Sashe 54
A Zato Na Complete Hausa Novel · about 8 min read
Kafin in tashi har Janan ta dafa mana jallop macaroni, lokacin dana tashi na gansu ita da Esther suna hira. Nayi mika tare da tashi zaune ina binsu da kallo, Janan ta kalleni "ki tashi ki wanko baki ki zo ki ci abinci. Ki gama muje wajen masu dinkin wancan mu gani idan sun gama mu amso".
Na tashi tsaye da kyar, ina jin jikina kamar an nada min dukan tsiya. Na dauki kettle na fita waje na daurayo bakina, na dawo na zauna a inda plate din abinci yake jirana. Na janyo abincin cikin mutuwar jiki na fara ci, ina ji suka ci gaba da hirarsu akan wajen da zasu je suyi nasu internship din, ita Janan a Kaduna zata yi, ita kuma Esther anan Shika zata yi. Nima dai nasan Shika dinne, don mun riga munyi maganar da Dr., ina karbar license dina zan mika mishi, zai yi applying internship din da kanshi anan Shika din.
Daga baya kuma sai hirar ta gangaro kan abinda zasu yi da abinda zasu saya idan suka dauki albashinsu na farko. Ina daga gefe ina jinsu, sai dai inyi dariya idan sun fadi wani abin daya bani dariya. Ko kuma in girgiza kai da jin absurdity din abubuwan da suke fada.
Ina gamawa, na maida kwanukan gefe. Esther ta jefo min wayata, nayi sauri na cafe. Tace "hubbynki ya kira lokacin da kike barci".
Na jefa mata harara cikin wasa, "shine kuma sai yanzu kika ga damar fada min? Kina so hankalin mijina ya tashi ne ko me?".
Ita da Janan suka yi dariya, tace "come on mana, nasan dana baki wayar nan daga tashinki daga barci, ba lallai kici abincin nan da wuri ba. Ko baki ga kokarina bane?".
Na daga baki zan bata amsa, aka amsa kiran dana dannawa wayar Dr., don haka na rufe bakina tare da kara wayar a kunne.
Tun kafin inyi magana ya riga ni, daga jin shi cike yake da doki da farinciki, "hey, guess what?".
Yanayin yadda yayi maganar kanshi ma, kasan cewa wani abu ne babba kuma muhimmi ya same shi, don haka naji na saki murmushi ba tare dana shiryawa hakan ba, nace "me ya faru ne?".
"Tafiyar nan fa ta samu, nan da sati biyu! Oh God!! I can't really believe this is happening!!". Ya karasa fada cikin karajin murya.
Naji na balle da murmushi nima kamar lebuna na zasu rabe biyu. Wani course ne asibitin zasu tura manyan doctors na department din su biyar kasar London duk bayan shekaru biyu, course ne na shekara biyu. Yace idan kaci sa'a, idan can asibitin da kaje yin course din suka ga kwazon ka, zasu iya daukar ka aiki kamar yadda suka dauki likitocinsu biyu aiki wadanda suka je waccan shekarar. Idan kuma baka samu aikin a can ba, idan ka dawo, zasu kara maka matsayi da kuma albashi anan. Wannan ba ma shine abin birgewar kadai ba, idan ka tafi can asibitin zasu dinga biyanka albashinka, su baka wajen zama, haka babu ruwanka da biyan kudin makaranta idan kaje. Tsarin shine, idan ka tafi yanzu, zaka yi wata takwas a makaranta kana daukar darasi abinka, a hakan ma kana da albashinka a hannu, bayan ka gama da nan zaka koma asibitin kayi aiki dasu na watanni goma sha biyu. Daga nan kuma sai su yanke shawarar yadda zasu yi da kai.
Yace min yanzu sau uku kenan yana applying ana hana shi, wannan karon ma kwata-kwata ya cire ranshi daga samu, sai kuma gashi yanzu babu zato babu tsammani, ya samu din.
Nace "Masha Allah, Alhamdulillah! Kai amma naji dadi wallahi, Allah ya tabbatar da alkhairi, Allah ya albarkaci aikin wannan".
Yace "ameen ameen amaryata. Ni har na rasa wace kalar murna ma yakamata inyi, ji nake kamar mafarki nake yi!".
Na saki yar dariya, "right! Kawai ka kalli alkibla yanzu, ta nan kadai zaka nunawa Allah godiyarka. Idan ka bar nan kuma, sai kayi sadaka".
Yace "haka ne, nagode dear. Bari in tafi yanzu".
Na girgiza kai fondly, wani lokacin kamar yaro haka yake gudanar da dabi'un shi, wasu lokutan ya baka dariya, watarana kuma takaicinshi ya cika maka ciki kamar kayi me.
Wani tunani ya darsu a raina, nace "to amma ya zamu yi ne? Bikin ma nan da sati biyu ne, kenan hakan yana nufin tare zamu tafi kenan?".
Ya danyi jim, zuwa can yace "har yanzu ina kan wannan tunanin ne. Yanzu zan shiga gida in sanar dasu, zan kira ki zuwa anjima". Nace mishi "to ka gaishe dasu Hajiya". Yace "zasu ji", ya kashe wayar.
Na bi wayar da kallo, ko menene abin yin tunani a cikin wannan maganar? Na tabe baki tare da daga kafada.
Su Janan da tunda muka fara wayar suka katse hirarsu suke kallona jifa-jifa, suka zubo min idanu, na kallesu cikin murmushi, "dudes, London ta kira mu yanzun nan!".
Habawa, suka saki ihu da shewa tare da fadowa kaina, sai da muka fadi kasa.
Janan tace "da gaske?!".
Esther kam, "Oh my God!" Kawai take fada tana nanatawa.
Sai da suka gama ihun murnarsu sannan Esther ta tashi zaune, muma muka tashi. Janan ta sake sarkafo hannunta ta rungumo ni, "Na taya ki murna wallahi dear... Allah yasa hakan shi yafi alkhairi. Yanzu sai kiyi tafiyarki ki barni?".
Nayi dariya, "sis, maganar fa bata tabbata ba. Ni fa ina assuming abubuwa ne kawai".
Ta kai min duka a kafada, "maganar banza kenan! Ke yanzu kina tunanin zai tafi ya barki anan har na tsawon shekaru biyu? Wasa kenan. Balle ma, su da ana basu gidajensu acan, ai babu ma wani dalili da zai hana mu zuwa kai amarya kasar London". Ta kyalkyale da dariya bayan ta gama fadin haka, ni da Esther muna taya ta.
Sai wajen karfe biyar na yamma sannan muka fita zuwa amsar dinkin. Har Esther muka tafi. A hanya Janan take tambayata, "su fa kayan lefen da ba'a kawo ba har yanzu, ya za ayi dasu?".
Na kalleta, "ke da kika san zamani ya canza, yanzu lefe da zaki ga har ana saura kwana biyar daurin aure ba'a kai ba. Balle shi fa yace kamar haka al'adar gidansu take, sai bayan aure ake kai kayan lefe".
Janan ta jinjina kai, "haka ne. Mu dai ya taimaka ya kawo kafin mu kaiki, idan haka ne, bamu da damar daukar turamenmu kenan".
Na kai mata duka ina dariya, "ke fa baki da M wallahi, wawashe min kayan zaku yi kenan?".
Muna wannan hirar har muka fita waje, muka hau bus zuwa inda muka kai dinki.
Dancing Banana, nan ne wajen da muka kai dinki. Duk da wasu kayayyakin suna can Katsina, Maryam ta kai min su, kai wasu ma suna Kaduna. Wadannan wadanda Ummahn su Janan ne ta bamu, manyan atamfofi guda biyu iri daya, da wani lafiyayyayen yadi ni da Janan din. Da kanta ta kai dinkin, namu kawai tura measurement dinmu ne.
Wadanda muka kawo nan, wanda angon ne ya kawo, tunda ba'a riga an kai lefe ba. Na Katsina kuma, wanda muka fitar ne a matsayin anko.
Kai tsaye wajen wanda yake mana dinkin muka wuce, muka samu ya dinka kala na mutum daya, na dayan kuma ya yanka bai dinka ba. Esther ta fara fuming, dama ita ta hada mu dashi, "yanzu kana nufin kusan sati biyu wai har yanzu baka gama mana dinkin ba? Mike meye hakan wai?".
Yace "na fa yi kokari, yanzu haka aikin wata na maida gefe nayi wannan din fa. Nayi alkawarin nan da kwana biyu zan gama muku, kin san bama yin haka dake Esther".
Muna nan tsaye, sai ga Haleemo a gabanmu. Bata ko yi acknowledging dinmu ba, ta hau zazzagawa mai dinki masifa. Apparently, ita ce wadda ya ture dinkinta dake kan layi ya mana namu. Tun yana bata hakuri, har shima ya hau sama ya fara zuba mata tata kalar masifa, mu kam muka koma gefe muna kallonsu.
Ta ja tsaki, "matsalarku kenan dama wallahi, ku kwata-kwata baku san mutumci ba. Su waye suka fito da martabar wannan shagon idan ba mu ba?".
Yace "ke kada fa ki kawo min rainin wayau nan wajen. Kada ki manta ko wancan dinkin dana miki, baki cika min kudina ba. Wannan ma kika wani ciccibo kaya kika kawo min babu ko sisi, an gaya miki ni din bawanki ne wai?".
Sai lokacin ta kallomu, ta fara borin kunya, "to ni nace ba zan baka kudin ka bane? Kada ka wulakanta ni a gaban mutane mana!".
Ni da Janan muka danne dariyar data ke neman subuce mana.
Shi kuwa Mike yayi dan tsaki, "whatever, kin san ni bana irin wadannan tone-tonen. Su ma don dinkin aure ne shi yasa ma na ajiye nakin gefe guda".
Ta kallemu ido a zare, "aure zaku yi?".
Nayi murmushi nace "eh".
Tare da bude jakata na dauko iv na mika mata, ta amsa ta karanta. Tace "to Allah ya sanya alkhairi". Muka ce ameen.
Bayan mun tabbatar da cewa zuwa jibi zamu dawo mu amshi dinkin mu, muka tafi muka bar su suna cigaba da sa'insar su.
A kofar wajen, muka samu Umar tsaye a jikin motar shi, da alama budurwar tashi yake jira. Muka yi kallon-kallo dashi, muka zagaye shi muka wuce abinmu ba tare da wani yayi magana ba. Janan gida ta wuce, ni da Esther kuma muka koma cikin asibiti.
Muna shiga daki sai ga kiran wayar Janan, wai Anty Sarah tayi yar diyarta kamar Mimah. Na mata fatan samun sauki da barka muka yi sallama.
Ranar juma'ah muka yi induction dinmu, bayan an rantsar damu, mun karbi nursing license dinmu, aka shiga shagalin ciye-ciye da shaye-shaye. Allah kadai yasan irin farincikin da muke ciki a wannan ranar. Duk da cewa convocation dinmu nan da satika biyu ne, amma kuma induction ya ma fi muhimmanci ga nurses nesa ba kusa ba. Yinin ranar guda, kira ne kawai yake shiga yana fita daga wayata, sakonni na taya murna daga yan uwa da abokan arziki.
Da yamma bayan mun gama shagalin, ni da Janan muka dauki hanya zuwa barka. Kasancewar gobe asabar zan wuce gida. Gashua zan fara zuwa inyi kwana biyu, sallama da yan uwa da abokan arziki, sai in wuce Katsina daga can.
Na tashi tsaye da kyar, ina jin jikina kamar an nada min dukan tsiya. Na dauki kettle na fita waje na daurayo bakina, na dawo na zauna a inda plate din abinci yake jirana. Na janyo abincin cikin mutuwar jiki na fara ci, ina ji suka ci gaba da hirarsu akan wajen da zasu je suyi nasu internship din, ita Janan a Kaduna zata yi, ita kuma Esther anan Shika zata yi. Nima dai nasan Shika dinne, don mun riga munyi maganar da Dr., ina karbar license dina zan mika mishi, zai yi applying internship din da kanshi anan Shika din.
Daga baya kuma sai hirar ta gangaro kan abinda zasu yi da abinda zasu saya idan suka dauki albashinsu na farko. Ina daga gefe ina jinsu, sai dai inyi dariya idan sun fadi wani abin daya bani dariya. Ko kuma in girgiza kai da jin absurdity din abubuwan da suke fada.
Ina gamawa, na maida kwanukan gefe. Esther ta jefo min wayata, nayi sauri na cafe. Tace "hubbynki ya kira lokacin da kike barci".
Na jefa mata harara cikin wasa, "shine kuma sai yanzu kika ga damar fada min? Kina so hankalin mijina ya tashi ne ko me?".
Ita da Janan suka yi dariya, tace "come on mana, nasan dana baki wayar nan daga tashinki daga barci, ba lallai kici abincin nan da wuri ba. Ko baki ga kokarina bane?".
Na daga baki zan bata amsa, aka amsa kiran dana dannawa wayar Dr., don haka na rufe bakina tare da kara wayar a kunne.
Tun kafin inyi magana ya riga ni, daga jin shi cike yake da doki da farinciki, "hey, guess what?".
Yanayin yadda yayi maganar kanshi ma, kasan cewa wani abu ne babba kuma muhimmi ya same shi, don haka naji na saki murmushi ba tare dana shiryawa hakan ba, nace "me ya faru ne?".
"Tafiyar nan fa ta samu, nan da sati biyu! Oh God!! I can't really believe this is happening!!". Ya karasa fada cikin karajin murya.
Naji na balle da murmushi nima kamar lebuna na zasu rabe biyu. Wani course ne asibitin zasu tura manyan doctors na department din su biyar kasar London duk bayan shekaru biyu, course ne na shekara biyu. Yace idan kaci sa'a, idan can asibitin da kaje yin course din suka ga kwazon ka, zasu iya daukar ka aiki kamar yadda suka dauki likitocinsu biyu aiki wadanda suka je waccan shekarar. Idan kuma baka samu aikin a can ba, idan ka dawo, zasu kara maka matsayi da kuma albashi anan. Wannan ba ma shine abin birgewar kadai ba, idan ka tafi can asibitin zasu dinga biyanka albashinka, su baka wajen zama, haka babu ruwanka da biyan kudin makaranta idan kaje. Tsarin shine, idan ka tafi yanzu, zaka yi wata takwas a makaranta kana daukar darasi abinka, a hakan ma kana da albashinka a hannu, bayan ka gama da nan zaka koma asibitin kayi aiki dasu na watanni goma sha biyu. Daga nan kuma sai su yanke shawarar yadda zasu yi da kai.
Yace min yanzu sau uku kenan yana applying ana hana shi, wannan karon ma kwata-kwata ya cire ranshi daga samu, sai kuma gashi yanzu babu zato babu tsammani, ya samu din.
Nace "Masha Allah, Alhamdulillah! Kai amma naji dadi wallahi, Allah ya tabbatar da alkhairi, Allah ya albarkaci aikin wannan".
Yace "ameen ameen amaryata. Ni har na rasa wace kalar murna ma yakamata inyi, ji nake kamar mafarki nake yi!".
Na saki yar dariya, "right! Kawai ka kalli alkibla yanzu, ta nan kadai zaka nunawa Allah godiyarka. Idan ka bar nan kuma, sai kayi sadaka".
Yace "haka ne, nagode dear. Bari in tafi yanzu".
Na girgiza kai fondly, wani lokacin kamar yaro haka yake gudanar da dabi'un shi, wasu lokutan ya baka dariya, watarana kuma takaicinshi ya cika maka ciki kamar kayi me.
Wani tunani ya darsu a raina, nace "to amma ya zamu yi ne? Bikin ma nan da sati biyu ne, kenan hakan yana nufin tare zamu tafi kenan?".
Ya danyi jim, zuwa can yace "har yanzu ina kan wannan tunanin ne. Yanzu zan shiga gida in sanar dasu, zan kira ki zuwa anjima". Nace mishi "to ka gaishe dasu Hajiya". Yace "zasu ji", ya kashe wayar.
Na bi wayar da kallo, ko menene abin yin tunani a cikin wannan maganar? Na tabe baki tare da daga kafada.
Su Janan da tunda muka fara wayar suka katse hirarsu suke kallona jifa-jifa, suka zubo min idanu, na kallesu cikin murmushi, "dudes, London ta kira mu yanzun nan!".
Habawa, suka saki ihu da shewa tare da fadowa kaina, sai da muka fadi kasa.
Janan tace "da gaske?!".
Esther kam, "Oh my God!" Kawai take fada tana nanatawa.
Sai da suka gama ihun murnarsu sannan Esther ta tashi zaune, muma muka tashi. Janan ta sake sarkafo hannunta ta rungumo ni, "Na taya ki murna wallahi dear... Allah yasa hakan shi yafi alkhairi. Yanzu sai kiyi tafiyarki ki barni?".
Nayi dariya, "sis, maganar fa bata tabbata ba. Ni fa ina assuming abubuwa ne kawai".
Ta kai min duka a kafada, "maganar banza kenan! Ke yanzu kina tunanin zai tafi ya barki anan har na tsawon shekaru biyu? Wasa kenan. Balle ma, su da ana basu gidajensu acan, ai babu ma wani dalili da zai hana mu zuwa kai amarya kasar London". Ta kyalkyale da dariya bayan ta gama fadin haka, ni da Esther muna taya ta.
Sai wajen karfe biyar na yamma sannan muka fita zuwa amsar dinkin. Har Esther muka tafi. A hanya Janan take tambayata, "su fa kayan lefen da ba'a kawo ba har yanzu, ya za ayi dasu?".
Na kalleta, "ke da kika san zamani ya canza, yanzu lefe da zaki ga har ana saura kwana biyar daurin aure ba'a kai ba. Balle shi fa yace kamar haka al'adar gidansu take, sai bayan aure ake kai kayan lefe".
Janan ta jinjina kai, "haka ne. Mu dai ya taimaka ya kawo kafin mu kaiki, idan haka ne, bamu da damar daukar turamenmu kenan".
Na kai mata duka ina dariya, "ke fa baki da M wallahi, wawashe min kayan zaku yi kenan?".
Muna wannan hirar har muka fita waje, muka hau bus zuwa inda muka kai dinki.
Dancing Banana, nan ne wajen da muka kai dinki. Duk da wasu kayayyakin suna can Katsina, Maryam ta kai min su, kai wasu ma suna Kaduna. Wadannan wadanda Ummahn su Janan ne ta bamu, manyan atamfofi guda biyu iri daya, da wani lafiyayyayen yadi ni da Janan din. Da kanta ta kai dinkin, namu kawai tura measurement dinmu ne.
Wadanda muka kawo nan, wanda angon ne ya kawo, tunda ba'a riga an kai lefe ba. Na Katsina kuma, wanda muka fitar ne a matsayin anko.
Kai tsaye wajen wanda yake mana dinkin muka wuce, muka samu ya dinka kala na mutum daya, na dayan kuma ya yanka bai dinka ba. Esther ta fara fuming, dama ita ta hada mu dashi, "yanzu kana nufin kusan sati biyu wai har yanzu baka gama mana dinkin ba? Mike meye hakan wai?".
Yace "na fa yi kokari, yanzu haka aikin wata na maida gefe nayi wannan din fa. Nayi alkawarin nan da kwana biyu zan gama muku, kin san bama yin haka dake Esther".
Muna nan tsaye, sai ga Haleemo a gabanmu. Bata ko yi acknowledging dinmu ba, ta hau zazzagawa mai dinki masifa. Apparently, ita ce wadda ya ture dinkinta dake kan layi ya mana namu. Tun yana bata hakuri, har shima ya hau sama ya fara zuba mata tata kalar masifa, mu kam muka koma gefe muna kallonsu.
Ta ja tsaki, "matsalarku kenan dama wallahi, ku kwata-kwata baku san mutumci ba. Su waye suka fito da martabar wannan shagon idan ba mu ba?".
Yace "ke kada fa ki kawo min rainin wayau nan wajen. Kada ki manta ko wancan dinkin dana miki, baki cika min kudina ba. Wannan ma kika wani ciccibo kaya kika kawo min babu ko sisi, an gaya miki ni din bawanki ne wai?".
Sai lokacin ta kallomu, ta fara borin kunya, "to ni nace ba zan baka kudin ka bane? Kada ka wulakanta ni a gaban mutane mana!".
Ni da Janan muka danne dariyar data ke neman subuce mana.
Shi kuwa Mike yayi dan tsaki, "whatever, kin san ni bana irin wadannan tone-tonen. Su ma don dinkin aure ne shi yasa ma na ajiye nakin gefe guda".
Ta kallemu ido a zare, "aure zaku yi?".
Nayi murmushi nace "eh".
Tare da bude jakata na dauko iv na mika mata, ta amsa ta karanta. Tace "to Allah ya sanya alkhairi". Muka ce ameen.
Bayan mun tabbatar da cewa zuwa jibi zamu dawo mu amshi dinkin mu, muka tafi muka bar su suna cigaba da sa'insar su.
A kofar wajen, muka samu Umar tsaye a jikin motar shi, da alama budurwar tashi yake jira. Muka yi kallon-kallo dashi, muka zagaye shi muka wuce abinmu ba tare da wani yayi magana ba. Janan gida ta wuce, ni da Esther kuma muka koma cikin asibiti.
Muna shiga daki sai ga kiran wayar Janan, wai Anty Sarah tayi yar diyarta kamar Mimah. Na mata fatan samun sauki da barka muka yi sallama.
Ranar juma'ah muka yi induction dinmu, bayan an rantsar damu, mun karbi nursing license dinmu, aka shiga shagalin ciye-ciye da shaye-shaye. Allah kadai yasan irin farincikin da muke ciki a wannan ranar. Duk da cewa convocation dinmu nan da satika biyu ne, amma kuma induction ya ma fi muhimmanci ga nurses nesa ba kusa ba. Yinin ranar guda, kira ne kawai yake shiga yana fita daga wayata, sakonni na taya murna daga yan uwa da abokan arziki.
Da yamma bayan mun gama shagalin, ni da Janan muka dauki hanya zuwa barka. Kasancewar gobe asabar zan wuce gida. Gashua zan fara zuwa inyi kwana biyu, sallama da yan uwa da abokan arziki, sai in wuce Katsina daga can.