Sashe 8
A Zato Na Complete Hausa Novel · about 8 min read
Tunda Janan taje gidan, take gasa mata aya a tafin hannu cikin ruwan sanyi. Bata da bakin korafi saboda koda wasa bata bar hanyar da Yaya zai yi suspecting dinta ba. Spare makullin gidan da Yaya ya bata, ta amshe, kullum sai ta buga mata gida idan ta dawo daga makaranta, kuma sai ta wulakantata kafin ta bude mata gidan, store din abinci a kulle yake, wani lokacin sai dai ta saka kudinta ta sayi abinci. Idan Yaya baya gidan to ita da babu duk daya suke, duk kokarin Janan akan su daidaita abin yaci tura. Ita cewa ma tayi gwanda ace fada suke yi akan wannan zaman doya da manja din.
Ita kuma tayi-tayi dashi akan ya bari ta koma wajen Anty Sa'a tunda suna Zaria yanzu, ko basa nan akwai kanwar mijinta da suke zaune tare a gidan sai ta zauna dasu, ko kuma ya kama mata gida a samaru, ko ma dai a ina ne, amma yayi fir ya ki. Ita kuma bata so ta takura mishi da maganar kada yace ko bata son zama da matar shi ne ko wani abu.
Sai a ranar naji cewa ashe ba mahaifinsu daya da Yaya Bilal ba. Mahaifinsu Yayan ya jima da rasuwa, bayan nan ne ta auri wani mutum a Kaduna, shine mahaifin Janan din. Sai lokacin na fahimci komi, ina ta mamakin dalilin da yasa Ummarsu take zaune a Kaduna bayan duk danginsu suna Zaria, nayi zaton ko aikine ya kai baban su Janan din Kaduna. Amma nayi mamaki, koda wasa basu taba nuna mata banbanci ba, ita ko su Harira diyar kishiyar Umma, basu taba nuna mata wani ki ko kyama ba.
Janan kuka take yi sosai lokacin da take bani labarin wannan, na rungumeta ina bata hakuri, don shine kadai abinda zan iya yi a lokacin, har ta gama kukan. Daga nan muka fito da littafanmu muka cigaba da karatu har aka kira sallah muka tashi muka yi, muka koma muka cigaba da karatunmu. Muna nan sai ga Anty Ameerah ta leko, tace muje mu debi abinci, Janan ta fita zata zubo mana abincin, sai gata ta dawo wai Yayan yace muje muci tare dasu. Tace haka yake, in dai yana gidan tare suke cin abinci. Na dauki hijabita na saka muka fita.
A falon sai na daga baki ina kallon ikon Allah, gabadaya mata ta rikide, ta koma kamar wata salihar kirki, kamar ba wannan matar da take amsa mana magana da dai-daya ba.
Sai nan-nan take yi damu, abinci kamar zata zuba mana a baki yadda take ta turo mana plates na varieties din abinci gaban mu. Tsabar mamaki ma ni kasa yin magana nayi. Lallai an saka Janan a cikin tsaka mai wuya. Idan har haka take mata, to lallai kuwa babu wanda zai yarda da cewa idan an saka mata yatsa a baki zata ciza, sai dai idan har tayi hakan a gabanka.
Muna gama cin abincin muka koma daki. Muna shiga na fara zuba magana, tsananin mamakin matar ya hana ni hada maganganu masu ma'ana ma, Janan sai gefe ta koma tana min dariya. Sai dana nutsu sannan na iya zama muka yi magana akan haka da ita.
Sai bayan sallar la'asar can, sannan na mike ganin cewa Yaya bashi da niyar barin gidan. Janan tayi-tayi dani akan in tsaya Yaya ya fito, nace mata ina da abubuwan yi ne a hostel, dole ta kyaleni na tafi.
Daga wannan rana ban kara taka kafata zuwa gidan Yaya Bilal ba har yau.
Karatunmu yaci gaba da tafiya cikin nasara. Ni da Janan duk bamu dauki karatunmu da wasa ba, duk da bamu yin topping, amma dai Alhamdulillah, babu abinda ya taba dawo mana.
Muna shekarar mu ta uku, Yaya ya sake yin wani auren, ya auro Anty Raheemah. Yadda ya rikice akan wannan auren, yasa na kara tsurewa da lamarin maza. Lokacin bikinsu da Anty Ameerah yadda yake ta rawar kai da zakewa, kai sai kayi zaton babu wata 'ya mace da zata sake yin daraja ko kuma a idonshi bayan ita, sai gashi tun ba aje ko'ina ba ya karo wani auren.
Janan tace ba karamin rikici suka yi da matar Yayan ba, har ta kai ga cewa ya fita ya bar mata gida, inda abin ya yiwa Yaya ciwo matuka. Ya karasa gyara gidan gadonsu, dama can ya fara gyarawa zai kai Ameerah din, iyayenta suka hana.
An dai yi biki lafiya, despite tashe-tashen hankulan da aka sha, amarya ta tare a gidan mijinta, Janan ma tayi kaura can.
Muna ta murna, a tunaninmu wannan zamu tafi da ita, tunda sa'ar mu ce ita, ashe yaudarar kanmu muke yi.
Raheemah da kannenta irin 'ya'yan mace dinnan ne. Zaku yi mamaki idan kuka ji cewa suna da uba da yake raye, kuma auren iyayensu yana nan, amma suna zaune separately. Duniya da son abin duniya ya rufe musu ido daga su har uwarsu, mahaifinsu kuwa mutum ne mai wadatar zuciya da tsoron Allah.
Tun yarintarsu, bin bokaye da malamai shine amsar tambayarsu da komi nasu. Kodayake, wanene a garin Zaria bai san da zaman Hajja Ladidi ba? Shi yasa tashin farko da naji wai Yaya zai auri daya daga cikin diyanta, abin ya bani mamaki kwarai. Sam ire-iren su ba irin wadanda yaya yake hulda dasu bane.
Kannen Raheemah biyu da suka tare a gidan su suke kara rura wutar dake cikin gidan Yaya Bilal. Su duka biyun suna karatu a jami'ar Kongo. Saboda haka suka baro gidansu dake Hanwa, suka koma can saboda ya fi kusa da makaranta. Duk da a zahirin gaskiya ba hakan bane. Haleemo da Salama sune yan kanzagin ta, sune masu zuwa garuruwa da kauyuka amso mata magunguna wajen malamai da yan tsubbu yayin da take gida ta mike kafa.
Sai da na yiwa Janan fatan dama a wajen Anty Ameerah ta zauna, tace mugun fata nake mata. A cewarta zama dasu Haleemo, duk da gallazawar da suke mata, yafi mata sau dubu akan zama da Ameerah. Don haka na kawo idanu na zuba mata. Don haka ban taba ganin laifinta ba don tana zuwa wajen Umma weekend ba duk karshen sati, watarana ma nima ina binta.
To da yake ita rayuwa babu abinda hakuri baya maka, gashi yanzu har zamu shiga shekararmu ta karshe, ko ma in ce mun shiga. Duk da har yanzu dai babu abinda ya canza, sai ma karuwa da yake yi. Tun basa cin karfin Yaya akan Janan, har suka zo suka ci galaba a kanshi. Wasu lokutan haka zai birkice mata kamar ba Yayan nan nata mai son ta ba, sau tari sai dai ta kira ni tayi ta kuka, ni kam sai dai inyi ta bata hakuri. Rabin abubuwan da ake mata a gidan nan, ko Ummarsu bata sani ba, tunda duk cikin danginsu babu mai zuwa gidan balle yaga halin da take ciki.
Shi kanshi Yaya din, yau da gobe ce tasa ya gane tana zaman gallazawa a gidanshi. Sai ma watarana da yazo ya tadda Sa'adiya wadda suke cewa Adi, kawar Raheemah din da take zaune a gidan, tana ta zagin Janan akan wai bata yi mopping din falo ba, ran Yaya ya baci matuka, ya tara su su duka ya ja musu kunne, kuma yace daga ranar duk wadda ta sake taba mishi kanwa a gidannan, sai ta bar mishi gida. Aikin gidan ma kuma daga ranar ya hana ta yi, ita ce dai taga dama taci gaba da yi, tunda kunnen kashi gareta. Duk yadda nayi da ita akan ta bari tunda yace ta bari din, kiyawa tayi. Don haka na zuba mata ido, ni dai nasan da ni ce, da zuwa yanzu su duka sun bar gidan.
To rayuwar dai haka ake yinta, yau dadi, gobe madaci, gashi yanzu wasu abubuwan sun zama sai dai a tarihi. Nan da lokaci kadan ma, zata bar musu gidan.
*
*☆⋆04⋆☆*
* ☆ *
Har washegari Lahdi ina jiran Baba ya turo min kudin mota, amma shiru kake ji, kamar an shuka dusa.
Na duba agogon dake daure a tsintsiyar hannuna, naga cewa karfe goma sha daya na safe ta wuce. Nayi kwafa. Wani text din na sake tura mishi. Sai can wajen karfe sha biyu da rabi naji karan shigowar text, na duba naga shine ya turo min kudin motar, nayi kokarin resisting takaicin daya tuko ni, zuciyata na tunatar dani gida za ni ba wani waje ba.
Sai da nayi sallah sannan muka yi sallama da Aylah cike da kewa. Ina shirin fita kiran Umar ya shigo wayata, ya sanar dani yana waje yana jira na, don haka na ciccibi akwatuna na fita.
Ya saka akwatin a bayan booth, ni kuma na bude gidan gaba na shiga. Ya shigo motar ya tashe ta. Sai daya tsaya a banki na ciri kudi, sannan muka tafi. Har tashar mota ya kaini. Sai daya biya min kudin mota, sannan ya min sallama. Na mishi godiya sosai. Allah ya taimakeni motar ta kusa cika, ba'a jima ba muka dauki hanyar Katsina.
*
Karfe biyar na yamma a cikin garin Katsina ta mana. Motar tayi karan karshe a cikin tasha, a gajiye na fito daga motar ina mika. Na rataya jakata a kafada tare da daukar dan madaidaicin trolley din dana sako kayan da zan bukata na fita daga tasha din. Shatar adaidata nayi har unguwar Magama inda gidanmu yake.
Madaidaicin gidane daidai masu rufin asiri. Na fita daga cikin adaidaita din bayan na biya shi kudin shi. Wasu daga cikin yaran gidan dake kofar gida suna wasa suka bazamo da gudu suna ihun min oyoyo, nayi dariya ina dukawa kasa yadda zasu ji dadin rungumeni sosai. Abbakar ya dauki trolley na, yayin da Auwal ya rike jakar hannuna, na kama hannun Mufeedah muka shiga gidan.
Ita kuma tayi-tayi dashi akan ya bari ta koma wajen Anty Sa'a tunda suna Zaria yanzu, ko basa nan akwai kanwar mijinta da suke zaune tare a gidan sai ta zauna dasu, ko kuma ya kama mata gida a samaru, ko ma dai a ina ne, amma yayi fir ya ki. Ita kuma bata so ta takura mishi da maganar kada yace ko bata son zama da matar shi ne ko wani abu.
Sai a ranar naji cewa ashe ba mahaifinsu daya da Yaya Bilal ba. Mahaifinsu Yayan ya jima da rasuwa, bayan nan ne ta auri wani mutum a Kaduna, shine mahaifin Janan din. Sai lokacin na fahimci komi, ina ta mamakin dalilin da yasa Ummarsu take zaune a Kaduna bayan duk danginsu suna Zaria, nayi zaton ko aikine ya kai baban su Janan din Kaduna. Amma nayi mamaki, koda wasa basu taba nuna mata banbanci ba, ita ko su Harira diyar kishiyar Umma, basu taba nuna mata wani ki ko kyama ba.
Janan kuka take yi sosai lokacin da take bani labarin wannan, na rungumeta ina bata hakuri, don shine kadai abinda zan iya yi a lokacin, har ta gama kukan. Daga nan muka fito da littafanmu muka cigaba da karatu har aka kira sallah muka tashi muka yi, muka koma muka cigaba da karatunmu. Muna nan sai ga Anty Ameerah ta leko, tace muje mu debi abinci, Janan ta fita zata zubo mana abincin, sai gata ta dawo wai Yayan yace muje muci tare dasu. Tace haka yake, in dai yana gidan tare suke cin abinci. Na dauki hijabita na saka muka fita.
A falon sai na daga baki ina kallon ikon Allah, gabadaya mata ta rikide, ta koma kamar wata salihar kirki, kamar ba wannan matar da take amsa mana magana da dai-daya ba.
Sai nan-nan take yi damu, abinci kamar zata zuba mana a baki yadda take ta turo mana plates na varieties din abinci gaban mu. Tsabar mamaki ma ni kasa yin magana nayi. Lallai an saka Janan a cikin tsaka mai wuya. Idan har haka take mata, to lallai kuwa babu wanda zai yarda da cewa idan an saka mata yatsa a baki zata ciza, sai dai idan har tayi hakan a gabanka.
Muna gama cin abincin muka koma daki. Muna shiga na fara zuba magana, tsananin mamakin matar ya hana ni hada maganganu masu ma'ana ma, Janan sai gefe ta koma tana min dariya. Sai dana nutsu sannan na iya zama muka yi magana akan haka da ita.
Sai bayan sallar la'asar can, sannan na mike ganin cewa Yaya bashi da niyar barin gidan. Janan tayi-tayi dani akan in tsaya Yaya ya fito, nace mata ina da abubuwan yi ne a hostel, dole ta kyaleni na tafi.
Daga wannan rana ban kara taka kafata zuwa gidan Yaya Bilal ba har yau.
Karatunmu yaci gaba da tafiya cikin nasara. Ni da Janan duk bamu dauki karatunmu da wasa ba, duk da bamu yin topping, amma dai Alhamdulillah, babu abinda ya taba dawo mana.
Muna shekarar mu ta uku, Yaya ya sake yin wani auren, ya auro Anty Raheemah. Yadda ya rikice akan wannan auren, yasa na kara tsurewa da lamarin maza. Lokacin bikinsu da Anty Ameerah yadda yake ta rawar kai da zakewa, kai sai kayi zaton babu wata 'ya mace da zata sake yin daraja ko kuma a idonshi bayan ita, sai gashi tun ba aje ko'ina ba ya karo wani auren.
Janan tace ba karamin rikici suka yi da matar Yayan ba, har ta kai ga cewa ya fita ya bar mata gida, inda abin ya yiwa Yaya ciwo matuka. Ya karasa gyara gidan gadonsu, dama can ya fara gyarawa zai kai Ameerah din, iyayenta suka hana.
An dai yi biki lafiya, despite tashe-tashen hankulan da aka sha, amarya ta tare a gidan mijinta, Janan ma tayi kaura can.
Muna ta murna, a tunaninmu wannan zamu tafi da ita, tunda sa'ar mu ce ita, ashe yaudarar kanmu muke yi.
Raheemah da kannenta irin 'ya'yan mace dinnan ne. Zaku yi mamaki idan kuka ji cewa suna da uba da yake raye, kuma auren iyayensu yana nan, amma suna zaune separately. Duniya da son abin duniya ya rufe musu ido daga su har uwarsu, mahaifinsu kuwa mutum ne mai wadatar zuciya da tsoron Allah.
Tun yarintarsu, bin bokaye da malamai shine amsar tambayarsu da komi nasu. Kodayake, wanene a garin Zaria bai san da zaman Hajja Ladidi ba? Shi yasa tashin farko da naji wai Yaya zai auri daya daga cikin diyanta, abin ya bani mamaki kwarai. Sam ire-iren su ba irin wadanda yaya yake hulda dasu bane.
Kannen Raheemah biyu da suka tare a gidan su suke kara rura wutar dake cikin gidan Yaya Bilal. Su duka biyun suna karatu a jami'ar Kongo. Saboda haka suka baro gidansu dake Hanwa, suka koma can saboda ya fi kusa da makaranta. Duk da a zahirin gaskiya ba hakan bane. Haleemo da Salama sune yan kanzagin ta, sune masu zuwa garuruwa da kauyuka amso mata magunguna wajen malamai da yan tsubbu yayin da take gida ta mike kafa.
Sai da na yiwa Janan fatan dama a wajen Anty Ameerah ta zauna, tace mugun fata nake mata. A cewarta zama dasu Haleemo, duk da gallazawar da suke mata, yafi mata sau dubu akan zama da Ameerah. Don haka na kawo idanu na zuba mata. Don haka ban taba ganin laifinta ba don tana zuwa wajen Umma weekend ba duk karshen sati, watarana ma nima ina binta.
To da yake ita rayuwa babu abinda hakuri baya maka, gashi yanzu har zamu shiga shekararmu ta karshe, ko ma in ce mun shiga. Duk da har yanzu dai babu abinda ya canza, sai ma karuwa da yake yi. Tun basa cin karfin Yaya akan Janan, har suka zo suka ci galaba a kanshi. Wasu lokutan haka zai birkice mata kamar ba Yayan nan nata mai son ta ba, sau tari sai dai ta kira ni tayi ta kuka, ni kam sai dai inyi ta bata hakuri. Rabin abubuwan da ake mata a gidan nan, ko Ummarsu bata sani ba, tunda duk cikin danginsu babu mai zuwa gidan balle yaga halin da take ciki.
Shi kanshi Yaya din, yau da gobe ce tasa ya gane tana zaman gallazawa a gidanshi. Sai ma watarana da yazo ya tadda Sa'adiya wadda suke cewa Adi, kawar Raheemah din da take zaune a gidan, tana ta zagin Janan akan wai bata yi mopping din falo ba, ran Yaya ya baci matuka, ya tara su su duka ya ja musu kunne, kuma yace daga ranar duk wadda ta sake taba mishi kanwa a gidannan, sai ta bar mishi gida. Aikin gidan ma kuma daga ranar ya hana ta yi, ita ce dai taga dama taci gaba da yi, tunda kunnen kashi gareta. Duk yadda nayi da ita akan ta bari tunda yace ta bari din, kiyawa tayi. Don haka na zuba mata ido, ni dai nasan da ni ce, da zuwa yanzu su duka sun bar gidan.
To rayuwar dai haka ake yinta, yau dadi, gobe madaci, gashi yanzu wasu abubuwan sun zama sai dai a tarihi. Nan da lokaci kadan ma, zata bar musu gidan.
*
*☆⋆04⋆☆*
* ☆ *
Har washegari Lahdi ina jiran Baba ya turo min kudin mota, amma shiru kake ji, kamar an shuka dusa.
Na duba agogon dake daure a tsintsiyar hannuna, naga cewa karfe goma sha daya na safe ta wuce. Nayi kwafa. Wani text din na sake tura mishi. Sai can wajen karfe sha biyu da rabi naji karan shigowar text, na duba naga shine ya turo min kudin motar, nayi kokarin resisting takaicin daya tuko ni, zuciyata na tunatar dani gida za ni ba wani waje ba.
Sai da nayi sallah sannan muka yi sallama da Aylah cike da kewa. Ina shirin fita kiran Umar ya shigo wayata, ya sanar dani yana waje yana jira na, don haka na ciccibi akwatuna na fita.
Ya saka akwatin a bayan booth, ni kuma na bude gidan gaba na shiga. Ya shigo motar ya tashe ta. Sai daya tsaya a banki na ciri kudi, sannan muka tafi. Har tashar mota ya kaini. Sai daya biya min kudin mota, sannan ya min sallama. Na mishi godiya sosai. Allah ya taimakeni motar ta kusa cika, ba'a jima ba muka dauki hanyar Katsina.
*
Karfe biyar na yamma a cikin garin Katsina ta mana. Motar tayi karan karshe a cikin tasha, a gajiye na fito daga motar ina mika. Na rataya jakata a kafada tare da daukar dan madaidaicin trolley din dana sako kayan da zan bukata na fita daga tasha din. Shatar adaidata nayi har unguwar Magama inda gidanmu yake.
Madaidaicin gidane daidai masu rufin asiri. Na fita daga cikin adaidaita din bayan na biya shi kudin shi. Wasu daga cikin yaran gidan dake kofar gida suna wasa suka bazamo da gudu suna ihun min oyoyo, nayi dariya ina dukawa kasa yadda zasu ji dadin rungumeni sosai. Abbakar ya dauki trolley na, yayin da Auwal ya rike jakar hannuna, na kama hannun Mufeedah muka shiga gidan.