Sashe 9
A Zato Na Complete Hausa Novel · about 8 min read
Matan gidan suna zaune a tsakar gida, Anty Alawiyya na dura kunun aya da take yi na sayarwa a cikin gororin ruwa, Anty Ramata kuma tana kofar kicin a zaune, ina zaton ita take da girki yau.
Duk suka saurara da abinda suke yi jin hayaniyar yara har muka shiga cikin gidan. Anty Alawiyya ce ta mike tana dan murmushi, "mutanen Zaria ne yau a garin? Ai bamu ji labarin zaki zo ba koda wasa!".
Nayi murmushin yake, dama a ina zasu ji? Na san koda wasa Baba ba zai fada musu ba. Ni kuwa dama ba waya muke yi dasu sosai ba, tunda na fara makaranta, babu wadda ta taba daga waya ta kira ni da sunan mu gaisa, sai nice idan naga an kwashi kwanaki nake kiransu haka nan dai, musamman ma don mu gaisa da yara. Kullum idan na dawo daga makaranta zancen daya, ne babu wani canji.
Na sauke Mufeedah kasa tare da gaidasu daya bayan daya, suka amsa fuska babu yabo babu fallasa, na tabe baki tare da ciccibar akwatuna na tunkari dakin daya kasance nawa tunda muka dawo Katsina.
Na ja nayi turus, sakamakon ganin kofar dakin a bude, abin ya bani mamaki. Na tabbata da zan tafi makaranta sai da na saka kwado na rufe kofar dakin, kuma ban bar dan makullin a gida ba. Babu wanda yayi tunanin yi min karin bayanin abinda yake faruwa, don haka na tura kofar dakin.
Abu na farko daya fara min sallama shine tarin kayana da aka hade waje guda acan karshen lungu, akwatuna daya kan daya, kwalaye bisa kwalaye, yayin da ilahirin tsakiyar dakin yake shake da tarkacen kayan Maryam. Na juya na kalli Saudah yar autar Anty Ramata dake zaune a kofar dakin mamanta dake kusa da dakin da nake, nace mata "waye yake kwana a dakina?".
Tace "Anty Maryam ce, Mama tace ta koma dakinki tunda kullum a kulle yake kuma tayi girma da zama a dakinta".
Nayi kwafa ina kallon Uwarta ta, nace "shine saboda tsabar bani da muhimmanci babu wanda yayi tunanin sanar dani?". Duk suka yi tsuru su biyun. Na sake yin kwafa tare da shiga cikin dakin. Ko karewa dakin kallo ban yi ba naje na dauro alwala na dawo dakin nayi sallah. Sai dana gama sannan na kira Umar na sanar dashi sauka ta, yayi min sannu da zuwa. Bayan nan na kira Janan itama muka gaisa, tana dariya tace "bana miki wayo, ni tun safe ina gaban Ummana!".
Nayi yar dariya, "ya miki kyau ai, Allah ne ma yasa motar tayi gudu sosai, kila da sai magriba zan iso ni kam".
Mun dan yi hira kadan da ita, har ta bani Umma muka gaisa, sannan muka yi sallama da ita.
Tashi nayi na fara gyara kayana da aka wulakanta a dakin, ina maida su ainihin wajen da suke da. Kafin a kira sallar magriba na kammala gyarasu tas. Nayi sallah, na zauna akan abin sallar nayi karatu kamar yadda na saba har aka kira isha'i nayi, sannan naci gaba da gyara dakin. Na share shi nayi mopping, na dauko room freshener dana saba yin guzurinta na fesa a dakin. Nan da nan dakin ya fito tas dashi, ba kamar yadda na same shi dazu ba kamar bana mahaukata.
Tun ina karatu naji alamun karan motar Baba alamun ya dawo gida. Kasancewar yau babu aiki nasan cewa daga shago yake. Zuwa yanzu nasan cewa ya ci abinci kuma ya huta, na dauki hijabina na fita zuwa dakinshi. Babu kowa a dakin na shi sai shi kadai. Na durkusa acan gefenshi na gaida shi, ya amsa. Da alamun yana cikin yanayi mai dadi, tunda har na zauna muka danyi hira dashi. Abinda sai lokaci zuwa lokaci yake faruwa.
Ban san me yasa ba, ni da Baba sam bamu cika shiri ba. Amma nafi kyautata zaton rawar kaina ce ta janyo hakan, tunda ya sha fada ba sau daya ba, ba sau biyu ba.
Sai da Ramata ta shigo dakin sannan na mishi sai da safe, na koma dakina, ko ince dakinmu.
Ina komawa shirin barci na fara yi. Bayan nayi Sallar shafa'i da wutiri, na samu gefen katifa na zauna tare da dauko wayata dana ajiye a kasan filona. Ina cikin chatting Maryam ta shigo cikin dakin.
Duk yan dakin Ramata, ita, Aliyu da Hareerah, da ita kadai muka fi dasawa. Sauran suna kan hudubar uwarsu na cewa 'yan uba, ba 'yan uwa bane! saboda haka bamu cika shiri dasu ba. Amma ita babu ruwanta ko kadan.
Tayi murmushi tana kallona, "yanzu Hareerah take fada min cewa kin zo, ina ta mamaki".
Nayi yar dariya ina kallonta tana zame after dress din dake jikinta, riga top mai karamin hannu da wnadon bakin jeans suka bayyana a jikinta, dariyata ta koma daga gida mai nuna alamun tambaya, nace "daga ina kike, kuma wannan shigar fa?".
Ta kalli jikinta kafin ta kalleni, "kawata take bikin birthday, shine na leka wallahi".
Na girgiza kai, "birthday party kuma sai da irin wannan shiga Maryam? Me yasa?".
Tayi dariya, "Yaya Na'ilah ke da kike makarantar jami'a kin fa fini sanin irin wadannan abubuwan. Yanzu 'yanmata ai sai da swagger! Idan mutum ba so yake a dinga mishi kallon taro-uku-sisi ba!".
Cikin mamaki nake kallonta, "ban san daga ina kika dauko wannan kalar abu ba Maryam, amma hakan bai kama ce ki ba gaskiya. Ta ya kike zaton Mamanki zata dauki wannan maganar idan taji irin shigar da kike boyewa a cikin hijabi? Don daga ji nasan cewa wannan ba shine karonki na farko ba".
Tayi dariya tana watso min wani kallo irin 'are you kidding me' dinnan Tace "me Mama zata ce kuwa? In fada miki gaskiya ita ta bani shawarar in dinga sanya after dress idan zan fita, in naje can inda zan je sai in cire saboda kada wani idon sani ya ganni a haka... Amma meye na wani boyo? Zamaninmu ne fa!".
Tunda ta fara maganar bakina a hangame yake a bude, Subhanallah! Yaushe yaran gidanmu suka fara bin wannan hanyar ne? Nasan cewa tsakanin iyalan dama babu hadin kai da kaunar juna, saboda tun farko basu ga hakan daga wajen iyayensu ba, amma wannan wani babban al'amari ne, wanda nake ganin idan har aka bari ya girmama, akwai matsala. To amma, abinda uwa take supporting da dukkan karfinta, waye yake da karfin hana ta?
Ta tunkari kofa zata fita tana furta, "bari in zo inyi sallah!".
Ina nan zaune ina ta saka da warwara ta dawo, ta shimfida abin sallah ta kalli gabas. Yadda take yin Sallar ma kadai abin zai baka mamaki. Kamar wadda bata taba taka ajin islamiya ba Raka'o'in data jero masu yawa yasa na fahimci cewa ba sallar isha'i kadai tayi ba.
Sai dana bari ta gama duk abinda zata yi, har ta kwanta sannan na dubi inda take, nace "ni kuwa a wani matakin karatu kike yanzu a islamiya?", na dai san cewa yanzu tana ss2.
Tayi dariya, "na kusa wata ma ni rabona da makarantar nan yanzu, yan ajinmu aka wa karin aji zuwa na yan sauka, ni kuma aka barni a ajin baya shi yasa na daina zuwa ma kwata-kwata".
Na tashi zaune sosai ina kallonta, sanin halin Maryam na saurin fahimta da ganewa yasa nafi jin dadin zama yi mata magana ko gyara akan wani abu, ba kamar Aliyu ba. Sau tari dan karamin gyara sai ya kaimu ga ya kalli tsakiyar idanuna ya zage tas kamar wanda yake jira dama.
Nace "kin san fa yanzu kece babba a gidannan Maryam. Kuma duk abinda kika yi, kannenki da suke tasowa shi zasu dinga yi. Yanzu idan basu ga yayarsu na zuwa makaranta ba, ta ya kike tunanin zasu samu kwarin gwiwar zuwa makaranta? Kinga ke dai baki da bakin cewa su zo su tafi, tunda kema ba zuwa kike yi ba. Sannan dubi dai irin shigar da kika yi yanzu, ya Baba zai ji, kuma me kike zaton zai ce duk ranar da yaci karo da irin wannan abu da kike yi? Maryam, kinga ke diya macece, sannan yarinya, kada ki bari rudin duniya da abokai ya rude ki, ki saka kanki cikin rayuwar da tafi karfinki. Shiga irin wannan da kike yi ta nuna jiki, ki shiga cikin kawaye ana ta cakuda da maza, akan wane dalili? Ina kika baro tarbiyar gidanmu da kuma al'adarmu ta hausa/fulani?".
Tayi kasa da kanta a kunyace, "wallahi Yaya, Mama ce take cewa in dai ba za'a hada mu da yan ajinmu ba, sai dai in daina zuwa makarantar. Kuma ita take sawa inyi shigar. Ranar ma ana bikin Na'imah dana sanya hijabi sai ta hau fada, tana cewa wai ni ban waye ba!".
Na girgiza kai cike da jimami, iyayen yanzu yawanci su suke bada gudummawa wajen lalacewar tarbiyar yaranmu. Uwa ce wai zata dorawa diya akidar yafa gyale da saka suturun banza, ita zata sanya mata akidar bin kawaye da samarin banza, daga karshe kuma idan lamari yazo ya bace bakinta ne zai fi na kowa wajen ihun cewa an lalata mata tarbiyar yara, bayan kuma itace tayi contributing wajen lalacewar tata.
Tsam na tashi na koma kusa da ita na zauna tare da dafa kafadarta, nace "idan tayi hakan ba laifi bane, tana so ne ki zama abar kallo, kamar tauraruwa. Sai dai, zaki iya zama fiye da hakan ma, ba kuma sai kin sabawa Ubangiji ba, kin gane?". Ta daga kai.
Nace "good. Saboda haka gobe zamu je islamiyar taku, zan samu malaman naku muyi magana dasu. Sannan don Allah, shiga ta banza mai nuna jiki, ki daina yin ta. Ko ba don ke ba, ki duba kimar da Baba yake da ita a idanun mutane, balle ke kanki idan baki kame kanki a matsayinki na ya mace ba, Maryam zaki ga kin rasa girmamawar mutane, kin fahimce ni?". Nan ma ta gyada kai.
Nayi murmushi cike da jindadi. Yanayin yadda jikinta yayi sanyi ya nuna min cewa taji, kuma ta dauki abinda nace. Na rungumota gefen kafadata ina kara yi mata bayanai da nasiha akan rayuwa. Daga karshe dai na janyo laptop dita na kunna mana kallo a ciki, babu TV a dakinmu sai na Baba dana matanshi, yawanci can muke zuwa muyi kallo. Ranar akan katifarta na kwana.
Duk suka saurara da abinda suke yi jin hayaniyar yara har muka shiga cikin gidan. Anty Alawiyya ce ta mike tana dan murmushi, "mutanen Zaria ne yau a garin? Ai bamu ji labarin zaki zo ba koda wasa!".
Nayi murmushin yake, dama a ina zasu ji? Na san koda wasa Baba ba zai fada musu ba. Ni kuwa dama ba waya muke yi dasu sosai ba, tunda na fara makaranta, babu wadda ta taba daga waya ta kira ni da sunan mu gaisa, sai nice idan naga an kwashi kwanaki nake kiransu haka nan dai, musamman ma don mu gaisa da yara. Kullum idan na dawo daga makaranta zancen daya, ne babu wani canji.
Na sauke Mufeedah kasa tare da gaidasu daya bayan daya, suka amsa fuska babu yabo babu fallasa, na tabe baki tare da ciccibar akwatuna na tunkari dakin daya kasance nawa tunda muka dawo Katsina.
Na ja nayi turus, sakamakon ganin kofar dakin a bude, abin ya bani mamaki. Na tabbata da zan tafi makaranta sai da na saka kwado na rufe kofar dakin, kuma ban bar dan makullin a gida ba. Babu wanda yayi tunanin yi min karin bayanin abinda yake faruwa, don haka na tura kofar dakin.
Abu na farko daya fara min sallama shine tarin kayana da aka hade waje guda acan karshen lungu, akwatuna daya kan daya, kwalaye bisa kwalaye, yayin da ilahirin tsakiyar dakin yake shake da tarkacen kayan Maryam. Na juya na kalli Saudah yar autar Anty Ramata dake zaune a kofar dakin mamanta dake kusa da dakin da nake, nace mata "waye yake kwana a dakina?".
Tace "Anty Maryam ce, Mama tace ta koma dakinki tunda kullum a kulle yake kuma tayi girma da zama a dakinta".
Nayi kwafa ina kallon Uwarta ta, nace "shine saboda tsabar bani da muhimmanci babu wanda yayi tunanin sanar dani?". Duk suka yi tsuru su biyun. Na sake yin kwafa tare da shiga cikin dakin. Ko karewa dakin kallo ban yi ba naje na dauro alwala na dawo dakin nayi sallah. Sai dana gama sannan na kira Umar na sanar dashi sauka ta, yayi min sannu da zuwa. Bayan nan na kira Janan itama muka gaisa, tana dariya tace "bana miki wayo, ni tun safe ina gaban Ummana!".
Nayi yar dariya, "ya miki kyau ai, Allah ne ma yasa motar tayi gudu sosai, kila da sai magriba zan iso ni kam".
Mun dan yi hira kadan da ita, har ta bani Umma muka gaisa, sannan muka yi sallama da ita.
Tashi nayi na fara gyara kayana da aka wulakanta a dakin, ina maida su ainihin wajen da suke da. Kafin a kira sallar magriba na kammala gyarasu tas. Nayi sallah, na zauna akan abin sallar nayi karatu kamar yadda na saba har aka kira isha'i nayi, sannan naci gaba da gyara dakin. Na share shi nayi mopping, na dauko room freshener dana saba yin guzurinta na fesa a dakin. Nan da nan dakin ya fito tas dashi, ba kamar yadda na same shi dazu ba kamar bana mahaukata.
Tun ina karatu naji alamun karan motar Baba alamun ya dawo gida. Kasancewar yau babu aiki nasan cewa daga shago yake. Zuwa yanzu nasan cewa ya ci abinci kuma ya huta, na dauki hijabina na fita zuwa dakinshi. Babu kowa a dakin na shi sai shi kadai. Na durkusa acan gefenshi na gaida shi, ya amsa. Da alamun yana cikin yanayi mai dadi, tunda har na zauna muka danyi hira dashi. Abinda sai lokaci zuwa lokaci yake faruwa.
Ban san me yasa ba, ni da Baba sam bamu cika shiri ba. Amma nafi kyautata zaton rawar kaina ce ta janyo hakan, tunda ya sha fada ba sau daya ba, ba sau biyu ba.
Sai da Ramata ta shigo dakin sannan na mishi sai da safe, na koma dakina, ko ince dakinmu.
Ina komawa shirin barci na fara yi. Bayan nayi Sallar shafa'i da wutiri, na samu gefen katifa na zauna tare da dauko wayata dana ajiye a kasan filona. Ina cikin chatting Maryam ta shigo cikin dakin.
Duk yan dakin Ramata, ita, Aliyu da Hareerah, da ita kadai muka fi dasawa. Sauran suna kan hudubar uwarsu na cewa 'yan uba, ba 'yan uwa bane! saboda haka bamu cika shiri dasu ba. Amma ita babu ruwanta ko kadan.
Tayi murmushi tana kallona, "yanzu Hareerah take fada min cewa kin zo, ina ta mamaki".
Nayi yar dariya ina kallonta tana zame after dress din dake jikinta, riga top mai karamin hannu da wnadon bakin jeans suka bayyana a jikinta, dariyata ta koma daga gida mai nuna alamun tambaya, nace "daga ina kike, kuma wannan shigar fa?".
Ta kalli jikinta kafin ta kalleni, "kawata take bikin birthday, shine na leka wallahi".
Na girgiza kai, "birthday party kuma sai da irin wannan shiga Maryam? Me yasa?".
Tayi dariya, "Yaya Na'ilah ke da kike makarantar jami'a kin fa fini sanin irin wadannan abubuwan. Yanzu 'yanmata ai sai da swagger! Idan mutum ba so yake a dinga mishi kallon taro-uku-sisi ba!".
Cikin mamaki nake kallonta, "ban san daga ina kika dauko wannan kalar abu ba Maryam, amma hakan bai kama ce ki ba gaskiya. Ta ya kike zaton Mamanki zata dauki wannan maganar idan taji irin shigar da kike boyewa a cikin hijabi? Don daga ji nasan cewa wannan ba shine karonki na farko ba".
Tayi dariya tana watso min wani kallo irin 'are you kidding me' dinnan Tace "me Mama zata ce kuwa? In fada miki gaskiya ita ta bani shawarar in dinga sanya after dress idan zan fita, in naje can inda zan je sai in cire saboda kada wani idon sani ya ganni a haka... Amma meye na wani boyo? Zamaninmu ne fa!".
Tunda ta fara maganar bakina a hangame yake a bude, Subhanallah! Yaushe yaran gidanmu suka fara bin wannan hanyar ne? Nasan cewa tsakanin iyalan dama babu hadin kai da kaunar juna, saboda tun farko basu ga hakan daga wajen iyayensu ba, amma wannan wani babban al'amari ne, wanda nake ganin idan har aka bari ya girmama, akwai matsala. To amma, abinda uwa take supporting da dukkan karfinta, waye yake da karfin hana ta?
Ta tunkari kofa zata fita tana furta, "bari in zo inyi sallah!".
Ina nan zaune ina ta saka da warwara ta dawo, ta shimfida abin sallah ta kalli gabas. Yadda take yin Sallar ma kadai abin zai baka mamaki. Kamar wadda bata taba taka ajin islamiya ba Raka'o'in data jero masu yawa yasa na fahimci cewa ba sallar isha'i kadai tayi ba.
Sai dana bari ta gama duk abinda zata yi, har ta kwanta sannan na dubi inda take, nace "ni kuwa a wani matakin karatu kike yanzu a islamiya?", na dai san cewa yanzu tana ss2.
Tayi dariya, "na kusa wata ma ni rabona da makarantar nan yanzu, yan ajinmu aka wa karin aji zuwa na yan sauka, ni kuma aka barni a ajin baya shi yasa na daina zuwa ma kwata-kwata".
Na tashi zaune sosai ina kallonta, sanin halin Maryam na saurin fahimta da ganewa yasa nafi jin dadin zama yi mata magana ko gyara akan wani abu, ba kamar Aliyu ba. Sau tari dan karamin gyara sai ya kaimu ga ya kalli tsakiyar idanuna ya zage tas kamar wanda yake jira dama.
Nace "kin san fa yanzu kece babba a gidannan Maryam. Kuma duk abinda kika yi, kannenki da suke tasowa shi zasu dinga yi. Yanzu idan basu ga yayarsu na zuwa makaranta ba, ta ya kike tunanin zasu samu kwarin gwiwar zuwa makaranta? Kinga ke dai baki da bakin cewa su zo su tafi, tunda kema ba zuwa kike yi ba. Sannan dubi dai irin shigar da kika yi yanzu, ya Baba zai ji, kuma me kike zaton zai ce duk ranar da yaci karo da irin wannan abu da kike yi? Maryam, kinga ke diya macece, sannan yarinya, kada ki bari rudin duniya da abokai ya rude ki, ki saka kanki cikin rayuwar da tafi karfinki. Shiga irin wannan da kike yi ta nuna jiki, ki shiga cikin kawaye ana ta cakuda da maza, akan wane dalili? Ina kika baro tarbiyar gidanmu da kuma al'adarmu ta hausa/fulani?".
Tayi kasa da kanta a kunyace, "wallahi Yaya, Mama ce take cewa in dai ba za'a hada mu da yan ajinmu ba, sai dai in daina zuwa makarantar. Kuma ita take sawa inyi shigar. Ranar ma ana bikin Na'imah dana sanya hijabi sai ta hau fada, tana cewa wai ni ban waye ba!".
Na girgiza kai cike da jimami, iyayen yanzu yawanci su suke bada gudummawa wajen lalacewar tarbiyar yaranmu. Uwa ce wai zata dorawa diya akidar yafa gyale da saka suturun banza, ita zata sanya mata akidar bin kawaye da samarin banza, daga karshe kuma idan lamari yazo ya bace bakinta ne zai fi na kowa wajen ihun cewa an lalata mata tarbiyar yara, bayan kuma itace tayi contributing wajen lalacewar tata.
Tsam na tashi na koma kusa da ita na zauna tare da dafa kafadarta, nace "idan tayi hakan ba laifi bane, tana so ne ki zama abar kallo, kamar tauraruwa. Sai dai, zaki iya zama fiye da hakan ma, ba kuma sai kin sabawa Ubangiji ba, kin gane?". Ta daga kai.
Nace "good. Saboda haka gobe zamu je islamiyar taku, zan samu malaman naku muyi magana dasu. Sannan don Allah, shiga ta banza mai nuna jiki, ki daina yin ta. Ko ba don ke ba, ki duba kimar da Baba yake da ita a idanun mutane, balle ke kanki idan baki kame kanki a matsayinki na ya mace ba, Maryam zaki ga kin rasa girmamawar mutane, kin fahimce ni?". Nan ma ta gyada kai.
Nayi murmushi cike da jindadi. Yanayin yadda jikinta yayi sanyi ya nuna min cewa taji, kuma ta dauki abinda nace. Na rungumota gefen kafadata ina kara yi mata bayanai da nasiha akan rayuwa. Daga karshe dai na janyo laptop dita na kunna mana kallo a ciki, babu TV a dakinmu sai na Baba dana matanshi, yawanci can muke zuwa muyi kallo. Ranar akan katifarta na kwana.