Sashe 35
A Zato Na Complete Hausa Novel · about 8 min read
Kamar yadda nayi tunani, maganar kudin jarabawa bata zo min da dadi ba. Yadda Baba ya rufe ido yana masifar shi bashi da kudi, ina nema in tatuke shi, abin ya bani mamaki. Tun bayan kudin school fees daya turo min, naira dubu goma ta sake hada ni dashi. Yanzu kusan wata na biyu kenan a Zaria, amma ba halin in daga baki inyi maganar kudi sai ya hau zagina. Ko provision yawanci Yaya ne yake turo min su, sai kuwa kudin da yake turo min jifa-jifa, dasu nake amfani in sayi kayan bukata. Bayan doguwar wayar da muka yi dashi a ranar Assabar kenan, daki na koma na kwanta. Esther ta tafi weekend gidan kawunta, Maimunah kuma bata ma dakin tun jiya, babu wanda yasan inda ta tafi. Don haka ni kadai na kwana a daki.
Nayi lamo akan katifa cikin tunani iri-iri, kala-kala, ban taba jin karatun nan ya fita a raina ba sai yau. A raina na raya wai da wanne ake so inji ne? Abu ne da bai taka kara ya karya ba, wanda na tabbata yafi karfin Baba, amma kullum cikin ja wa kanshi babu yake, kullum babu, kuma babun a kaina kadai take.
Yawancin matsaloli irin haka idan suka taso dama sai dai in tuntubi Yaya da maganar, idan bata fi karfinshi ba ya maganceta, in kuma tafi sai ya kai ga dangana da su Malam. To ita kuma rayuwa ba zai yiwu taci gaba a haka ba, ba zai yiwu ace kai kullum cikin bani-bani da a maka-a maka kake ba, kowa ma dama zai ji ya gaji.
Sai dai idan nayi duba ta wani bangaren, sai inga yaushe na cika bani-bani kamar yadda Baba yace? Tsakanina dashi kawai kudin handout ne, sai abinda yaga dama ya dan lafo min ciki kawai. Dama can yawancin hidima da dawainiya Yaya ne yake yi, idan aka samu ya biya school fees da kyar, ya hado min provision, to sauran fa sai dai yadda hali yayi, sai na sha matukar wahala ya kuma yazga ni yadda yaga dama sannan zai turo min na bukatun yau da gobe. To maganar gaskiya na gaji yanzu, yanzu haka kwanciyar da nayi ina tunani, tunanin hada kan kayana nake in koma gida kawai, azabar ta isa.
Sai kuma naga idan ma na koma, ni zan kwari kaina, babu wanda zai ji a jikinsa dai sai ni. Don haka naci gaba da tunani ina laluben mafita. Nasan mafita daya itace in fadawa Yaya, amma gani nake kamar abin yayi yawa. Shi shikenan kullum cikin ji da matsalata, kullum babu hutu?.
Ban tashi daga kwanciyar ba sai da aka kira Sallar azuhur, ashe wani wahalallen barci ne ya daukeni. Wani irin barci mai dauke da wasu irin sarkakkun mafarkai. Na tashi ina mika da hamma, maimakon inji gajiyata ta tafi, sai naji kamar an dauko gajiyar duniya ne an dora min aka. Haka nan na lallaba na watsa ruwa a jikin nawa ya dan min karfi, sannan nazo nayi sallah.
Ina cikin karatu Janan ta kirani. Roko na ta dinga yi akan inje in mata weekend, kai tsaye nace mata a'ah, ta dawo tana magiyar to inje in tayata shan ruwa, nan ma nace a'ah. Ni dai tunda na samu nayi sa'a, Allah ya taimakeni na baro gidan, ai an wuce wurin. Ta gaji tayi fushi ta ajiye wayar. Da yake ba a cikin yanayi mai dadi nake ba, kyaleta nayi kawai.
Yinin ranar haka na yi shi sukuku, can da yamma wai sai ga Maryam, mun gaisa da ita gari-gari, wai in na shiga kasuwa in sayo mata sarka da yan kunne idan ma naga da halin takalmi in karo, naji kamar in hau rusa mata ihu na dai cije nace mata to kawai, na ajiye wayar.
*
Dole kanwar naki haka na dage na kira Yaya zuwa ranar talata, domin duk ta inda na buga abubuwan babu sauki, babu wata mafita. Na zayyane mishi matsalar da muke ciki da Baba, Yayan yayi shiru yana tunani, kafin daga baya yace zai kira shi sai yayi mishi bayani. Na mishi godiya nace to, na kashe wayar.
Allah ya taimakeni cikin satin aka turo mana kudin scholarship da aka saba bamu. Kuka ne kadai banyi ba ranar saboda murna, dama nayi karaf, bani da ko sisi. Haka kayayyakin da suka rage min duk sun tasamma karewa. Yawanci idan aka turo min ina fadawa Baba, amma wannan karon da yake a wuya nake da kowa, babu wanda yaji labari. Kasuwa kawai na fada.
*
Abu wasa-wasa, tun ana yau azumi, har gashi mun zo mun ci tsakiyar shi. Yaya ya samu ya shawo kan Baba da kyar ya turo min kudin, naje na biya. Allah ya taimakeni basu kai ga rufewa ba. Abubuwa zuwa yanzu sun yi min sauki nesa ba kusa ba, ba kamar satin daya gabata ba. Ban bar wannan abin ya dameni ba ko kuma ya hana ni aikata abubuwana na yau da gobe. Allah ya kan jarabci bawanshi ta kowace irin hanya. Zata iya yiwuwa ta kankanin abu, ko babba, ko iyaye, ko 'ya'ya, ko cuta, ko kuma sauran abubuwa. Na yarda hakan yana daga cikin jarabawata, don haka ban damu ba sosai. Fatana Allah ya bani ikon cinyeta. Nasan watarana idan da rai, hakan zai zamo tamkar ba ayi ba. Don haka nake godewa Allah a kullum, kuma a koyaushe.
Jiya Yaya Bilal ya tafi Umarah shi da Anty Ameerah. Ba'a tafi da Raheemah ba saboda last year da ita aka je a cewar Janan. Bata ji dadin hakan ba, saboda haka sai da suka dan yi rikici da Yayan akan wai yana gwada mata rashin adalci kafin ya tafi. Bayan tafiyar tashi kuma sai abin ya koma kan Janan, tsangawamar yau daban, ta jibi daban. Wai kicin ma suke rufe mata yanzu, bayan da Yayan zai tafi sai daya cika kicin din ya batse shi da duk kayan amfani. Nace ta kira shi a waya ta gaya mishi mana, tace wai bata son ta dinga tada musu zaune tsaye, nace "ai sai kiyi tayi!".
Kawai sai ganinta nayi da dubu dai-daya har guda goma, wai inji Yaya inyi sayayyar azumi. Abin ya bani mamaki matuka, na karba nayi godiya. Da yake ma hannuna da kudi, cikin wannan satin wata karamar kwangila da Yaya yayi ta fito, cikin kudin da aka samu ne nima ya dan tsakuro min. Na hada su waje guda na ajiye ban tasar musu haikan ba, nasan a hankali a hankali idan na tattala zasu dade min.
Tunda Yaya Bilal yayi tafiyar nan, kusan kullum anan wajena Janan take shan ruwa. Wasu lokutan ma sai mun gama sallar tarawihi sannan take tafiya gida, idan kuma Allah ya taimaketa Is'haq ya shigo ta nan wajajen, sai ya dauketa su tafi.
Kasancewar ba wani dogon hutu zamu yi ba, yasa na yanke shawarar bin Janan Kaduna kawai inyi sallata acan. Don haka na lallaba Maryam ta karban min kayan sallar da aka bani, atamfa da leshi da takalmi kala daya, ta bayar ta motar haya aka kawo min na kai wajen dinki. Tun dai ana saura kwana biyar muyi tafiyar na kira Baba na fada mishi, yace babu laifi.
Shi dama Yaya da yake ya riga yasan Janan, itama wasu lokutan idan muka samu hutu gajere muna zuwa Gashua da ita. Sannan idan Allah yasa yayo ta wajen Zaria ya biyo mu gaisa, suna haduwa da ita. Ya santa sosai har su Ummahn, saboda haka koda na fada mishi acan zanyi sallah cewa yayi hakan ma yafi, tunda yafi kusa. Shima dubu biyar ya turo min wai in samu karamar atamfa in saya in dinka, na mishi godiya sosai kuwa.
Ranar da muka dauki azumi na ashirin da takwas, ranar muka wuce Kaduna. Sallah ta rage kwana biyu ko daya kenan. Itama Ummah a daren ranar zata dawo, yayin da Yaya Bilal kuma sai washegari.
#F.W.A
*☆⋆19⋆☆*
Ranar sallah muka sha kwalliyarmu, da safe muka bi yaran gidan muka je idi. Jiya da dare bamu kwanta da wuri ba saboda hidimar abincin sallah. Mun yi miyar taushe, aka soya nama, kaji, har da su snacks. Da safe da zamu tafi idi muka bar yan aiki suna soya masa ta farar shinkafa. Don haka muna dawowa aka fara rabon abinci, gida-gida.
Ummah mace ce mai mutane sosai, saboda haka yinin ranar mutane ne yara da manya, yan gida ko yan unguwa, suna ta shigi da fici kamar wata hidimar biki ko suna.
Gidansu Janan babban gidane, Alhaji Salisu Makarfi mahaifinsu Janan babban mutum ne kuma dan dangi, tsohon soja ne amma yanzu yayi ritaya. Kafin ya auri Ummah yana da mata wadda ta mutu ta bar manyan 'ya'ya maza har su hudu, bayan sunyi aure da Ummah kuma ta haifi Janan, daga baya ne ya sake aurar Usaina babar su Harira da suke kira Yaya. Mutum ne shi na mutane, ya kuma rike zumunci sosai, shi yasa iyalanshi suka taso cike da zumunci da kauna ta yan uwantaka, idan kaje gidan baka banbance dan gida dana waje, baka banbance dan daki da dan daki. Yawancin diyan yan uwanshi a gidan suka girma har suka riski lokacin aure wasu kuma tare da nashi diyan suka yi makaranta wanda shi yake biya musu kudin makarantar. Shi yasa kullum baka raba gidan da mutane.
Samarin gidan da suka taso a gidan, ko bayan da suka yi aure, wasu lokutan idan kaje gidan zaka gansu ko a kofar gida, ko kuma a cikin gidan karkashin daya daga cikin bishiyoyin gidan suna hutawa ko suna hira. Da yake babban gidane, akwai part daban da aka ware wanda mazan gidan suke amfani dashi.
Nayi lamo akan katifa cikin tunani iri-iri, kala-kala, ban taba jin karatun nan ya fita a raina ba sai yau. A raina na raya wai da wanne ake so inji ne? Abu ne da bai taka kara ya karya ba, wanda na tabbata yafi karfin Baba, amma kullum cikin ja wa kanshi babu yake, kullum babu, kuma babun a kaina kadai take.
Yawancin matsaloli irin haka idan suka taso dama sai dai in tuntubi Yaya da maganar, idan bata fi karfinshi ba ya maganceta, in kuma tafi sai ya kai ga dangana da su Malam. To ita kuma rayuwa ba zai yiwu taci gaba a haka ba, ba zai yiwu ace kai kullum cikin bani-bani da a maka-a maka kake ba, kowa ma dama zai ji ya gaji.
Sai dai idan nayi duba ta wani bangaren, sai inga yaushe na cika bani-bani kamar yadda Baba yace? Tsakanina dashi kawai kudin handout ne, sai abinda yaga dama ya dan lafo min ciki kawai. Dama can yawancin hidima da dawainiya Yaya ne yake yi, idan aka samu ya biya school fees da kyar, ya hado min provision, to sauran fa sai dai yadda hali yayi, sai na sha matukar wahala ya kuma yazga ni yadda yaga dama sannan zai turo min na bukatun yau da gobe. To maganar gaskiya na gaji yanzu, yanzu haka kwanciyar da nayi ina tunani, tunanin hada kan kayana nake in koma gida kawai, azabar ta isa.
Sai kuma naga idan ma na koma, ni zan kwari kaina, babu wanda zai ji a jikinsa dai sai ni. Don haka naci gaba da tunani ina laluben mafita. Nasan mafita daya itace in fadawa Yaya, amma gani nake kamar abin yayi yawa. Shi shikenan kullum cikin ji da matsalata, kullum babu hutu?.
Ban tashi daga kwanciyar ba sai da aka kira Sallar azuhur, ashe wani wahalallen barci ne ya daukeni. Wani irin barci mai dauke da wasu irin sarkakkun mafarkai. Na tashi ina mika da hamma, maimakon inji gajiyata ta tafi, sai naji kamar an dauko gajiyar duniya ne an dora min aka. Haka nan na lallaba na watsa ruwa a jikin nawa ya dan min karfi, sannan nazo nayi sallah.
Ina cikin karatu Janan ta kirani. Roko na ta dinga yi akan inje in mata weekend, kai tsaye nace mata a'ah, ta dawo tana magiyar to inje in tayata shan ruwa, nan ma nace a'ah. Ni dai tunda na samu nayi sa'a, Allah ya taimakeni na baro gidan, ai an wuce wurin. Ta gaji tayi fushi ta ajiye wayar. Da yake ba a cikin yanayi mai dadi nake ba, kyaleta nayi kawai.
Yinin ranar haka na yi shi sukuku, can da yamma wai sai ga Maryam, mun gaisa da ita gari-gari, wai in na shiga kasuwa in sayo mata sarka da yan kunne idan ma naga da halin takalmi in karo, naji kamar in hau rusa mata ihu na dai cije nace mata to kawai, na ajiye wayar.
*
Dole kanwar naki haka na dage na kira Yaya zuwa ranar talata, domin duk ta inda na buga abubuwan babu sauki, babu wata mafita. Na zayyane mishi matsalar da muke ciki da Baba, Yayan yayi shiru yana tunani, kafin daga baya yace zai kira shi sai yayi mishi bayani. Na mishi godiya nace to, na kashe wayar.
Allah ya taimakeni cikin satin aka turo mana kudin scholarship da aka saba bamu. Kuka ne kadai banyi ba ranar saboda murna, dama nayi karaf, bani da ko sisi. Haka kayayyakin da suka rage min duk sun tasamma karewa. Yawanci idan aka turo min ina fadawa Baba, amma wannan karon da yake a wuya nake da kowa, babu wanda yaji labari. Kasuwa kawai na fada.
*
Abu wasa-wasa, tun ana yau azumi, har gashi mun zo mun ci tsakiyar shi. Yaya ya samu ya shawo kan Baba da kyar ya turo min kudin, naje na biya. Allah ya taimakeni basu kai ga rufewa ba. Abubuwa zuwa yanzu sun yi min sauki nesa ba kusa ba, ba kamar satin daya gabata ba. Ban bar wannan abin ya dameni ba ko kuma ya hana ni aikata abubuwana na yau da gobe. Allah ya kan jarabci bawanshi ta kowace irin hanya. Zata iya yiwuwa ta kankanin abu, ko babba, ko iyaye, ko 'ya'ya, ko cuta, ko kuma sauran abubuwa. Na yarda hakan yana daga cikin jarabawata, don haka ban damu ba sosai. Fatana Allah ya bani ikon cinyeta. Nasan watarana idan da rai, hakan zai zamo tamkar ba ayi ba. Don haka nake godewa Allah a kullum, kuma a koyaushe.
Jiya Yaya Bilal ya tafi Umarah shi da Anty Ameerah. Ba'a tafi da Raheemah ba saboda last year da ita aka je a cewar Janan. Bata ji dadin hakan ba, saboda haka sai da suka dan yi rikici da Yayan akan wai yana gwada mata rashin adalci kafin ya tafi. Bayan tafiyar tashi kuma sai abin ya koma kan Janan, tsangawamar yau daban, ta jibi daban. Wai kicin ma suke rufe mata yanzu, bayan da Yayan zai tafi sai daya cika kicin din ya batse shi da duk kayan amfani. Nace ta kira shi a waya ta gaya mishi mana, tace wai bata son ta dinga tada musu zaune tsaye, nace "ai sai kiyi tayi!".
Kawai sai ganinta nayi da dubu dai-daya har guda goma, wai inji Yaya inyi sayayyar azumi. Abin ya bani mamaki matuka, na karba nayi godiya. Da yake ma hannuna da kudi, cikin wannan satin wata karamar kwangila da Yaya yayi ta fito, cikin kudin da aka samu ne nima ya dan tsakuro min. Na hada su waje guda na ajiye ban tasar musu haikan ba, nasan a hankali a hankali idan na tattala zasu dade min.
Tunda Yaya Bilal yayi tafiyar nan, kusan kullum anan wajena Janan take shan ruwa. Wasu lokutan ma sai mun gama sallar tarawihi sannan take tafiya gida, idan kuma Allah ya taimaketa Is'haq ya shigo ta nan wajajen, sai ya dauketa su tafi.
Kasancewar ba wani dogon hutu zamu yi ba, yasa na yanke shawarar bin Janan Kaduna kawai inyi sallata acan. Don haka na lallaba Maryam ta karban min kayan sallar da aka bani, atamfa da leshi da takalmi kala daya, ta bayar ta motar haya aka kawo min na kai wajen dinki. Tun dai ana saura kwana biyar muyi tafiyar na kira Baba na fada mishi, yace babu laifi.
Shi dama Yaya da yake ya riga yasan Janan, itama wasu lokutan idan muka samu hutu gajere muna zuwa Gashua da ita. Sannan idan Allah yasa yayo ta wajen Zaria ya biyo mu gaisa, suna haduwa da ita. Ya santa sosai har su Ummahn, saboda haka koda na fada mishi acan zanyi sallah cewa yayi hakan ma yafi, tunda yafi kusa. Shima dubu biyar ya turo min wai in samu karamar atamfa in saya in dinka, na mishi godiya sosai kuwa.
Ranar da muka dauki azumi na ashirin da takwas, ranar muka wuce Kaduna. Sallah ta rage kwana biyu ko daya kenan. Itama Ummah a daren ranar zata dawo, yayin da Yaya Bilal kuma sai washegari.
#F.W.A
*☆⋆19⋆☆*
Ranar sallah muka sha kwalliyarmu, da safe muka bi yaran gidan muka je idi. Jiya da dare bamu kwanta da wuri ba saboda hidimar abincin sallah. Mun yi miyar taushe, aka soya nama, kaji, har da su snacks. Da safe da zamu tafi idi muka bar yan aiki suna soya masa ta farar shinkafa. Don haka muna dawowa aka fara rabon abinci, gida-gida.
Ummah mace ce mai mutane sosai, saboda haka yinin ranar mutane ne yara da manya, yan gida ko yan unguwa, suna ta shigi da fici kamar wata hidimar biki ko suna.
Gidansu Janan babban gidane, Alhaji Salisu Makarfi mahaifinsu Janan babban mutum ne kuma dan dangi, tsohon soja ne amma yanzu yayi ritaya. Kafin ya auri Ummah yana da mata wadda ta mutu ta bar manyan 'ya'ya maza har su hudu, bayan sunyi aure da Ummah kuma ta haifi Janan, daga baya ne ya sake aurar Usaina babar su Harira da suke kira Yaya. Mutum ne shi na mutane, ya kuma rike zumunci sosai, shi yasa iyalanshi suka taso cike da zumunci da kauna ta yan uwantaka, idan kaje gidan baka banbance dan gida dana waje, baka banbance dan daki da dan daki. Yawancin diyan yan uwanshi a gidan suka girma har suka riski lokacin aure wasu kuma tare da nashi diyan suka yi makaranta wanda shi yake biya musu kudin makarantar. Shi yasa kullum baka raba gidan da mutane.
Samarin gidan da suka taso a gidan, ko bayan da suka yi aure, wasu lokutan idan kaje gidan zaka gansu ko a kofar gida, ko kuma a cikin gidan karkashin daya daga cikin bishiyoyin gidan suna hutawa ko suna hira. Da yake babban gidane, akwai part daban da aka ware wanda mazan gidan suke amfani dashi.