Sashe 38
A Zato Na Complete Hausa Novel · about 8 min read
Maganar da yayi ce ta dakatar dani, "haba sister, daga zuwana kuma sai ki tafi sai kace ina korarki? Idan dai saboda nine, yi hakuri ki dawo ki zauna, sai in tafi".
Na juya ina kallonshi cikin dan murmushin da bai wuce fatar baki ba, nace "ba don kai bane likita, kawai naji ina son fita in dan shaki iska ne".
Yace "to idan haka ne, muje in raka ki shan iskan mana? Nima wajen na nufa yanzu ai".
Nace mishi "babu komi likita!".
Na zagaya kusa dashi muka jera muka fara tafiya. Muna ba Janan baya ya juyo ya kalleni, "to ya sunan malamar?".
Nace "Na'ilah!".
Ya maimaita sunan, "Na'ilah! So unique, I like it!". Nace mishi "nagode".
Muka cigaba da tafiya yana min kananun hirarraki har muka fita wajen, muka cinye karshen ginin. Ko dai ya fita, ko kuma ya hau sama ko kuma ya koma inda muka fito. Ya tsaya ya ja tunga tare da juyowa ya kalleni hannuwa cikin aljihun fara kal din rigar labcoat daya saka tana ta sheki a cikin ranar da muka tsaya a ciki, ya juyo muna fuskantar juna dashi.
Yace "ni fa son malamar nake, ya za ayi ne?".
Banyi mamaki ba, don dama nasan ko ba dade ko ba jima sai ya fadi hakan, nace "ni kuma?".
Ya langwabar da kai gefe, "yanzu duk alamomin da nayi ta jefo miki, kina so kice min baki taba kula ba?".
Na girgiza kai ina kallonshi, "ko kadan, ta yaya kake so in kula da hakan? I mean, ba tambari bane a goshinka da idan na ganka zan ga hakan kai tsaye ba".
Ya kyalkyale da dariya, "I like you, kina da ban dariya gaskiya. Ga murmushinki mai kyau". Na dan saki murmushi kawai.
Yace "nasan ke ba karamar yarinya bace, kin fahimceni tunda ba tun yau kike a cikin ward dinnan ba, amma tunda haka kika ce, zan bi ta hanyoyin daya kamata tuntuni, ko zan iya samun lambar malamar?".
Na dan girgiza kai ina murmushi, mutumin nan is very charming, da dai ace wani Muhammad bai sace min zuciya ba. Nace "ni fa kayi hakuri likita, an riga anyi mun miji a gida".
Ya kalleni tun daga sama har kasa yana wani murmushi, "ke din?". Na gyada mishi kai.
Yace "well then, na makara kenan. Amma shi mutum ai baya cire rai daga rahamar Allah, don haka ba zan saddakar ba tun yanzu...", ya ciro dan katinshi daga cikin aljihunshi ya miko min, nasa hannu na karba, ya cigaba da magana, "ina fata zamu cigaba da gaisawa haka nan, don maganar gaskiya kina burgeni sosai. Ina fata zaki taimaka min da lambar wayarki?". Wannan babu musu na karbi wayarshi na zuba mishi lambobina, ya karba yayi saving. Ya dago ya kalleni da dan siririn murmushi akan siraran fatar lebenshi, "sai kin ji daga gareni dear, thank you", ya kanne ido daya tare da juyawa abinshi ya tafi. Na bishi da kallo, yar karamar dariya na subuce min, na girgiza kai kawai.
Ban yi cikakken minti biyar ba na juya na koma, Janan ta kalleni tana wani murmushi tunda na shiga har na je kusa da ita, na ja kujera na zauna ina kallonta a daddage. Tace "meye kike wani hade fuska? Tambaya ce sai na miki ita, you and the doc?".
Na kwantar da kaina akan benci, "ni fa babu abinda yake tsakaninmu, ke da kika san komi, ina zan kai Muhammadu na kuma?".
Tayi murmushi, "ke da Muhammadun nan naki, Allah dai ya mana zabi nagari. Zaki shiga makaranta gobe, ko kuma zaki raka ni ne?".
Nace "zan raka ki dai kawai, ka samu dan hutu daga wannan wahalar". Ta kwashe da dariya, "daga dawowa har kin gaji?".
Na maida kaina na kwantar kawai.
*
Wajen karfe goma muka shiga cikin makaranta washegari bayan mun dauko excuse, da yake akwai sauran abokanmu dake cikin hostels din makarantar, Janan ta wuce department wajen supervisor dinta, ni kuma na shiga cikin makaranta da niyar idan ta gama dashi zata kira ni sai mu hadu da ita a gate mu koma asibitin. Ni sai gobe zan ga nawa supervisor din.
Dakin wata kawata Fatima da muka yi mutunci da ita naje sai aka ce min ai tana sick bay ma bata da lafiya, don haka na karkata na tafi wajenta. Na dan jima a wajenta muna hira da yake jikin nata da sauki, har ma ana za'a sallameta anjima. Janan ta kira ni tace min ta gama yanzu zata fito daga department, don haka na yiwa Fatima sallama da fatan karin sauki, na fita.
A daidai bakin gate naga Yaya Jameel sun shigo shi da Anty Sarah, abin ya bani mamaki da naga ciki a jikinta, dama ciki gareta? Suka wuce ni a mota ni kuma na wuce na fita. Sai dana ganta ne ma sannan na tuno cikin Sailuba itama, nasan cikinta ya tsufa yanzu, haihuwa ko yau ko gobe.
Akan hanya na kirata nake tambayarta, tace ai tana ma cikin asibiti, suna expecting din baby nan da sati daya. Nan muka yi sallama da ita muka kashe wayar.
A bakin gate muka hadu da Janan, muka jera muka fita daga cikin makarantar. Cikin asibiti zamu koma gabadayanmu. Nace mata "baki fada min Anty Sarah tana da ciki ba".
Tace "a ina kika gansu ne? Ashe baki kula da cikinta ba, kodayake last zuwan da kika yi baki ganta ba sosai, amma naji suna cewa ya jima ai".
Nace "a sick bay na gansu, naga ma kamar irin dadadden nan".
Tace "kinsan dogayen mutane dama, yanzu haka idan ba ido kika sanya mata ba, ba lallai ki gane tana dauke da ciki ba".
Na gyada kai, nace "haka ne, Allah ya raba lafiya". Tace "ameen".
Muka samu bus muka hau, tunda muka hau babu wanda yayi magana a cikinmu, da alamu kowa da tunanin da yake damunshi. Ni yawanci akan yadda zan karke rayuwata a gida ne idan na koma kafin inga yadda Allah zai yi dani, ko mai zai faru? Ita kuma Janan ban sani ba, har muka sauka daga bus din dai muka shiga cikin asibitin. Sai da muka fara tunkarar ginin asibitin sannan ta kalleni, murya cike da damuwa tace "ko yaushe matan Yaya Bilal zasu haihu ne?".
Nace mata "ita haihuwa ai ta Allah ce, idan ya nufa sai kiga an sameta ba zato babu tsammani".
Tace "haka ne, amma ina tausaya mishi wallahi. Shekaru suna ja suna kara wucewa, yakamata ace kamar yanzu dai ya fara ajiye nashi iyalin, kowa a cikin dangi ma abinda yake fada kenan".
Nayi shiru ina jinta, ni kaina wasu lokutan ina wannan tunanika, sai dai mafiya yawanci ban san akan wani tunani zan tsaya ba. Tsakanin Yaya da matanshi ban san waye bai haihuwa ba zata kuma iya yiwuwa wata kaddara ce daga Allah. Don haka na dafa kafadarta, nace "kada ki damu, in Allah ya yarda Allah zai kawo masu albarka".
Tace "Allah ya yarda". Muka cigaba da tafiya ba tare da mun sake yin magana ba har muka shige cikin ward din.
Ko bayan da muka tashi dakina muka wuce da ita, na mana danwake da yake Janan tana matukar son shi, ina cikin yin danwaken ita kuma tana gefe tana yanka mana cocumber, tumatiri da dafaffen kwai Esther kuma tana gefenmu tana taya mu hira, har na gama muka zauna muka fara ci bayan mun zambada yaji kamar na kamun mayu. Bayan mun gama ci muka sauka kasa ni da ita muka wanke kayan muka dauro alwala daga can muka dawo daki muka yi sallah. Tana sallame sallah wayarta ta dauki ruri kamar dama jiranta ake yi, ta daga wayar tayi murmushi tare da nuno min, sunan Yaya Bilal ne yake ta tsalle akan screen din wayar, na taya ta murmushi cike da mugunta.
Ta daga wayar a ladabce tana wani yin kasa-kasa da kai da kuma murya, hakuri kawai naji tana badawa, daga karshe dai ta kashe wayar tare da mikewa tsaye, ko babu tambaya nasan tafiya zata yi don haka nima na dauki hijabina na saka na bita a baya. Kamar kullum, sai dana rakata ta hau bus sannan na juyo na dawo hostel.
Ina dawowa sallah nayi na, dana gama na koma kan katifa na zauna tare da dauko littafaina ina kara reviewing takardun da zan kaiwa supervisor dina gobe, dana gama kuma na dauko textbooks ina kara karatun exams din da zamu yi sati mai zuwa. Har wajen karfe goma tayi Muhammad ya kira ni, na hada kan littafan na ajiye na amshi wayar.
*
Washegari sai da rana Mr. Akafyi ya min waya akan inje in sameshi, don haka na tafi makaranta. Bayan ya dudduba takarduna da sauran gyare-gyaren da zai min, yace inje inyi printing din wata chapter, na sauka kasa da sauri nayi, ina tsaye mutumin yayi da yake babu yawa kuma babu layin mutane, ya gama na biyashi na koma na kai mishi. Abin haushi da takaici, ina kai mishi yace ai ba wannan chapter din yace ba, wata ce daban, meaning na bata lokacina da kudina a banza. Tun farko kuma shi yace ba sai na dinga printing ba, kawai in dinga rubutawa ina kai mishi, gashi yanzu yana kokarin janyo min ciwon kai ta dalilin haka.
Nan na sake sauka kasa na bashi takardun, kusan zaman awa daya nayi a wajen yana aikin typing, ya gama ya miko min. Ina komawa ofishin mutumin aka ce ai har ya tashi, wani dan banzan makoko da kududu ya tsaye min a makoshi, naji kamar in kurma ihu. Takardun kawai na tura mishi ta karkashin kofar ofishin na tura mishi text akan na ajiye su, na tafi. Na kula mutumin da alamu sai na biyo mishi ta bayan gida sannan zamu rabu lafiya dashi.
Na juya ina kallonshi cikin dan murmushin da bai wuce fatar baki ba, nace "ba don kai bane likita, kawai naji ina son fita in dan shaki iska ne".
Yace "to idan haka ne, muje in raka ki shan iskan mana? Nima wajen na nufa yanzu ai".
Nace mishi "babu komi likita!".
Na zagaya kusa dashi muka jera muka fara tafiya. Muna ba Janan baya ya juyo ya kalleni, "to ya sunan malamar?".
Nace "Na'ilah!".
Ya maimaita sunan, "Na'ilah! So unique, I like it!". Nace mishi "nagode".
Muka cigaba da tafiya yana min kananun hirarraki har muka fita wajen, muka cinye karshen ginin. Ko dai ya fita, ko kuma ya hau sama ko kuma ya koma inda muka fito. Ya tsaya ya ja tunga tare da juyowa ya kalleni hannuwa cikin aljihun fara kal din rigar labcoat daya saka tana ta sheki a cikin ranar da muka tsaya a ciki, ya juyo muna fuskantar juna dashi.
Yace "ni fa son malamar nake, ya za ayi ne?".
Banyi mamaki ba, don dama nasan ko ba dade ko ba jima sai ya fadi hakan, nace "ni kuma?".
Ya langwabar da kai gefe, "yanzu duk alamomin da nayi ta jefo miki, kina so kice min baki taba kula ba?".
Na girgiza kai ina kallonshi, "ko kadan, ta yaya kake so in kula da hakan? I mean, ba tambari bane a goshinka da idan na ganka zan ga hakan kai tsaye ba".
Ya kyalkyale da dariya, "I like you, kina da ban dariya gaskiya. Ga murmushinki mai kyau". Na dan saki murmushi kawai.
Yace "nasan ke ba karamar yarinya bace, kin fahimceni tunda ba tun yau kike a cikin ward dinnan ba, amma tunda haka kika ce, zan bi ta hanyoyin daya kamata tuntuni, ko zan iya samun lambar malamar?".
Na dan girgiza kai ina murmushi, mutumin nan is very charming, da dai ace wani Muhammad bai sace min zuciya ba. Nace "ni fa kayi hakuri likita, an riga anyi mun miji a gida".
Ya kalleni tun daga sama har kasa yana wani murmushi, "ke din?". Na gyada mishi kai.
Yace "well then, na makara kenan. Amma shi mutum ai baya cire rai daga rahamar Allah, don haka ba zan saddakar ba tun yanzu...", ya ciro dan katinshi daga cikin aljihunshi ya miko min, nasa hannu na karba, ya cigaba da magana, "ina fata zamu cigaba da gaisawa haka nan, don maganar gaskiya kina burgeni sosai. Ina fata zaki taimaka min da lambar wayarki?". Wannan babu musu na karbi wayarshi na zuba mishi lambobina, ya karba yayi saving. Ya dago ya kalleni da dan siririn murmushi akan siraran fatar lebenshi, "sai kin ji daga gareni dear, thank you", ya kanne ido daya tare da juyawa abinshi ya tafi. Na bishi da kallo, yar karamar dariya na subuce min, na girgiza kai kawai.
Ban yi cikakken minti biyar ba na juya na koma, Janan ta kalleni tana wani murmushi tunda na shiga har na je kusa da ita, na ja kujera na zauna ina kallonta a daddage. Tace "meye kike wani hade fuska? Tambaya ce sai na miki ita, you and the doc?".
Na kwantar da kaina akan benci, "ni fa babu abinda yake tsakaninmu, ke da kika san komi, ina zan kai Muhammadu na kuma?".
Tayi murmushi, "ke da Muhammadun nan naki, Allah dai ya mana zabi nagari. Zaki shiga makaranta gobe, ko kuma zaki raka ni ne?".
Nace "zan raka ki dai kawai, ka samu dan hutu daga wannan wahalar". Ta kwashe da dariya, "daga dawowa har kin gaji?".
Na maida kaina na kwantar kawai.
*
Wajen karfe goma muka shiga cikin makaranta washegari bayan mun dauko excuse, da yake akwai sauran abokanmu dake cikin hostels din makarantar, Janan ta wuce department wajen supervisor dinta, ni kuma na shiga cikin makaranta da niyar idan ta gama dashi zata kira ni sai mu hadu da ita a gate mu koma asibitin. Ni sai gobe zan ga nawa supervisor din.
Dakin wata kawata Fatima da muka yi mutunci da ita naje sai aka ce min ai tana sick bay ma bata da lafiya, don haka na karkata na tafi wajenta. Na dan jima a wajenta muna hira da yake jikin nata da sauki, har ma ana za'a sallameta anjima. Janan ta kira ni tace min ta gama yanzu zata fito daga department, don haka na yiwa Fatima sallama da fatan karin sauki, na fita.
A daidai bakin gate naga Yaya Jameel sun shigo shi da Anty Sarah, abin ya bani mamaki da naga ciki a jikinta, dama ciki gareta? Suka wuce ni a mota ni kuma na wuce na fita. Sai dana ganta ne ma sannan na tuno cikin Sailuba itama, nasan cikinta ya tsufa yanzu, haihuwa ko yau ko gobe.
Akan hanya na kirata nake tambayarta, tace ai tana ma cikin asibiti, suna expecting din baby nan da sati daya. Nan muka yi sallama da ita muka kashe wayar.
A bakin gate muka hadu da Janan, muka jera muka fita daga cikin makarantar. Cikin asibiti zamu koma gabadayanmu. Nace mata "baki fada min Anty Sarah tana da ciki ba".
Tace "a ina kika gansu ne? Ashe baki kula da cikinta ba, kodayake last zuwan da kika yi baki ganta ba sosai, amma naji suna cewa ya jima ai".
Nace "a sick bay na gansu, naga ma kamar irin dadadden nan".
Tace "kinsan dogayen mutane dama, yanzu haka idan ba ido kika sanya mata ba, ba lallai ki gane tana dauke da ciki ba".
Na gyada kai, nace "haka ne, Allah ya raba lafiya". Tace "ameen".
Muka samu bus muka hau, tunda muka hau babu wanda yayi magana a cikinmu, da alamu kowa da tunanin da yake damunshi. Ni yawanci akan yadda zan karke rayuwata a gida ne idan na koma kafin inga yadda Allah zai yi dani, ko mai zai faru? Ita kuma Janan ban sani ba, har muka sauka daga bus din dai muka shiga cikin asibitin. Sai da muka fara tunkarar ginin asibitin sannan ta kalleni, murya cike da damuwa tace "ko yaushe matan Yaya Bilal zasu haihu ne?".
Nace mata "ita haihuwa ai ta Allah ce, idan ya nufa sai kiga an sameta ba zato babu tsammani".
Tace "haka ne, amma ina tausaya mishi wallahi. Shekaru suna ja suna kara wucewa, yakamata ace kamar yanzu dai ya fara ajiye nashi iyalin, kowa a cikin dangi ma abinda yake fada kenan".
Nayi shiru ina jinta, ni kaina wasu lokutan ina wannan tunanika, sai dai mafiya yawanci ban san akan wani tunani zan tsaya ba. Tsakanin Yaya da matanshi ban san waye bai haihuwa ba zata kuma iya yiwuwa wata kaddara ce daga Allah. Don haka na dafa kafadarta, nace "kada ki damu, in Allah ya yarda Allah zai kawo masu albarka".
Tace "Allah ya yarda". Muka cigaba da tafiya ba tare da mun sake yin magana ba har muka shige cikin ward din.
Ko bayan da muka tashi dakina muka wuce da ita, na mana danwake da yake Janan tana matukar son shi, ina cikin yin danwaken ita kuma tana gefe tana yanka mana cocumber, tumatiri da dafaffen kwai Esther kuma tana gefenmu tana taya mu hira, har na gama muka zauna muka fara ci bayan mun zambada yaji kamar na kamun mayu. Bayan mun gama ci muka sauka kasa ni da ita muka wanke kayan muka dauro alwala daga can muka dawo daki muka yi sallah. Tana sallame sallah wayarta ta dauki ruri kamar dama jiranta ake yi, ta daga wayar tayi murmushi tare da nuno min, sunan Yaya Bilal ne yake ta tsalle akan screen din wayar, na taya ta murmushi cike da mugunta.
Ta daga wayar a ladabce tana wani yin kasa-kasa da kai da kuma murya, hakuri kawai naji tana badawa, daga karshe dai ta kashe wayar tare da mikewa tsaye, ko babu tambaya nasan tafiya zata yi don haka nima na dauki hijabina na saka na bita a baya. Kamar kullum, sai dana rakata ta hau bus sannan na juyo na dawo hostel.
Ina dawowa sallah nayi na, dana gama na koma kan katifa na zauna tare da dauko littafaina ina kara reviewing takardun da zan kaiwa supervisor dina gobe, dana gama kuma na dauko textbooks ina kara karatun exams din da zamu yi sati mai zuwa. Har wajen karfe goma tayi Muhammad ya kira ni, na hada kan littafan na ajiye na amshi wayar.
*
Washegari sai da rana Mr. Akafyi ya min waya akan inje in sameshi, don haka na tafi makaranta. Bayan ya dudduba takarduna da sauran gyare-gyaren da zai min, yace inje inyi printing din wata chapter, na sauka kasa da sauri nayi, ina tsaye mutumin yayi da yake babu yawa kuma babu layin mutane, ya gama na biyashi na koma na kai mishi. Abin haushi da takaici, ina kai mishi yace ai ba wannan chapter din yace ba, wata ce daban, meaning na bata lokacina da kudina a banza. Tun farko kuma shi yace ba sai na dinga printing ba, kawai in dinga rubutawa ina kai mishi, gashi yanzu yana kokarin janyo min ciwon kai ta dalilin haka.
Nan na sake sauka kasa na bashi takardun, kusan zaman awa daya nayi a wajen yana aikin typing, ya gama ya miko min. Ina komawa ofishin mutumin aka ce ai har ya tashi, wani dan banzan makoko da kududu ya tsaye min a makoshi, naji kamar in kurma ihu. Takardun kawai na tura mishi ta karkashin kofar ofishin na tura mishi text akan na ajiye su, na tafi. Na kula mutumin da alamu sai na biyo mishi ta bayan gida sannan zamu rabu lafiya dashi.