Sashe 79
A Zato Na Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ta rausayar da kanta gefe guda, "to shikenan ai tunda haka kika ce. Zaki ci abinci?".
Ta watso min tambayar tana nufar kulolin dake ajiye a wajen wadanda yawanci abokan aikina ne na nan suka kawo min su, nasan duk don ta dauke hankalina daga kan zancen ne. Murmushi kawai nayi na gyada mata kai.
[Hello there! 😽].
*☆⋆45⋆☆*
Kwana na biyu ina hutawa a gadon asibiti. Bayan an tabbatar da lafiyata da komi, aka sallamomu muka koma gida. A ranar Janan ta koma Kaduna ina ta mata godiya.
Sai dana kara kwanaki uku ina kara hutawa, sannan na koma bakin aikina na kuma karbi girki. Rayuwa ta koma normal, mun maida komai bayanmu mun fuskanci gabanmu.
Zaune muke gabadayanmu a falon Yaya da misalin karfe tara na dare. Yanzu har Raheemah ta kan fito ayi hira da ita, kafin dare yayi kowa ya nemi makwancinsa kuma.
Na fahimci Yaya a mutum mai son karfafa zumunci da son kusanci ga iyalinshi, hakan yana kara min girmanshi da kimarshi da nake gani a cikin idanuna. Duk da cewa ta fanninsu, ba hakan suke so ba.
Na tashi na shiga kicin, fruit salad din dana hada yayi sanyi karara, na dauko forks guda hudu, na koma falon. A tsakiyarmu na ajiyeshi tare da ajiye cokulan masu yatsu, muka fara shan fruits din aka kuma cigaba da hira. Sai dai hirar kamar kowacce tata kawai take yi, idan Yaya yana hira da daya, baka ji biyun sun sanya baki sai dai su kalli TV ko kuma suyi shiru da bakinsu. Duk yadda yaso ya saka mu cikin hirar gabadaya abin gagara yayi, idan ma ya sanya bakin wata a cikin hirar ta danyi magana, sai ita dayar kuma tayi kim da baki, sai ta jira sun gama hirar sannan ta sako wata. Abin gwanin ban dariya, na dai yi ta kokarin makale tawa a ciki.
Duk da cewa a hakan ma ba karamin kokari yayi ba, tun da yanzu har mu kan zauna mu duka a waje daya ba tare da kaji kananan maganganu suna tashi ba. A ganina hakan kamar an fara daukar matakin farko kenan wajen hade kai.
Sai dai, tunda na dawo daga asibiti, wani shiru da matan suka yi su duka, yanzu babu bataccen girki idan nayi, Ameerah ta daina shiga dakin Yaya tunda safe, haka ita kanta Raheemah ta daina wannan yawan mitar tata. Jikina kawai yana bani ba daidai ba. Sai inji kamar shirun nan nasu, 'silence before the storm' ne.
Ko kuwa sun fara shiryuwa ne??.
Kadan-kadan Ameerah ta fara yatsina fuska, tun ana yi babu wanda ya kula har Yaya ya lura, ya kalleta cike da alamar tambaya, "lafiya, baki jin dadi ne?".
Duk sai muka juya hankulanmu kansu.
Ta girgiza kai a hankali, "cikina nake ji yana juyawa... Kamar zanyi amai...".
Tana rufe baki, ta tashi a sukwane tayi dakin Yaya, mu duka ukun muka tsaya muna kallon-kallo, kafin muka tashi da sauri muka bi bayanta.
Tana cikin bandaki tana ta kakarin amai, Yaya ya matsa da sauri ya tattagota suka dawo dakin, daga shi har mu sannu muke jera mata wanda take amsawa cikin jan numfashi. Muka rankaya muka koma falo muka zauna.
Muna zama ta fara wani kakarin da yatsina fuska, Yaya yace "wai wani abu yana damunki ne?".
Tana daga baki, sai cewa tayi, "ai ita warin kankana ne yake tada mata hankali".
Na daga girata sama cikin tsananin mamaki, Raheemah kam sai ta kama baki. Yaya yace in dauke farantin in maida kicin tunda mun gama shan fruits din. Ban ce komi ba na dauke kayan, a raina ina nanata ikon Allah kenan mai rike zariyar wando.
Na koma muka cigaba da hirarmu, har lokacin kwanciya barci yayi duk muka tashi. Na koma dakina nayi shirin barci, na koma dakin Yaya.
Cikin dare kawai sai karan waya muka ji, Ameerah ce wai cikinta ya dameta da ciwo. Nan muka nufi dakinta muka sameta tana ta birgima akan gado. Yaya yace min "ko kina da maganin ciwon ciki ne ki bata ta sha?".
Nan na koma daki na lalubo maganin boskafone na koma dakin bayan na biya ta kicin na dauko ruwa mara sanyi.
Nan na sameta kwance shame-shame a jikin Yaya. Ban ce musu komi ba, na mika mishi maganin, ya tallafo kanta zai bata maganin, nan tayi fir tace ba zata sha ba.
Yaya ya fara aikin lallashi, amma ta kafe.
Cikin nuna alamun gajiya da halinta yace "kinsan ba neman magani kike yi ba, zaki tado ni da tsakiyar wannan daren, idan ba zaki sha maganin ba zan tafi in kyaleki yanzu wallahi".
Sannan fa ta karba ta sha. Har wajen karfe hudu na dare muna kanta. Ni naki tafiya daki duk da sai da Yaya yace in tafi, ban san ko ciwon gaske take yi ko na karya ba. Sai da aka fara kiran assalatu sannan barci ya dauketa. Sai lokacin muka koma daki.
Bayan kwana biyu da yin haka, sai gata wai taje likita ya aunata ance tana da ciki. Nan suka hau murnarsu ita da Yaya, na bisu da addu'ar Allah ya raba lafiya. Wani abin mamakin shine, yanayinta sam bai yi kama dana masu ciki ba. Yadda take da, haka take yanzu, babu canjin komi a tattare da ita. Hakan yasa na fara tunanin anya ba cikin karya bane ba kuwa? Sai dai a yadda Yaya yake ta doki da rawar jiki akan cikin wannan, nasan ko giyar wake na sha ba zan fito in ce mishi ga abinda ake ciki ba. Don haka na kawo idanu na zuba musu, koma dai menene, nasan it's only a matter of time, zamu ga ciki dai ya bayyana ai ko?.
Ranar nan ina jinsu ita da Raheemah suna gabzawa, ranar Adi tazo gidan ta wuni, a cewarsu itama ta samu wani house of rep dake zaune anan Abujar har an sanya musu ranar aure. Ina tunanin Adin ce ta fada mata kamar ba cikine da Ameerah ba.
Sai gata ta tsareta a kicin, ta kare mata zagi tas, tace "kuma idan karyar cikine zamu zuba ni da mutum anan gidan mu gani. Haba, biri yayi kama da mutum! Ke da kike da ciki, maimakon ki dinga yin kiba ko rama, amma kina nan a yadda kike? To wallahi mu zuba don uban mutum, zamu ga karshen karya!".
Ta fita daga kicin din ta bar Ameerah tana ihun "tunda ita take bada cikin, ta riga ta san babu shi, ba sai ta fadawa Yayan ba?".
Ban ce musu komi ba ni kam sai kai dana dinga girgizawa. Su dai suka sani ai.
Ranar assabar a Kaduna na wuni, Yaya zai shigo su gaisa dasu Ummah, don haka nima na biyo shi. A gidan su Ummahn muka fara sauka, duk da sunyi murna da ganina, hakan bai hana su min fadan mai ya kaini fara yawo yanzu ba, jikina har yayi karfin da zan fara yawo ne? Nace musu lafiyata lau, na warke.
Bayan mun gaisa dasu na huta, na tafi gidan Janan. Nan muka wuni muna hira da hirar yaushe gamo.
Lokacin dana mata zancen cikin Ameerah, dariya ta dinga kyalkyalawa har sai data kifa daga kan kujera. Na bita da kallo ina dan murmushi duk da bansan akan meye take dariyar ba. Sai data yi ta isheta, sannan ta dago idanu taf da hawaye don dariya, tace "yanzu kuma Yaya ya yarda da wannan crap din??".
Nace "me zai hana shi yarda?".
Tace "haba, tun yaushe suke zarya wajen likitoci ana cewa kwayoyin haihuwarta basu da kwari? Wace kasa ce basu je ba akan wannan matsalar amma magana daya, ba zata iya conceiving ba. Kila dai Yaya mantawa yayi, ko kuma tsabar son yara ne yasa idanunshi suka rufe. Amma daga ma jin labarin da kika bani, ko rantsuwa nayi nasan ba zata taba ci na ba, cikin karya ne!".
Nayi shiru ina processing abinda tace, daga karshe na daga kafada, nace "kika san ko Allah ne ya dubeta da rahamar shi? Shi ikon Allah ai yawa ne dashi. Idan ma ba hakan bane, wannan matsalarta ce, ina zaune a gefe daya koma menene zai bayyana. Shi ciki ai ba'a boye sa, dole zai fito kowa ya gani".
Janan ta gyada kai, "haka ne kam. Allah dai ya rufa mana asiri bakidayanmu". Nace "ameen".
Da yamma da Yaya ya gama ziyararshi, ya biyo muka juya bayan sun gaisa da Janan da mijinta Almustapha. Ashe har Zaria yaje, sai a hanya yake fada min.
Kafin mu karasa gida sai da muka biya wani fast food joint, ya sai roll cakes, tarkacen hamburger, ice creams dasu chocolate, sakon Ameerah. Muna komawa na kwashi kasona na fada daki saboda girkin Ameerah ne ranar. Sai ya zama wadannan su muka ci abinci matsayin abincin dare, saboda apparently bata da karfin yin girki ranar.
Sai abin yazo ya zama kamar al'ada Yawancin ranakun girkinta sai dai Yaya yayo odar abinci.
Nace mishi me zai sa maimakon yayi ta asarar kudi wajen siyo abinci, mu dinga girka kayanmu duk ranar da taji ba zata iya yin girki ba? Sai cewa yayi idan aka yi hakan, za'a bata mishi tsari da dokar gidanshi. Da na matsa, sai yayi kici-kicin da rai, yace "wai idan ma na batar da kudin, kudina ne ko naki?".
Mamaki ya kama ni, na kama baki nace "daga maganar gaskiya? To Allah ya baka hakuri!". Na tashi na koma dakina.
Can kuma sai gashi ya biyo bayana, wai inyi hakuri, kawai yaga yana kokarin dauke mana wahala ne amma kamar bamu gani, maimakon mu mishi godiya, sai mu hau korafi, waye da waye, nan ma dai na kara bashi hakuri aka wuce wajen.
To rayuwar fa kenan, yau dadi, gobe akasinsa.
Kamar yadda duk kokarin mutum wajen kaucewa kaddarar data riga fata, duk gudunka da fata da burinka, baka da wani katabus akan abinda Allah ya kaddara. Shi yasa ita yarda da kaddara take da matukar kyau. Ko babu komi, kowani irin abu ne ya kan zo wa wanda ya yarda babu abinda yake faruwa a doron kasa face da izinin Allah, da sauki.
Ta watso min tambayar tana nufar kulolin dake ajiye a wajen wadanda yawanci abokan aikina ne na nan suka kawo min su, nasan duk don ta dauke hankalina daga kan zancen ne. Murmushi kawai nayi na gyada mata kai.
[Hello there! 😽].
*☆⋆45⋆☆*
Kwana na biyu ina hutawa a gadon asibiti. Bayan an tabbatar da lafiyata da komi, aka sallamomu muka koma gida. A ranar Janan ta koma Kaduna ina ta mata godiya.
Sai dana kara kwanaki uku ina kara hutawa, sannan na koma bakin aikina na kuma karbi girki. Rayuwa ta koma normal, mun maida komai bayanmu mun fuskanci gabanmu.
Zaune muke gabadayanmu a falon Yaya da misalin karfe tara na dare. Yanzu har Raheemah ta kan fito ayi hira da ita, kafin dare yayi kowa ya nemi makwancinsa kuma.
Na fahimci Yaya a mutum mai son karfafa zumunci da son kusanci ga iyalinshi, hakan yana kara min girmanshi da kimarshi da nake gani a cikin idanuna. Duk da cewa ta fanninsu, ba hakan suke so ba.
Na tashi na shiga kicin, fruit salad din dana hada yayi sanyi karara, na dauko forks guda hudu, na koma falon. A tsakiyarmu na ajiyeshi tare da ajiye cokulan masu yatsu, muka fara shan fruits din aka kuma cigaba da hira. Sai dai hirar kamar kowacce tata kawai take yi, idan Yaya yana hira da daya, baka ji biyun sun sanya baki sai dai su kalli TV ko kuma suyi shiru da bakinsu. Duk yadda yaso ya saka mu cikin hirar gabadaya abin gagara yayi, idan ma ya sanya bakin wata a cikin hirar ta danyi magana, sai ita dayar kuma tayi kim da baki, sai ta jira sun gama hirar sannan ta sako wata. Abin gwanin ban dariya, na dai yi ta kokarin makale tawa a ciki.
Duk da cewa a hakan ma ba karamin kokari yayi ba, tun da yanzu har mu kan zauna mu duka a waje daya ba tare da kaji kananan maganganu suna tashi ba. A ganina hakan kamar an fara daukar matakin farko kenan wajen hade kai.
Sai dai, tunda na dawo daga asibiti, wani shiru da matan suka yi su duka, yanzu babu bataccen girki idan nayi, Ameerah ta daina shiga dakin Yaya tunda safe, haka ita kanta Raheemah ta daina wannan yawan mitar tata. Jikina kawai yana bani ba daidai ba. Sai inji kamar shirun nan nasu, 'silence before the storm' ne.
Ko kuwa sun fara shiryuwa ne??.
Kadan-kadan Ameerah ta fara yatsina fuska, tun ana yi babu wanda ya kula har Yaya ya lura, ya kalleta cike da alamar tambaya, "lafiya, baki jin dadi ne?".
Duk sai muka juya hankulanmu kansu.
Ta girgiza kai a hankali, "cikina nake ji yana juyawa... Kamar zanyi amai...".
Tana rufe baki, ta tashi a sukwane tayi dakin Yaya, mu duka ukun muka tsaya muna kallon-kallo, kafin muka tashi da sauri muka bi bayanta.
Tana cikin bandaki tana ta kakarin amai, Yaya ya matsa da sauri ya tattagota suka dawo dakin, daga shi har mu sannu muke jera mata wanda take amsawa cikin jan numfashi. Muka rankaya muka koma falo muka zauna.
Muna zama ta fara wani kakarin da yatsina fuska, Yaya yace "wai wani abu yana damunki ne?".
Tana daga baki, sai cewa tayi, "ai ita warin kankana ne yake tada mata hankali".
Na daga girata sama cikin tsananin mamaki, Raheemah kam sai ta kama baki. Yaya yace in dauke farantin in maida kicin tunda mun gama shan fruits din. Ban ce komi ba na dauke kayan, a raina ina nanata ikon Allah kenan mai rike zariyar wando.
Na koma muka cigaba da hirarmu, har lokacin kwanciya barci yayi duk muka tashi. Na koma dakina nayi shirin barci, na koma dakin Yaya.
Cikin dare kawai sai karan waya muka ji, Ameerah ce wai cikinta ya dameta da ciwo. Nan muka nufi dakinta muka sameta tana ta birgima akan gado. Yaya yace min "ko kina da maganin ciwon ciki ne ki bata ta sha?".
Nan na koma daki na lalubo maganin boskafone na koma dakin bayan na biya ta kicin na dauko ruwa mara sanyi.
Nan na sameta kwance shame-shame a jikin Yaya. Ban ce musu komi ba, na mika mishi maganin, ya tallafo kanta zai bata maganin, nan tayi fir tace ba zata sha ba.
Yaya ya fara aikin lallashi, amma ta kafe.
Cikin nuna alamun gajiya da halinta yace "kinsan ba neman magani kike yi ba, zaki tado ni da tsakiyar wannan daren, idan ba zaki sha maganin ba zan tafi in kyaleki yanzu wallahi".
Sannan fa ta karba ta sha. Har wajen karfe hudu na dare muna kanta. Ni naki tafiya daki duk da sai da Yaya yace in tafi, ban san ko ciwon gaske take yi ko na karya ba. Sai da aka fara kiran assalatu sannan barci ya dauketa. Sai lokacin muka koma daki.
Bayan kwana biyu da yin haka, sai gata wai taje likita ya aunata ance tana da ciki. Nan suka hau murnarsu ita da Yaya, na bisu da addu'ar Allah ya raba lafiya. Wani abin mamakin shine, yanayinta sam bai yi kama dana masu ciki ba. Yadda take da, haka take yanzu, babu canjin komi a tattare da ita. Hakan yasa na fara tunanin anya ba cikin karya bane ba kuwa? Sai dai a yadda Yaya yake ta doki da rawar jiki akan cikin wannan, nasan ko giyar wake na sha ba zan fito in ce mishi ga abinda ake ciki ba. Don haka na kawo idanu na zuba musu, koma dai menene, nasan it's only a matter of time, zamu ga ciki dai ya bayyana ai ko?.
Ranar nan ina jinsu ita da Raheemah suna gabzawa, ranar Adi tazo gidan ta wuni, a cewarsu itama ta samu wani house of rep dake zaune anan Abujar har an sanya musu ranar aure. Ina tunanin Adin ce ta fada mata kamar ba cikine da Ameerah ba.
Sai gata ta tsareta a kicin, ta kare mata zagi tas, tace "kuma idan karyar cikine zamu zuba ni da mutum anan gidan mu gani. Haba, biri yayi kama da mutum! Ke da kike da ciki, maimakon ki dinga yin kiba ko rama, amma kina nan a yadda kike? To wallahi mu zuba don uban mutum, zamu ga karshen karya!".
Ta fita daga kicin din ta bar Ameerah tana ihun "tunda ita take bada cikin, ta riga ta san babu shi, ba sai ta fadawa Yayan ba?".
Ban ce musu komi ba ni kam sai kai dana dinga girgizawa. Su dai suka sani ai.
Ranar assabar a Kaduna na wuni, Yaya zai shigo su gaisa dasu Ummah, don haka nima na biyo shi. A gidan su Ummahn muka fara sauka, duk da sunyi murna da ganina, hakan bai hana su min fadan mai ya kaini fara yawo yanzu ba, jikina har yayi karfin da zan fara yawo ne? Nace musu lafiyata lau, na warke.
Bayan mun gaisa dasu na huta, na tafi gidan Janan. Nan muka wuni muna hira da hirar yaushe gamo.
Lokacin dana mata zancen cikin Ameerah, dariya ta dinga kyalkyalawa har sai data kifa daga kan kujera. Na bita da kallo ina dan murmushi duk da bansan akan meye take dariyar ba. Sai data yi ta isheta, sannan ta dago idanu taf da hawaye don dariya, tace "yanzu kuma Yaya ya yarda da wannan crap din??".
Nace "me zai hana shi yarda?".
Tace "haba, tun yaushe suke zarya wajen likitoci ana cewa kwayoyin haihuwarta basu da kwari? Wace kasa ce basu je ba akan wannan matsalar amma magana daya, ba zata iya conceiving ba. Kila dai Yaya mantawa yayi, ko kuma tsabar son yara ne yasa idanunshi suka rufe. Amma daga ma jin labarin da kika bani, ko rantsuwa nayi nasan ba zata taba ci na ba, cikin karya ne!".
Nayi shiru ina processing abinda tace, daga karshe na daga kafada, nace "kika san ko Allah ne ya dubeta da rahamar shi? Shi ikon Allah ai yawa ne dashi. Idan ma ba hakan bane, wannan matsalarta ce, ina zaune a gefe daya koma menene zai bayyana. Shi ciki ai ba'a boye sa, dole zai fito kowa ya gani".
Janan ta gyada kai, "haka ne kam. Allah dai ya rufa mana asiri bakidayanmu". Nace "ameen".
Da yamma da Yaya ya gama ziyararshi, ya biyo muka juya bayan sun gaisa da Janan da mijinta Almustapha. Ashe har Zaria yaje, sai a hanya yake fada min.
Kafin mu karasa gida sai da muka biya wani fast food joint, ya sai roll cakes, tarkacen hamburger, ice creams dasu chocolate, sakon Ameerah. Muna komawa na kwashi kasona na fada daki saboda girkin Ameerah ne ranar. Sai ya zama wadannan su muka ci abinci matsayin abincin dare, saboda apparently bata da karfin yin girki ranar.
Sai abin yazo ya zama kamar al'ada Yawancin ranakun girkinta sai dai Yaya yayo odar abinci.
Nace mishi me zai sa maimakon yayi ta asarar kudi wajen siyo abinci, mu dinga girka kayanmu duk ranar da taji ba zata iya yin girki ba? Sai cewa yayi idan aka yi hakan, za'a bata mishi tsari da dokar gidanshi. Da na matsa, sai yayi kici-kicin da rai, yace "wai idan ma na batar da kudin, kudina ne ko naki?".
Mamaki ya kama ni, na kama baki nace "daga maganar gaskiya? To Allah ya baka hakuri!". Na tashi na koma dakina.
Can kuma sai gashi ya biyo bayana, wai inyi hakuri, kawai yaga yana kokarin dauke mana wahala ne amma kamar bamu gani, maimakon mu mishi godiya, sai mu hau korafi, waye da waye, nan ma dai na kara bashi hakuri aka wuce wajen.
To rayuwar fa kenan, yau dadi, gobe akasinsa.
Kamar yadda duk kokarin mutum wajen kaucewa kaddarar data riga fata, duk gudunka da fata da burinka, baka da wani katabus akan abinda Allah ya kaddara. Shi yasa ita yarda da kaddara take da matukar kyau. Ko babu komi, kowani irin abu ne ya kan zo wa wanda ya yarda babu abinda yake faruwa a doron kasa face da izinin Allah, da sauki.