Sashe 3
A Zato Na Complete Hausa Novel · about 8 min read
Na dauki agogon hannu ruwan kasa mai haske na daura, a jikinta naga cewa bakwai da rabi ta kusa yi. Cikin sauri na dauki gyale mai yalwar fadi na yafa a jikina. Na dauki purse, wayar hannu da littafin da nake shigar da duk wasu bayanai na ilimin dana dauka a ranar da naje asibiti, cikin sauri na zura bakin toms a kafata, na yiwa abokiyar zamana sallama na fita har ina hadawa da dan gudu.
Ina zuwa, bus din da take daukanmu zuwa Kongo tana zuwa, don haka na bi jerin mutanen dake layi suna shiga ciki, bayan na biya kudin mota.
Karfe takwas da yan mintuna na sauka a inda na saba sauka. Daga nan acaba na hau, zuwa cikin unguwar Gyallesu, wani karamin public health centre nake zuwa aikin TP na. Karfe takwas muke farawa mu gama karfe daya zuwa biyu. Kowa dai yasan yadda dalibai suke da son yin latti, musamman a irin wannan lokacin da kasan cewa babu wanda zai kulle maka aji, ko ya hana ka attendance.
Duk da lattin da nayi, sai da na riga Janan isa. Ita wannan dama ba'a maganarta idan ana zancen latti, sam bata dana biyu.
Karfe sha daya da rabi muka tashi. Muka fita daga wajen ni da ita a gajiye, kuma cikin sanyin jiki. Babu ranar banza da ba zaka je asibitin nan baka ga abinda zai tayar maka da hankali ba.
Ranar an kai wata mata mai ciki asibitin. Kwanaki uku kenan da aka yi mata scanning, aka ga cewar dan cikinta ya rasu. Maimakon a yi inducing dinta, sai mijin ya ciccibeta suka koma gida. Wani abin karin haushi da ban takaici shine, mijin nata likita ne, duk da ba zan ce likitan ainihi ba tunda shago ne yake dashi babba da ake sayar da magunguna.
Tun shakaranjiya take nakuda, bai kaita asibiti ba sai ya kira unguwar-zoma. Ana ta kai da kawo dai, har jiya bata samu ta haihu ba, shine yau da safe suka tarkata ta zuwa asibitin. Ana maganar a dauketa a kaita Shika, domin a mata tiyata a cire cikin, rai yayi halinsa.
Abin gwanin ban tausayi da takaici. Ga ta da yara kanana wadanda basu gama mallakar hankulan kansu ba.
Har muka je inda muke hawa acaba, abinda muke tattaunawa kenan ni da Janan.
Ta kalleni tana canza muryarta zuwa alamun roko, "don Allah sis, kizo muje gida mana. Sai ki koma da yamma, kinji?".
Na harareta, "tab! Allah Ya kyauta wallahi. Ni kin ma ga tafiyata!".
Nayi saurin sa hannu ina kiran daya daga cikin yan acaban da suka yi jerin gwano, suna jiran fasinjoji.
Da sauri ta riko hannuna, "please, kinji? Don Allah!. Wallahi kwana biyun nan gidan babu dadi. Dama a wajen Yaya Bilal nake samu na dan ji sauki wasu lokutan, idan yana gida. To shima kwanannan sai a hankali. Tun jiya da yamma ya rikice, ko kallona baya yi wallahi. Yau da safe dana gaida shi, ko amsawa ma baiyi ba. Kuma ya hana ni yawo, balle inje wani wajen. Don Allah, muje ki dan debe min kewa, kinji?".
Gabadaya tausayin ta ya lullube ni. Wani irin bahagon zama suke yi da matar yayanta. Wani lokacin sai kayi kuskure kace irin zaman kishiyoyin nan ne da suke zabga dan banzan kishi suke yi.
Ba tare dana sake tunani ba, na gyada mata kai. Tayi tsallen murna tare da rukunkume ni.
Napep muka tara, bayan na ba dan acaban da muka kira hakuri. Unguwar PZ muka nufa, wadda bata da nisa da wajen da muke zuwa TP din.
Gidan Yaya Bilal, inda Janan take zaune, babban gida ne sosai. Daga nesa idan ka hango shi zaka yi tunanin irin family house dinnan ne. Sai dai su biyu ne suke zaune, shi da kaninshi Jameel, sai kuma matansu.
Kowacce tana da part dinta, masu fadi da nisa da kowannensu, ta yadda idan daya taga dama, zata kwashe watanni bata ga yar'uwarta ba.
Sashen gidan Yaya Bilal ake fara tardawa idan aka shiga gidan. Shima can din ya kasu kusan parts uku, duk da sauran biyun duk a kulle suke, dayan ne Janan take zaune ita da Raheema matar Yaya Bilal.
Shekaru biyu da suka wuce ne suka yi auren, basu ma cika da yin shekara biyu ba. Har yau Allah bai basu haihuwa ba.
Abu ne da naji kus-kus suna tashi akan cewa wai, wai Yaya Bilal din baya haihuwa. Saboda matarshi ta farko ma, Ameerah, wadda suka kwashe shekaru kusan shida a tare, auren saurayi da budurwa, bata taba haihuwa ba itama.
A hankali muka yi sallama cikin falon gidan, bamu ji motsin kowa ba, ko na TV babu, balle na mutane. Janan ta ja ni zuwa dakinta, ta koma kicin ta dauko mana ruwa da lemu.
Ina zaune a gefen gadonta, na dinga jiyo karar sautin kida tana tashi. Na kalleta, tana tsaye a gaban wardrobe tana nema mana kaya masu saukin nauyi da zamu saka.
Nace "wannan karar fa, daga ina take fitowa haka?".
Ta dan juyo ta kalleni, kafin ta maida kanta cikin closet din. "babu mamaki su Haleemo ne suke kallo!".
Na dafe baki, "wai dama yaran nan suna nan har yanzu?".
Tayi yar dariya, wadda take lullube da zallan takaici, "to dama ina zasu je? Ai suna nan a gidan nan, basu da ranar fita!".
Ta miko min Skirt dogo na wani yadi tare da riga, na amsa na fara zare kayan jikina, nace "to Allah Ya kara rufa mana asiri!".
Tace "ameen".
Ni tunda nake ganin gidan aure da cakudewar rayuwar aure, ban taba ganin irin wadda ta kama kafar ta gidan Yaya Bilal ba.
An saba idan aka yi aure, akai amarya ita daya zikal dinta gidan miji. Sai dai ita wannan abun nata ya bambanta. Koda aka kai amarya, sai kannenta guda biyu suka samu waje suka share, suka mike kafafu a gidan. _Marry one, get two free kenan!._
Watanni bakwai da kai amarya, Babbar kawar amaryar ta kaso aurenta, itama taje tabi layin jerin yan'uwanta dake gidan kamar wadda bata da gidan zama. Yanzu dai su ukun duka suna zaune a karkashin kulawar Yaya Bilal ne. Amma yar kanwarsa daya tilo dake zaune dasu, sun kasa riketa balle su kula da ita.
Kullum fata da buri nasu ta bar gidan, bin malamai, asiri, kissa da kisisina, babu wadda basa yi. Allah ne kadai yake kareta a gidan nan.
Tana gama sallatar azuhur, ta ja ni muka shiga kicin domin mu nemi abinda zamu saka a cikinmu. Muna cikin girkin Yaya Bilal ya shigo kicin din, ya amsa gaisuwar da muka mishi a kaikaice.
Ya kalli Janan yana wani cin magani, "ke ina Raheema take ne?".
A hankali kamar mai tsoron magana, tace "yanzu muma muka dawo, bamu sameta a gidan ba".
Bai kara cewa komi ba, ya fita daga kicin din. Ko me yake faruwa kuma yanzu? Na saba ganin kallon so da kulawa daga gareshi zuwa ga yar kanwar tashi, yau kuma naga wani abu daban.
Na kalli Janan dake kokarin hadiye kwallar data cika mata ido, cike da tausayi. Haka Allah ya halicceta mai sanyin hali, da sanyin zuciya.
Danwaken fulawa muka kwaba, daidai wanda zai dauki cikin mutum biyu. Duk kokarin da tayi na mu kara yawan fulawar, ki nayi. Saboda nasan saboda wannan lalatattun yaran take so muyi da yawa. Ni kuwa da in dafa abinci da hannuna, kattin banza su cinye, su goge hannu da tissue su kara mike kafa, karshe ni ce zan kwashe kwanukan da suka ci abincin ma, na gwammace in zauna da yunwa.
Muna gamawa, muka juye shi a cikin kula tare da gyara kicin din tsaf, kamar babu abinda aka yi. Janan ta wuce mana da kular daki, ni kuma na dauki plates da vegetables din da muka yanka nima na fita dasu.
A bakin kofar kicin muka ci karo da Salama, kanwar Anty Raheemah. Duk cikin kannenta babu wadda ta fita rashin da'a da rashin mutunci, shi yasa jininmu bai hadu ba, sam.
Ta wani tsaya kerere, ta kama kugu tare da kara babakewa akan hanya. Ko tayi zaton zagayeta zanyi in wuce? Na saki wani murmushin mugunta. Lallai yarinya har yau baki gama sani na ba.
Na tunkareta gadan-gadan. Da dai taga ina shirin bangajeta, sai taja baya. Na ja dan siririn tsaki a cikin raina, ina raya 'dama kin tsaya kin ga karshen wulakanci!'.
Ta wani daga murya, "ina namu abincin?".
Na kuwa tsaya cak, na juya na kalleta, "ban gane naku abincin ba? Kin daukeni aikatau din yi miki girki ne dama ban sani ba?".
Tayi gyatsine, "taya za ayi ki shigo har cikin gidan Yayata, kiyi girki sannan kuma ki k'i ajiye mana?".
Naji wata dariya na neman subuce min, nace "to sannu hamshakiya! Sarauniya mai girma!! Allah Ya bamu hakuri mu da bamu da gidan Yaya dake aure a gidan mutane, balle muje mu shimfida mulki a inda bai dace ba!. Girki ne, bamu yi daku ba. In kinyi zuciya, ga hanyar kicin nan, ki shiga ki girka wanda yafi wanda muka girka!".
Na juya na shige daki, tare da maida kofar dakin na rufe. Ina jin sautin maganganu da zage-zagen da take yi. Janan tace "ni dai wallahi da baki biye mata ba!".
Harara na jefa mata, "ai a haka suke samun damar taka ki kamar wata sakara. Ke dai da kika ga zaki iya, sai kije kiyi tayi. Ni kam, ba zan iya jure rashin kunya irin nasu ba wallahi!".
Kai kawai ta gyada, don tasan gardama dani ma bata baki ne.
Karfe biyar na mata sallama zan koma makaranta. Zuwa lokacin babu kowa a cikin gidan, muna jin lokacin da suka fita. Daidai bayan tagar dakin Yaya Bilal, na hangi wani abu daya dauke min hankali. Da sauri na kalli Janan, "kai! Kinga kuwa na manta jotter na akan gado, don Allah taimaka ki dauko min ita mana, zan jira ki anan!".
Babu musu tace "to!".
Ina zuwa, bus din da take daukanmu zuwa Kongo tana zuwa, don haka na bi jerin mutanen dake layi suna shiga ciki, bayan na biya kudin mota.
Karfe takwas da yan mintuna na sauka a inda na saba sauka. Daga nan acaba na hau, zuwa cikin unguwar Gyallesu, wani karamin public health centre nake zuwa aikin TP na. Karfe takwas muke farawa mu gama karfe daya zuwa biyu. Kowa dai yasan yadda dalibai suke da son yin latti, musamman a irin wannan lokacin da kasan cewa babu wanda zai kulle maka aji, ko ya hana ka attendance.
Duk da lattin da nayi, sai da na riga Janan isa. Ita wannan dama ba'a maganarta idan ana zancen latti, sam bata dana biyu.
Karfe sha daya da rabi muka tashi. Muka fita daga wajen ni da ita a gajiye, kuma cikin sanyin jiki. Babu ranar banza da ba zaka je asibitin nan baka ga abinda zai tayar maka da hankali ba.
Ranar an kai wata mata mai ciki asibitin. Kwanaki uku kenan da aka yi mata scanning, aka ga cewar dan cikinta ya rasu. Maimakon a yi inducing dinta, sai mijin ya ciccibeta suka koma gida. Wani abin karin haushi da ban takaici shine, mijin nata likita ne, duk da ba zan ce likitan ainihi ba tunda shago ne yake dashi babba da ake sayar da magunguna.
Tun shakaranjiya take nakuda, bai kaita asibiti ba sai ya kira unguwar-zoma. Ana ta kai da kawo dai, har jiya bata samu ta haihu ba, shine yau da safe suka tarkata ta zuwa asibitin. Ana maganar a dauketa a kaita Shika, domin a mata tiyata a cire cikin, rai yayi halinsa.
Abin gwanin ban tausayi da takaici. Ga ta da yara kanana wadanda basu gama mallakar hankulan kansu ba.
Har muka je inda muke hawa acaba, abinda muke tattaunawa kenan ni da Janan.
Ta kalleni tana canza muryarta zuwa alamun roko, "don Allah sis, kizo muje gida mana. Sai ki koma da yamma, kinji?".
Na harareta, "tab! Allah Ya kyauta wallahi. Ni kin ma ga tafiyata!".
Nayi saurin sa hannu ina kiran daya daga cikin yan acaban da suka yi jerin gwano, suna jiran fasinjoji.
Da sauri ta riko hannuna, "please, kinji? Don Allah!. Wallahi kwana biyun nan gidan babu dadi. Dama a wajen Yaya Bilal nake samu na dan ji sauki wasu lokutan, idan yana gida. To shima kwanannan sai a hankali. Tun jiya da yamma ya rikice, ko kallona baya yi wallahi. Yau da safe dana gaida shi, ko amsawa ma baiyi ba. Kuma ya hana ni yawo, balle inje wani wajen. Don Allah, muje ki dan debe min kewa, kinji?".
Gabadaya tausayin ta ya lullube ni. Wani irin bahagon zama suke yi da matar yayanta. Wani lokacin sai kayi kuskure kace irin zaman kishiyoyin nan ne da suke zabga dan banzan kishi suke yi.
Ba tare dana sake tunani ba, na gyada mata kai. Tayi tsallen murna tare da rukunkume ni.
Napep muka tara, bayan na ba dan acaban da muka kira hakuri. Unguwar PZ muka nufa, wadda bata da nisa da wajen da muke zuwa TP din.
Gidan Yaya Bilal, inda Janan take zaune, babban gida ne sosai. Daga nesa idan ka hango shi zaka yi tunanin irin family house dinnan ne. Sai dai su biyu ne suke zaune, shi da kaninshi Jameel, sai kuma matansu.
Kowacce tana da part dinta, masu fadi da nisa da kowannensu, ta yadda idan daya taga dama, zata kwashe watanni bata ga yar'uwarta ba.
Sashen gidan Yaya Bilal ake fara tardawa idan aka shiga gidan. Shima can din ya kasu kusan parts uku, duk da sauran biyun duk a kulle suke, dayan ne Janan take zaune ita da Raheema matar Yaya Bilal.
Shekaru biyu da suka wuce ne suka yi auren, basu ma cika da yin shekara biyu ba. Har yau Allah bai basu haihuwa ba.
Abu ne da naji kus-kus suna tashi akan cewa wai, wai Yaya Bilal din baya haihuwa. Saboda matarshi ta farko ma, Ameerah, wadda suka kwashe shekaru kusan shida a tare, auren saurayi da budurwa, bata taba haihuwa ba itama.
A hankali muka yi sallama cikin falon gidan, bamu ji motsin kowa ba, ko na TV babu, balle na mutane. Janan ta ja ni zuwa dakinta, ta koma kicin ta dauko mana ruwa da lemu.
Ina zaune a gefen gadonta, na dinga jiyo karar sautin kida tana tashi. Na kalleta, tana tsaye a gaban wardrobe tana nema mana kaya masu saukin nauyi da zamu saka.
Nace "wannan karar fa, daga ina take fitowa haka?".
Ta dan juyo ta kalleni, kafin ta maida kanta cikin closet din. "babu mamaki su Haleemo ne suke kallo!".
Na dafe baki, "wai dama yaran nan suna nan har yanzu?".
Tayi yar dariya, wadda take lullube da zallan takaici, "to dama ina zasu je? Ai suna nan a gidan nan, basu da ranar fita!".
Ta miko min Skirt dogo na wani yadi tare da riga, na amsa na fara zare kayan jikina, nace "to Allah Ya kara rufa mana asiri!".
Tace "ameen".
Ni tunda nake ganin gidan aure da cakudewar rayuwar aure, ban taba ganin irin wadda ta kama kafar ta gidan Yaya Bilal ba.
An saba idan aka yi aure, akai amarya ita daya zikal dinta gidan miji. Sai dai ita wannan abun nata ya bambanta. Koda aka kai amarya, sai kannenta guda biyu suka samu waje suka share, suka mike kafafu a gidan. _Marry one, get two free kenan!._
Watanni bakwai da kai amarya, Babbar kawar amaryar ta kaso aurenta, itama taje tabi layin jerin yan'uwanta dake gidan kamar wadda bata da gidan zama. Yanzu dai su ukun duka suna zaune a karkashin kulawar Yaya Bilal ne. Amma yar kanwarsa daya tilo dake zaune dasu, sun kasa riketa balle su kula da ita.
Kullum fata da buri nasu ta bar gidan, bin malamai, asiri, kissa da kisisina, babu wadda basa yi. Allah ne kadai yake kareta a gidan nan.
Tana gama sallatar azuhur, ta ja ni muka shiga kicin domin mu nemi abinda zamu saka a cikinmu. Muna cikin girkin Yaya Bilal ya shigo kicin din, ya amsa gaisuwar da muka mishi a kaikaice.
Ya kalli Janan yana wani cin magani, "ke ina Raheema take ne?".
A hankali kamar mai tsoron magana, tace "yanzu muma muka dawo, bamu sameta a gidan ba".
Bai kara cewa komi ba, ya fita daga kicin din. Ko me yake faruwa kuma yanzu? Na saba ganin kallon so da kulawa daga gareshi zuwa ga yar kanwar tashi, yau kuma naga wani abu daban.
Na kalli Janan dake kokarin hadiye kwallar data cika mata ido, cike da tausayi. Haka Allah ya halicceta mai sanyin hali, da sanyin zuciya.
Danwaken fulawa muka kwaba, daidai wanda zai dauki cikin mutum biyu. Duk kokarin da tayi na mu kara yawan fulawar, ki nayi. Saboda nasan saboda wannan lalatattun yaran take so muyi da yawa. Ni kuwa da in dafa abinci da hannuna, kattin banza su cinye, su goge hannu da tissue su kara mike kafa, karshe ni ce zan kwashe kwanukan da suka ci abincin ma, na gwammace in zauna da yunwa.
Muna gamawa, muka juye shi a cikin kula tare da gyara kicin din tsaf, kamar babu abinda aka yi. Janan ta wuce mana da kular daki, ni kuma na dauki plates da vegetables din da muka yanka nima na fita dasu.
A bakin kofar kicin muka ci karo da Salama, kanwar Anty Raheemah. Duk cikin kannenta babu wadda ta fita rashin da'a da rashin mutunci, shi yasa jininmu bai hadu ba, sam.
Ta wani tsaya kerere, ta kama kugu tare da kara babakewa akan hanya. Ko tayi zaton zagayeta zanyi in wuce? Na saki wani murmushin mugunta. Lallai yarinya har yau baki gama sani na ba.
Na tunkareta gadan-gadan. Da dai taga ina shirin bangajeta, sai taja baya. Na ja dan siririn tsaki a cikin raina, ina raya 'dama kin tsaya kin ga karshen wulakanci!'.
Ta wani daga murya, "ina namu abincin?".
Na kuwa tsaya cak, na juya na kalleta, "ban gane naku abincin ba? Kin daukeni aikatau din yi miki girki ne dama ban sani ba?".
Tayi gyatsine, "taya za ayi ki shigo har cikin gidan Yayata, kiyi girki sannan kuma ki k'i ajiye mana?".
Naji wata dariya na neman subuce min, nace "to sannu hamshakiya! Sarauniya mai girma!! Allah Ya bamu hakuri mu da bamu da gidan Yaya dake aure a gidan mutane, balle muje mu shimfida mulki a inda bai dace ba!. Girki ne, bamu yi daku ba. In kinyi zuciya, ga hanyar kicin nan, ki shiga ki girka wanda yafi wanda muka girka!".
Na juya na shige daki, tare da maida kofar dakin na rufe. Ina jin sautin maganganu da zage-zagen da take yi. Janan tace "ni dai wallahi da baki biye mata ba!".
Harara na jefa mata, "ai a haka suke samun damar taka ki kamar wata sakara. Ke dai da kika ga zaki iya, sai kije kiyi tayi. Ni kam, ba zan iya jure rashin kunya irin nasu ba wallahi!".
Kai kawai ta gyada, don tasan gardama dani ma bata baki ne.
Karfe biyar na mata sallama zan koma makaranta. Zuwa lokacin babu kowa a cikin gidan, muna jin lokacin da suka fita. Daidai bayan tagar dakin Yaya Bilal, na hangi wani abu daya dauke min hankali. Da sauri na kalli Janan, "kai! Kinga kuwa na manta jotter na akan gado, don Allah taimaka ki dauko min ita mana, zan jira ki anan!".
Babu musu tace "to!".