Sashe 39
A Zato Na Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ina fita daga cikin department din naji ana kiran sallar la'asar, don haka na tsaya a masallaci nayi sallah sannan na wuce. A bakin gate na tsaya na sayi yoghurt mai sanyi, da niyar dana koma asibiti kafin in shiga ciki zan tsaya in sha saboda tun dazu cikina yake kiran ciroma, dama ban wani ci abin kirki ba yau da safe. Bayan na biya kudin an saka min a leda, na karbi canjin da suka rage min na maida cikin purse dita. Typing din da Mr. Akafyi ya saka ni sun cinye min kudi, nasan sai na sake zama na tsara yadda zan tafiyar dasu kafin in kashe su ban tantance ba.
Na daga kafa da niyar tafiya kenan, naji karan horn a bayana. Banyi tunanin da ni ake ba daga farko, don haka na daga kafa na fara tafiya. Sai naji an sake a karo na biyu, an kuma kara, na dan juya gefen inda naji karan a kaikaice, gabana naji yayi wata irin faduwa lokacin da muka hada ido da Yaya Bilal. Na kalli gefena domin in tabbatar da cewa ni yake yiwa horn, da dai naga alamun da ni yake, don gashi nan har yanzu ni yake kallo, sai na daga kafa a hankali na tsallaka ta inda ya tsayar da motarshi a bakin titi.
Kofar gidan gaba ya bude min, don haka na silala na shiga a hankali kamar wata mai takatsan-tsan. Nace "Yaya ina yini?".
Yana kokarin tayar da motar ya amsa da, "lafiya lau, daga ina haka?".
Nace "naje ganin supervisor dina ne, amma cikin asibiti zan koma yanzu".
Ya gyada kai tana humming, amma bai sake cewa komi ba, kawai motar naga ya ja ya abinshi.
Kamar yadda na kula da motar shi baka rabata da tattausan kida ko karatu, yau ma tattausar kidan wakar mawaki 'Zayn Malik_Let Me' ce take tashi. Ina son wakokin mutumin sosai. Na kwantar da kaina akan gilashin murfin motar, kamshin turaren Polo na RL da kamshin fresh strawberries na turara mota da kuma sanyin ac dake tashi a cikin motar, yasa na lumshe idanuna. Wata irin natsuwa dana rasa daga ina take naji tana shigata, naji kamar ana zare min duk wata gajiyar dake jikina. Ban san lokacin da barci ya fara daukata ba.
Sai da wani irin awkard feeling ya dameni a bayan kaina sannan, irin wannan feeling din da zaka ji idanu a kanka, kallo kuma na kurilla. Na tuna wata rana lokacin daya daukoni daga gidanshi, irin wadannan abubuwan na dinga ji har na dinga tunanin ko kuma kawai ina imagining hakan ne.
A hankali na saci kallon inda yake, karaf sai muka hada ido. Yayi saurin janye idanunshi daga kaina ya maida kan titi, sai dai ba'a jima ba muka sake hada wani idon dai.
Wannan karon ni na janye nawa idanun da sauri, na maida su na rufe, ban sake dagowa ba.
Tafiya da Yaya Bilal a rufi daya na mota ba yau muka fara yinshi ba, tun muna SBRS ya sha zuwa ya daukemu muje muyi hutun karshen mako a Kaduna, haka ma bayan mun dawo Zaria. Duk da cewa yawanci tare da Janan muke yin tafiyar, amma akwai daidaikun lokuta da yake rago min hanya daga gidanshi. Amma hakan bata taba faruwa ba, idan ma ta taba ko kuma tana faruwan, ni ban taba kula ba sai a dan wadannan lokuta. Shirun cikin motar yayi yawa, kidan ma ya tsaya cak kamar da can babu shi, it was unsettling.
Cikin sa'a muka karasa asibiti cikin dan kankanin lokaci, da kwatance na kwatanta mishi inda muke, yana gyara parking din motar na fita a sukwane kamar wadda ake mintsila, sai dana maida murfin motar na rufe sannan na leka ta saitin motar ina zuba mishi godiya. Ko jira inji ko ya amsa ko bai amsa banyi ba, na kara gaba kamar zan tashi akan iska saboda sauri.
Na rasa dalilin da yasa Yaya ya kirkiro da wasu irin halaye da bai saba ba sam cikin wadannan kwanakin. Koma dai menene, ni dai ina fata Allah Yasa lafiya.
*
Ranar Juma'ah, har na kwanta da dare kiran wayar Muhammad ya tashe ni, donhaka na daga wayar cikin barcin daya fara daukata, mun kwaso gajiya a asibiti yau.
Maganar daya fara min bayan mun gaisa ne tasa na bude idanuwana sosai, yace "are you ready baby?".
Nace "ready for what?".
Yace "ganina mana baby!! Kin shirya gani na gobe?".
Na tashi zaune sosai akan katifata, nace "da gaske?! Don Allah kada kace min wasa kake yi!".
Yace "kin san babu irin wannan wasan a tsakaninmu baby, da gaske nake. Kin shiryawa gani na gobe?".
Na hau gyada kaina da sauri kamar ina gabanshi, "oh God yes, I'm hella ready!!".
Ya saki yar dariya mai sauti, "yayi kyau. One thing though, ina neman alfarmar kiyi min fahimta mai kyau, ki kuma fahimci kyakkyawar manufata a gareki. Don Allah idan na bayyana miki kaina Na'ilah, kada ki guje ni!".
Tunda muke dashi yau ne karo na farko da naji ainihin sunana ya fita daga fatar bakinshi, naji jikina yayi sanyi, nasan he's serious. Nace "in shaa Allah Muhammad, zan yi iyaka kokarina".
Yace "good, and no matter what kada ki manta cewa ina son ki Baby".
Sai kuma naji gabana yana duka sosai, maganganunshi suke nema su tayar min da hankali, nace "wani abu yana faruwa ne Muhammad? Kana tsorata ni!".
Yace "babu abinda ya faru baby, ki kuma kwantar da hankalinki. Am sorry idan yanayin halayena suna tsorata ki, I couldn't help myself".
Sai muka yi shiru, kamar wasu wadanda aka wa rasuwa, can kuma sai yayi gyaran murya, yace "don't mind me fa, insecurities ne irin nawa, amma babu komi we are safe. Saboda haka ki koma barcinki yadda zaki tashi da wuri kin shirya delicacies na tara na, tuwo za'a dafa min ne ko kuma shinkafa?!".
Nan da nan na warware, muka fara magana akan abinda ya dace in tanadar mishi. Sai daya tabbatar da cewa na ware, sannan ya min sallama, bakinshi yana kara nanata min kalamomin so da kauna.
Muna gama wayar na koma na kwanta tare da janyo filo na rungume a kirjina, zuciyata cike da farinciki mara misaltuwa. Gobe zan ga Muhammadu na!!.
*☆⋆21⋆☆*
Daren ranar nayi barcin da ban taba yin irinsa ba koda wasa, cike da mafarkai masu dadi wasu kuma very weird.
Abu na farko daya fara fado min a cikin raina lokacin dana farka daga barcin daya daukeni bayan nayi sallar asubahi shine, 'what a ridiculous dream!', wani irin mafarki dana rasa gane kanshi balle gindinshi. A ganina meye hadin biri da kaska?! Na yakitar da wannan mafarki domin kwata-kwata bai ma yi kama da abinda zan kasa a cikin raina ya dameni a banza a wofi ba.
Tunda na tashi da safe na rasa inda zanyi da raina saboda murna da jindadi. I practically glowed all day. Tun da safe na gama duk wasu abubuwa daya kamata inyi, nayi wankin kayan uniform dina, bayan sun bushe na goge su na ajiye, sannan na kara gyara kayana.
Munyi dashi akan sai yammaci likis sannan zai zo, ban san abinda yakamata in mishi ba wanda zai ci ba, don haka bayan na gama wanki na hada meat pie wanda nayi filling da minced meat har da su carrots da dankalin turawa. Na hada mishi zobo hadadde saboda in dai harkar hada drinks ne musamman na gargajiya, ni kaina nasan cewa na iya sosai. Mawuyaci ne wanda ya sha ya kushe. Bayan nan na sayo lemun exotic na abarba da kwakwa da ruwan cikin gora, na kaishi dakin wata yar ajinmu da take da firjin na roketa ta ajiye min zuwa anjima da yamma yadda zai yi sanyi, tace babu damuwa.
Gabadaya na kasa zaune na kasa tsaye, motsi kadan na lalubo waya, ko in duba lokaci ko kuma in turawa Muhammad text. Ji nake kamar in janyo yinin ranar saboda nisan da naga yayi min.
Karfe hudu na yammacin ranar, ina zaune a gefen kujerata ina nade gashin kaina. Jiya na warware kalbar kalbar sallah da Janan ta min, na je saloon na wanke shi. Yanzu dana taje shi sai ya zubo har gadon bayana, yana ta sheki da tashin kamshin shampoo. Da yake ban cika son nuna gashi a waje ba, sai nake nade kayana in saka cikin dakwali ko hula.
Wata bugaggiyar doguwar rigar atamfa ce na saka, irin dinkin yan Senegale dinnan ne. Atamfar kanta yar can ce, wata tafiya da Yaya Mudatthir yayi zuwa can gudanar da wani aiki, ya kawo min ita a dinkenta. Sau daya kacal na taba sakata. Dinkin zanen single ne, rigar kuma kamar half buba dinnan ce, data tsaya min a gwiwa, dankwalin mai fadi ne sosai, na kashe daurin Zara Buhari a kan nawa. Dana tsayawa karewa kaina kallo a madubi, ni kaina sai dana burge kaina. Allah ya azurtani da baiwar wani irin tattausan kyawu, irin kyawun nan da ba'a gani kai tsaye, sai a hankali a hankali yake fita. Wai a hakan ma don ba wata kwalliyar kirki nayi ba, hoda kawai na shafa tare da murza kwalli a idanuna, nayi amfani da brush na taje gashin girata, daga shi ban kara komi ba.
Abinda Esther ta dinga yiwa korafi kenan, tace in zo ta min kwalliya ko da simple one ce, "bai kamata ki je wa saurayin da zaku hadu dashi yau a karo na farko haka ba, ba kya tsoron yaji baya yi dake?".
Na daga kafa da niyar tafiya kenan, naji karan horn a bayana. Banyi tunanin da ni ake ba daga farko, don haka na daga kafa na fara tafiya. Sai naji an sake a karo na biyu, an kuma kara, na dan juya gefen inda naji karan a kaikaice, gabana naji yayi wata irin faduwa lokacin da muka hada ido da Yaya Bilal. Na kalli gefena domin in tabbatar da cewa ni yake yiwa horn, da dai naga alamun da ni yake, don gashi nan har yanzu ni yake kallo, sai na daga kafa a hankali na tsallaka ta inda ya tsayar da motarshi a bakin titi.
Kofar gidan gaba ya bude min, don haka na silala na shiga a hankali kamar wata mai takatsan-tsan. Nace "Yaya ina yini?".
Yana kokarin tayar da motar ya amsa da, "lafiya lau, daga ina haka?".
Nace "naje ganin supervisor dina ne, amma cikin asibiti zan koma yanzu".
Ya gyada kai tana humming, amma bai sake cewa komi ba, kawai motar naga ya ja ya abinshi.
Kamar yadda na kula da motar shi baka rabata da tattausan kida ko karatu, yau ma tattausar kidan wakar mawaki 'Zayn Malik_Let Me' ce take tashi. Ina son wakokin mutumin sosai. Na kwantar da kaina akan gilashin murfin motar, kamshin turaren Polo na RL da kamshin fresh strawberries na turara mota da kuma sanyin ac dake tashi a cikin motar, yasa na lumshe idanuna. Wata irin natsuwa dana rasa daga ina take naji tana shigata, naji kamar ana zare min duk wata gajiyar dake jikina. Ban san lokacin da barci ya fara daukata ba.
Sai da wani irin awkard feeling ya dameni a bayan kaina sannan, irin wannan feeling din da zaka ji idanu a kanka, kallo kuma na kurilla. Na tuna wata rana lokacin daya daukoni daga gidanshi, irin wadannan abubuwan na dinga ji har na dinga tunanin ko kuma kawai ina imagining hakan ne.
A hankali na saci kallon inda yake, karaf sai muka hada ido. Yayi saurin janye idanunshi daga kaina ya maida kan titi, sai dai ba'a jima ba muka sake hada wani idon dai.
Wannan karon ni na janye nawa idanun da sauri, na maida su na rufe, ban sake dagowa ba.
Tafiya da Yaya Bilal a rufi daya na mota ba yau muka fara yinshi ba, tun muna SBRS ya sha zuwa ya daukemu muje muyi hutun karshen mako a Kaduna, haka ma bayan mun dawo Zaria. Duk da cewa yawanci tare da Janan muke yin tafiyar, amma akwai daidaikun lokuta da yake rago min hanya daga gidanshi. Amma hakan bata taba faruwa ba, idan ma ta taba ko kuma tana faruwan, ni ban taba kula ba sai a dan wadannan lokuta. Shirun cikin motar yayi yawa, kidan ma ya tsaya cak kamar da can babu shi, it was unsettling.
Cikin sa'a muka karasa asibiti cikin dan kankanin lokaci, da kwatance na kwatanta mishi inda muke, yana gyara parking din motar na fita a sukwane kamar wadda ake mintsila, sai dana maida murfin motar na rufe sannan na leka ta saitin motar ina zuba mishi godiya. Ko jira inji ko ya amsa ko bai amsa banyi ba, na kara gaba kamar zan tashi akan iska saboda sauri.
Na rasa dalilin da yasa Yaya ya kirkiro da wasu irin halaye da bai saba ba sam cikin wadannan kwanakin. Koma dai menene, ni dai ina fata Allah Yasa lafiya.
*
Ranar Juma'ah, har na kwanta da dare kiran wayar Muhammad ya tashe ni, donhaka na daga wayar cikin barcin daya fara daukata, mun kwaso gajiya a asibiti yau.
Maganar daya fara min bayan mun gaisa ne tasa na bude idanuwana sosai, yace "are you ready baby?".
Nace "ready for what?".
Yace "ganina mana baby!! Kin shirya gani na gobe?".
Na tashi zaune sosai akan katifata, nace "da gaske?! Don Allah kada kace min wasa kake yi!".
Yace "kin san babu irin wannan wasan a tsakaninmu baby, da gaske nake. Kin shiryawa gani na gobe?".
Na hau gyada kaina da sauri kamar ina gabanshi, "oh God yes, I'm hella ready!!".
Ya saki yar dariya mai sauti, "yayi kyau. One thing though, ina neman alfarmar kiyi min fahimta mai kyau, ki kuma fahimci kyakkyawar manufata a gareki. Don Allah idan na bayyana miki kaina Na'ilah, kada ki guje ni!".
Tunda muke dashi yau ne karo na farko da naji ainihin sunana ya fita daga fatar bakinshi, naji jikina yayi sanyi, nasan he's serious. Nace "in shaa Allah Muhammad, zan yi iyaka kokarina".
Yace "good, and no matter what kada ki manta cewa ina son ki Baby".
Sai kuma naji gabana yana duka sosai, maganganunshi suke nema su tayar min da hankali, nace "wani abu yana faruwa ne Muhammad? Kana tsorata ni!".
Yace "babu abinda ya faru baby, ki kuma kwantar da hankalinki. Am sorry idan yanayin halayena suna tsorata ki, I couldn't help myself".
Sai muka yi shiru, kamar wasu wadanda aka wa rasuwa, can kuma sai yayi gyaran murya, yace "don't mind me fa, insecurities ne irin nawa, amma babu komi we are safe. Saboda haka ki koma barcinki yadda zaki tashi da wuri kin shirya delicacies na tara na, tuwo za'a dafa min ne ko kuma shinkafa?!".
Nan da nan na warware, muka fara magana akan abinda ya dace in tanadar mishi. Sai daya tabbatar da cewa na ware, sannan ya min sallama, bakinshi yana kara nanata min kalamomin so da kauna.
Muna gama wayar na koma na kwanta tare da janyo filo na rungume a kirjina, zuciyata cike da farinciki mara misaltuwa. Gobe zan ga Muhammadu na!!.
*☆⋆21⋆☆*
Daren ranar nayi barcin da ban taba yin irinsa ba koda wasa, cike da mafarkai masu dadi wasu kuma very weird.
Abu na farko daya fara fado min a cikin raina lokacin dana farka daga barcin daya daukeni bayan nayi sallar asubahi shine, 'what a ridiculous dream!', wani irin mafarki dana rasa gane kanshi balle gindinshi. A ganina meye hadin biri da kaska?! Na yakitar da wannan mafarki domin kwata-kwata bai ma yi kama da abinda zan kasa a cikin raina ya dameni a banza a wofi ba.
Tunda na tashi da safe na rasa inda zanyi da raina saboda murna da jindadi. I practically glowed all day. Tun da safe na gama duk wasu abubuwa daya kamata inyi, nayi wankin kayan uniform dina, bayan sun bushe na goge su na ajiye, sannan na kara gyara kayana.
Munyi dashi akan sai yammaci likis sannan zai zo, ban san abinda yakamata in mishi ba wanda zai ci ba, don haka bayan na gama wanki na hada meat pie wanda nayi filling da minced meat har da su carrots da dankalin turawa. Na hada mishi zobo hadadde saboda in dai harkar hada drinks ne musamman na gargajiya, ni kaina nasan cewa na iya sosai. Mawuyaci ne wanda ya sha ya kushe. Bayan nan na sayo lemun exotic na abarba da kwakwa da ruwan cikin gora, na kaishi dakin wata yar ajinmu da take da firjin na roketa ta ajiye min zuwa anjima da yamma yadda zai yi sanyi, tace babu damuwa.
Gabadaya na kasa zaune na kasa tsaye, motsi kadan na lalubo waya, ko in duba lokaci ko kuma in turawa Muhammad text. Ji nake kamar in janyo yinin ranar saboda nisan da naga yayi min.
Karfe hudu na yammacin ranar, ina zaune a gefen kujerata ina nade gashin kaina. Jiya na warware kalbar kalbar sallah da Janan ta min, na je saloon na wanke shi. Yanzu dana taje shi sai ya zubo har gadon bayana, yana ta sheki da tashin kamshin shampoo. Da yake ban cika son nuna gashi a waje ba, sai nake nade kayana in saka cikin dakwali ko hula.
Wata bugaggiyar doguwar rigar atamfa ce na saka, irin dinkin yan Senegale dinnan ne. Atamfar kanta yar can ce, wata tafiya da Yaya Mudatthir yayi zuwa can gudanar da wani aiki, ya kawo min ita a dinkenta. Sau daya kacal na taba sakata. Dinkin zanen single ne, rigar kuma kamar half buba dinnan ce, data tsaya min a gwiwa, dankwalin mai fadi ne sosai, na kashe daurin Zara Buhari a kan nawa. Dana tsayawa karewa kaina kallo a madubi, ni kaina sai dana burge kaina. Allah ya azurtani da baiwar wani irin tattausan kyawu, irin kyawun nan da ba'a gani kai tsaye, sai a hankali a hankali yake fita. Wai a hakan ma don ba wata kwalliyar kirki nayi ba, hoda kawai na shafa tare da murza kwalli a idanuna, nayi amfani da brush na taje gashin girata, daga shi ban kara komi ba.
Abinda Esther ta dinga yiwa korafi kenan, tace in zo ta min kwalliya ko da simple one ce, "bai kamata ki je wa saurayin da zaku hadu dashi yau a karo na farko haka ba, ba kya tsoron yaji baya yi dake?".