GREATEST HAPPINESS OF LIFE IS THE CONVICTION THAT WE ARE LOVED; LOVED FOR OURSELVES, OR RATHER, LOVED IN SPITE OF OULSELVES!'.
VICTOR HUGO
*☆⋆Epilogue⋆☆*
Bayan Shekaru Biyar...
"Ni abinda yake daure min kai shine, babu fa abinda na mishi, kawai daga sama kamar saukar aradu naji maganar, ya sakar min ita aka kamar tashin bomb!".
Janan take fada cikin tsananin kunar zuci.
Ni kuwa me zanyi in ba shekewa da dariya ba? Na dinga kya-kyatata kamar ba zan daina ba. Tana gefena tana jefo min bama-baman harara ita kuma. Sai da nayi ta isheni, na gyara zamana ina kwashe kwallar data zubo min.
Tayi kwafa, "baki da kirki wallahi Na'ilah. Saboda ke kina da kishiya, shi yasa kike sheka min dariyar mugunta nima don za'a min?".
Na daga kafada, "tunda na dandana, kowa ma ya dandana mana. Ke dalla ki kwantar da hankalinki, ki daina wani daga hankalinki akan abinda bai taka kara ya karya ba. Ita fa kishiyar nan, wallahi gane mata ne mutane basu yi ba saboda kawai sun riga sun fadawa kansu ba abokiyar zama bace, amma da gaske abokiyar zama ce. Ke ni yanzu wallahi Abban Maama ko ta uku da hudu yace zai karo, zamana zan gyara kawai ince Allah ya shigo dasu gidan lafiya. Ga fili ga mai doki, to ma wai, a kaina zasu zauna ne? Wasu ayyukan ma zasu rage min karewa. Ko ba komi, kin samu rarar kwanakin girki, kin samu abokiyar tayin ayyuka da hira, kin samu yar tayin raino da hidimar gida, sannan at least, wulakancin namiji ba sai kare a kanki ke kadai ba, ya dinga rabawa biyu yana bata rabi itama".
Janan ta kame baki, tace "Innalillahi! Na'ilah, kece kuwa ko dai wata ce mai kama dake?".
Nayi murmushi nace, "shafa ki ji!".
Ta jinijina kai, "Allah kenan! Kuma rayuwa kenan, babu abinda ta bari. Idan wani yace min akwai rana da zata zo ki tausar da wani akan zama da kishiya, wallahi ba zan taba yarda ba".
Na gyada kai a hankali, ko ni kaina ina mamakin kaina.
A shekaru biyar ko shida da suka wuce, idan wani ya fada min cewa zan zauna in fadi wani alkhairi game da zama da kishiya, hakika da idan muka fara fada dashi babu wanda zai iya raba mu dashi sai Allah.
Ban taba zaton akwai lokacin da zai zo, in so kishiya ba, in kuma kaunace ta, ban taba ba.
Duk a zato na, kishiyar bala'i, masifa ce, wadda zata kawo maka rashin zaman lafiya da kowa naka, wadda zata kawo maka bakin jini ta sanya maka cuta a cikin jiki da zuciyarka. Ashe duk rashin fahimta ce ta kawo hakan.
A zato na, bata nufar kowa da alkhairi sai sharri. Nayi zaton tana shigowa tunanin fitar dani daga cikin gidan aurena zata fara yi, sai naga banbanci.
Tabbas Anty Sailu tayi gaskiya, da tace ba duka aka taru aka zama daya ba. Duniyar Allah mai fadi ce, ba'a rasa mutanen kirki a cikinta. Kamar yadda ba'a rasa abokan zama na gari a cikinta.
Ina ga ni nayi dace ne sosai, Allah ya hada ni da wadda ban taba zaton zan hadu da ita ba.
Koma dai menene, ta dalilinta sai gashi ina kallon abokiyar zama da wani ido daban, in a different way, in a different light.
Ta saka ni fahimtar cewa, tsanar kishiya dana taso ina yi, saboda banyi dacen haduwa da mai halin kirki bane, wadda take kaunar zaman lafiya da zaman aminci da amana.
Ramata dama can halinta mara kyau ne, irin mutanen nan ne da dama can tun asali basa son wani daban ya rabe su ko wani nasu, sun fi son komi ya kasance nasu ne su kadai, basa son cigaban kowa sai nasu. Saboda haka ne suke yin duk abinda suka ga zasu iya, don su ga cewa sun kawar da duk wani abu da zai yi threatening dinsu da cigaban su. Saboda haka ne su son kishiya ko diyanta, baya cikin lissafinsu, me yasa zaka so abinda kasan cewa ya fika matsayi a inda kake so kaga cewa kafi kowa matsayi?.
Haka Raheemah, haka ma Ameerah.
Na fahimci cewa su irin wadannan mutanen, son zuciya da son kai ya musu yawa. Shi yasa basa tunanin komi, kuma basa tunanin kowa sai kansu.
Ita kuma duniyar yanzu, cike take da mutane masu son kai da son zuciya, yan kalilan ne masu son farincikin wasu da cigaban wasu.
Duk ban fahimci hakan ba sai a dalilin zaman da nayi da abokiyar zama na, Hajara. Yanzu zan iya fada da alfaharina, cewa ita ba kishiya ta bace, 'yar uwa ce. Ta dalilinta idanu na suka washe sosai, har nake iya dauko uzurirrika akan dalilin da yasa wadanda na zauna dasu a baya suka dinga yin abubuwan da suka yi din, sai naji na dan fahimce su. Duk da cewa naga rashin wayonsu, tausayinsu yafi rinjayata.
Dama sun bi ta wata hanyar da ba wannan ba.
Dama basu biyewa rudin duniya, shawarar abokan banza, da bakar zuciyarsu ba.
Dama sun bi ta hanyar data dace, dama sun sowa wasu daban irin rayuwar da suke sowa kansu.
Watakila da yanzu muna tare dasu cikin aminci kamar yadda muke zaune da Hajara.